52

الطور

At-Tur

The Mount

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ Da sunan Allah Mai rahama Mai jin kai
Ayoyi 49
Juzu'i 27
Shafi 523-525
Nau'i Makkiya
Tsarin Saukarwa 76
0:00 / 0:00
Aya: 1 / 49
1

وَٱلطُّورِ

wal-ṭūri

Inã rantsuwa da ¦ũr (Dũtsen Mũsã).

2

وَكِتَـٰبٍۢ مَّسْطُورٍۢ

wakitābin masṭūrin

Da wani littãfi rubũtacce.

3

فِى رَقٍّۢ مَّنشُورٍۢ

fī raqqin manshūrin

A cikin wata takardar fãta shimfiɗaɗɗa.

4

وَٱلْبَيْتِ ٱلْمَعْمُورِ

wal-bayti l-maʿmūri

Da Gidan da aka rãyar da shi (da ibãda).

5

وَٱلسَّقْفِ ٱلْمَرْفُوعِ

wal-saqfi l-marfūʿi

Da rufin nan da aka ɗaukaka.

6

وَٱلْبَحْرِ ٱلْمَسْجُورِ

wal-baḥri l-masjūri

Da tẽkun nan da aka cika (da ruwa).

7

إِنَّ عَذَابَ رَبِّكَ لَوَٰقِعٌۭ

inna ʿadhāba rabbika lawāqiʿun

Lalle, azãbar Ubangijinka, haƙĩƙa, mai aukuwa ce.

8

مَّا لَهُۥ مِن دَافِعٍۢ

mā lahu min dāfiʿin

Bã ta da mai tunkuɗẽwa.

9

يَوْمَ تَمُورُ ٱلسَّمَآءُ مَوْرًۭا

yawma tamūru l-samāu mawran

Rãnar da samã ke yin mõtsi tanã kai kãwo.

10

وَتَسِيرُ ٱلْجِبَالُ سَيْرًۭا

watasīru l-jibālu sayran

Kuma duwãtsu nã tafiya sunã shũɗẽwa.

11

فَوَيْلٌۭ يَوْمَئِذٍۢ لِّلْمُكَذِّبِينَ

fawaylun yawma-idhin lil'mukadhibīna

To, bone yã tabbata a rãnar nan ga mãsu ƙaryatãwa.

12

ٱلَّذِينَ هُمْ فِى خَوْضٍۢ يَلْعَبُونَ

alladhīna hum fī khawḍin yalʿabūna

Waɗanda suke a cikin kududdufi sunã wãsã.

13

يَوْمَ يُدَعُّونَ إِلَىٰ نَارِ جَهَنَّمَ دَعًّا

yawma yudaʿʿūna ilā nāri jahannama daʿʿan

Rãnar da zã a tunkuɗa su zuwa wutar Jahannama, tunkuɗãwa.

14

هَـٰذِهِ ٱلنَّارُ ٱلَّتِى كُنتُم بِهَا تُكَذِّبُونَ

hādhihi l-nāru allatī kuntum bihā tukadhibūna

(A ce musu): "Wannan ita ce wutar da kuka kasance kunã ƙaryatãwa game da ita."

15

أَفَسِحْرٌ هَـٰذَآ أَمْ أَنتُمْ لَا تُبْصِرُونَ

afasiḥ'run hādhā am antum lā tub'ṣirūna

"To, shin wannan sihiri ne kõ kuwa kũ ne bã ku gani?"

16

ٱصْلَوْهَا فَٱصْبِرُوٓا۟ أَوْ لَا تَصْبِرُوا۟ سَوَآءٌ عَلَيْكُمْ ۖ إِنَّمَا تُجْزَوْنَ مَا كُنتُمْ تَعْمَلُونَ

iṣ'lawhā fa-iṣ'birū aw lā taṣbirū sawāon ʿalaykum innamā tuj'zawna mā kuntum taʿmalūna

"Ku shigẽ ta. To, ku yi haƙuri ko kuma kada ku yi haƙuri, dai dai ne a kanku, kawai anã yi muku sakamakon abin da kuka kasance kunã aikatãwa."

17

إِنَّ ٱلْمُتَّقِينَ فِى جَنَّـٰتٍۢ وَنَعِيمٍۢ

inna l-mutaqīna fī jannātin wanaʿīmin

Lalle, mãsu taƙawa, sunã a cikin gidãjen Aljanna da wata ni'ima.

18

فَـٰكِهِينَ بِمَآ ءَاتَىٰهُمْ رَبُّهُمْ وَوَقَىٰهُمْ رَبُّهُمْ عَذَابَ ٱلْجَحِيمِ

fākihīna bimā ātāhum rabbuhum wawaqāhum rabbuhum ʿadhāba l-jaḥīmi

Sunã mãsu jin dãɗi da abin da Ubangijinsu Ya ba su, kuma Ubangijinsu Ya tsãre musu azãbar Jahĩm.

19

كُلُوا۟ وَٱشْرَبُوا۟ هَنِيٓـًٔۢا بِمَا كُنتُمْ تَعْمَلُونَ

kulū wa-ish'rabū hanīan bimā kuntum taʿmalūna

(A ce musu): "Ku ci, ku sha, da ni'ima, dõmin abin da kuka kasance kunã aikatãwa."

20

مُتَّكِـِٔينَ عَلَىٰ سُرُرٍۢ مَّصْفُوفَةٍۢ ۖ وَزَوَّجْنَـٰهُم بِحُورٍ عِينٍۢ

muttakiīna ʿalā sururin maṣfūfatin wazawwajnāhum biḥūrin ʿīnin

Sunã kishingiɗe a kan karagu waɗanda ke cikin sahu, kuma Muka aurar da su waɗansu mãtã mãsu farin idãnu, mãsu girmansu.

21

وَٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ وَٱتَّبَعَتْهُمْ ذُرِّيَّتُهُم بِإِيمَـٰنٍ أَلْحَقْنَا بِهِمْ ذُرِّيَّتَهُمْ وَمَآ أَلَتْنَـٰهُم مِّنْ عَمَلِهِم مِّن شَىْءٍۢ ۚ كُلُّ ٱمْرِئٍۭ بِمَا كَسَبَ رَهِينٌۭ

wa-alladhīna āmanū wa-ittabaʿathum dhurriyyatuhum biīmānin alḥaqnā bihim dhurriyyatahum wamā alatnāhum min ʿamalihim min shayin kullu im'ri-in bimā kasaba rahīnun

Kuma waɗanda suka yi ĩmãni kuma zũriyarsu 1suka bĩ su ga ĩmãnin, Mun riskar da zũriyarsu da su, alhãli kuwa bã da Mun rage musu kõme ba daga aikinsu, kõwane mutum jingina ne ga abin da ya sana'anta.

22

وَأَمْدَدْنَـٰهُم بِفَـٰكِهَةٍۢ وَلَحْمٍۢ مِّمَّا يَشْتَهُونَ

wa-amdadnāhum bifākihatin walaḥmin mimmā yashtahūna

Kuma Muka yalwata musu 'ya'yan itãce da nãma irin wanda suke marmari.

23

يَتَنَـٰزَعُونَ فِيهَا كَأْسًۭا لَّا لَغْوٌۭ فِيهَا وَلَا تَأْثِيمٌۭ

yatanāzaʿūna fīhā kasan lā laghwun fīhā walā tathīmun

Sunã mĩƙa wa jũnansu a cikinta hinjãlan giya, wadda bãbu yãsassar magana a cikinta, kuma bãbu jin nauyin zunubi.

24

۞ وَيَطُوفُ عَلَيْهِمْ غِلْمَانٌۭ لَّهُمْ كَأَنَّهُمْ لُؤْلُؤٌۭ مَّكْنُونٌۭ

wayaṭūfu ʿalayhim ghil'mānun lahum ka-annahum lu'lu-on maknūnun

Kuma waɗansu samãri nã gẽwayãwa a kansu, kamar dai sũ lu'ulu'u ne wanda ke kulle.

25

وَأَقْبَلَ بَعْضُهُمْ عَلَىٰ بَعْضٍۢ يَتَسَآءَلُونَ

wa-aqbala baʿḍuhum ʿalā baʿḍin yatasāalūna

Waɗansunsu suka fuskanta zuwa ga waɗansu, sunã tambayar jũna.

26

قَالُوٓا۟ إِنَّا كُنَّا قَبْلُ فِىٓ أَهْلِنَا مُشْفِقِينَ

qālū innā kunnā qablu fī ahlinā mush'fiqīna

Suka ce: "Lalle mũ mun kasance a gabãnin wannan (a dũniya) a cikin iyãlanmu munã jin tsõro."

27

فَمَنَّ ٱللَّهُ عَلَيْنَا وَوَقَىٰنَا عَذَابَ ٱلسَّمُومِ

famanna l-lahu ʿalaynā wawaqānā ʿadhāba l-samūmi

"To, Allah Yã yi mana kyautar falala, kuma Yã tsare mana azãbar iskar zãfi."

28

إِنَّا كُنَّا مِن قَبْلُ نَدْعُوهُ ۖ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلْبَرُّ ٱلرَّحِيمُ

innā kunnā min qablu nadʿūhu innahu huwa l-baru l-raḥīmu

"Lalle mũ mun kasance, a gãbanin haka, munã kiran sa. Lalle Shĩ, Shĩ ne Mai kyautatãwa, Mai rahama."

29

فَذَكِّرْ فَمَآ أَنتَ بِنِعْمَتِ رَبِّكَ بِكَاهِنٍۢ وَلَا مَجْنُونٍ

fadhakkir famā anta biniʿ'mati rabbika bikāhinin walā majnūnin

To, ka tunãtar kai fa sabõda ni'imar Ubangjinka, bã bõka kake ba, kuma bã mahaukaci ba.

30

أَمْ يَقُولُونَ شَاعِرٌۭ نَّتَرَبَّصُ بِهِۦ رَيْبَ ٱلْمَنُونِ

am yaqūlūna shāʿirun natarabbaṣu bihi rayba l-manūni

Shin zã su ce: "Mawãƙi ne, munã jiran, masĩfun mutuwa game da shĩ"?

31

قُلْ تَرَبَّصُوا۟ فَإِنِّى مَعَكُم مِّنَ ٱلْمُتَرَبِّصِينَ

qul tarabbaṣū fa-innī maʿakum mina l-mutarabiṣīna

Ka ce: "Ku yi jira, domin nĩ ma lalle inã a cikin mãsu jira tãre da ku."

32

أَمْ تَأْمُرُهُمْ أَحْلَـٰمُهُم بِهَـٰذَآ ۚ أَمْ هُمْ قَوْمٌۭ طَاغُونَ

am tamuruhum aḥlāmuhum bihādhā am hum qawmun ṭāghūna

Shin, hankulansu ne ke umarin su da wannan, kõ kuwa sũ wasu mutãne ne mãsu ƙetare haddi?

33

أَمْ يَقُولُونَ تَقَوَّلَهُۥ ۚ بَل لَّا يُؤْمِنُونَ

am yaqūlūna taqawwalahu bal lā yu'minūna

Shin, cẽwa suke yi: "Shi ne ke ƙãga faɗarsa"? Ã'a ba su dai yi ĩmãni ba.

34

فَلْيَأْتُوا۟ بِحَدِيثٍۢ مِّثْلِهِۦٓ إِن كَانُوا۟ صَـٰدِقِينَ

falyatū biḥadīthin mith'lihi in kānū ṣādiqīna

Sai su zõ da wani lãbãri mai misãlinsa idan sun kasance sũmãsu gaskiya ne.

35

أَمْ خُلِقُوا۟ مِنْ غَيْرِ شَىْءٍ أَمْ هُمُ ٱلْخَـٰلِقُونَ

am khuliqū min ghayri shayin am humu l-khāliqūna

Shin, an halitta su ne bã daga kõme ba, kõ kuwa sũ ne mãsu yin halitta?

36

أَمْ خَلَقُوا۟ ٱلسَّمَـٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضَ ۚ بَل لَّا يُوقِنُونَ

am khalaqū l-samāwāti wal-arḍa bal lā yūqinūna

Shin, sun halitta sammai da ƙasa ne? Ã'a ba su dai yi ĩmãnin yaƙĩni ba.

37

أَمْ عِندَهُمْ خَزَآئِنُ رَبِّكَ أَمْ هُمُ ٱلْمُصَۣيْطِرُونَ

am ʿindahum khazāinu rabbika am humu l-muṣayṭirūna

Shin, taskõkin Ubangijinka, sunã a wurinsu ne? Kõ kuwa sũ ne mãsu rinjãya?

38

أَمْ لَهُمْ سُلَّمٌۭ يَسْتَمِعُونَ فِيهِ ۖ فَلْيَأْتِ مُسْتَمِعُهُم بِسُلْطَـٰنٍۢ مُّبِينٍ

am lahum sullamun yastamiʿūna fīhi falyati mus'tamiʿuhum bisul'ṭānin mubīnin

Shin, sunã da wani tsãni ne wanda suke (hawa sunã) saurãron (lãbãrin samã) a cikinsa? Sai mai saurarõnsu ya zo da wani dalĩli bayyananne.

39

أَمْ لَهُ ٱلْبَنَـٰتُ وَلَكُمُ ٱلْبَنُونَ

am lahu l-banātu walakumu l-banūna

Shin, Yanã da1 'ya'ya mãtã ne kuma kũ, kunã da ɗiya maza ne?

40

أَمْ تَسْـَٔلُهُمْ أَجْرًۭا فَهُم مِّن مَّغْرَمٍۢ مُّثْقَلُونَ

am tasaluhum ajran fahum min maghramin muth'qalūna

Shin, kanã tambayar su wata ijãra ne, sabõda haka suka zama mãsu jin nauyin biyan tãrar?

41

أَمْ عِندَهُمُ ٱلْغَيْبُ فَهُمْ يَكْتُبُونَ

am ʿindahumu l-ghaybu fahum yaktubūna

Shin, a wurinsu akwai ilmin gaibi, sabõda haka sunã rubũtãwa?

42

أَمْ يُرِيدُونَ كَيْدًۭا ۖ فَٱلَّذِينَ كَفَرُوا۟ هُمُ ٱلْمَكِيدُونَ

am yurīdūna kaydan fa-alladhīna kafarū humu l-makīdūna

Shin, sunã nufin wani kaidi ne? To, waɗanda suka kãfirta sũ ne waɗanda ake yi wa kaidi.

43

أَمْ لَهُمْ إِلَـٰهٌ غَيْرُ ٱللَّهِ ۚ سُبْحَـٰنَ ٱللَّهِ عَمَّا يُشْرِكُونَ

am lahum ilāhun ghayru l-lahi sub'ḥāna l-lahi ʿammā yush'rikūna

Shin, sunã da wani abin bautãwa ne wanda bã Allah ba? Tsarki ya tabbata ga Allah daga abin da suke yi na shirki!

44

وَإِن يَرَوْا۟ كِسْفًۭا مِّنَ ٱلسَّمَآءِ سَاقِطًۭا يَقُولُوا۟ سَحَابٌۭ مَّرْكُومٌۭ

wa-in yaraw kis'fan mina l-samāi sāqiṭan yaqūlū saḥābun markūmun

Kuma idan sun ga wani ɓaɓɓake daga samã yãnã fãɗuwa, sai su ce wani girgije ne, mai hauhawar jũna.

45

فَذَرْهُمْ حَتَّىٰ يُلَـٰقُوا۟ يَوْمَهُمُ ٱلَّذِى فِيهِ يُصْعَقُونَ

fadharhum ḥattā yulāqū yawmahumu alladhī fīhi yuṣ'ʿaqūna

To, ka bar su, sai sun haɗu da yinin nan da za a sũmar da su a cikinsa.

46

يَوْمَ لَا يُغْنِى عَنْهُمْ كَيْدُهُمْ شَيْـًۭٔا وَلَا هُمْ يُنصَرُونَ

yawma lā yugh'nī ʿanhum kayduhum shayan walā hum yunṣarūna

Rãnar da kaidinsu bã ya wadãtar masu da kõme, kuma bã a taimakon su.

47

وَإِنَّ لِلَّذِينَ ظَلَمُوا۟ عَذَابًۭا دُونَ ذَٰلِكَ وَلَـٰكِنَّ أَكْثَرَهُمْ لَا يَعْلَمُونَ

wa-inna lilladhīna ẓalamū ʿadhāban dūna dhālika walākinna aktharahum lā yaʿlamūna

Kuma lalle, waɗannan da suka yi zãluncin, sunã da azãba (a nan dũniya) banda waccan, kuma mafi yawansu ba su sani ba.

48

وَٱصْبِرْ لِحُكْمِ رَبِّكَ فَإِنَّكَ بِأَعْيُنِنَا ۖ وَسَبِّحْ بِحَمْدِ رَبِّكَ حِينَ تَقُومُ

wa-iṣ'bir liḥuk'mi rabbika fa-innaka bi-aʿyuninā wasabbiḥ biḥamdi rabbika ḥīna taqūmu

Sai ka yi hakuri da hukuncin Ubangijinka, lalle kai fa kanã idãnun Mu, kuma ka tsarkake1 Ubangijinka da (tasbĩhi) game da gõde Masa a lõkacin da kake tãshi tsaye (dõmin salla kõ wani abu).

49

وَمِنَ ٱلَّيْلِ فَسَبِّحْهُ وَإِدْبَـٰرَ ٱلنُّجُومِ

wamina al-layli fasabbiḥ'hu wa-id'bāra l-nujūmi

Kuma daga dare, sai ka tsarkake Shi (da tasbĩhin) da lõkacin jũyãwar taurãri.

Game da Wannan Sura