51

الذاريات

Adh-Dhariyat

The Winnowing Winds

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ Da sunan Allah Mai rahama Mai jin kai
Ayoyi 60
Juzu'i 26-27
Shafi 520-523
Nau'i Makkiya
Tsarin Saukarwa 67
0:00 / 0:00
Aya: 1 / 60
1

وَٱلذَّٰرِيَـٰتِ ذَرْوًۭا

wal-dhāriyāti dharwan

Inã rantsuwa da iskõki mãsu shẽkar abũbuwa, shẽƙẽwa.

2

فَٱلْحَـٰمِلَـٰتِ وِقْرًۭا

fal-ḥāmilāti wiq'ran

Sa'an nan da girãgizai mãsu ɗaukar nauyi (na ruwa).

3

فَٱلْجَـٰرِيَـٰتِ يُسْرًۭا

fal-jāriyāti yus'ran

Sa'an nan da jirãge mãsu gudãna (a kan ruwa) da sauƙi.

4

فَٱلْمُقَسِّمَـٰتِ أَمْرًا

fal-muqasimāti amran

Sa'an nan da Malã'iku mãsu rabon al'amari (bisa umurnin Allah).

5

إِنَّمَا تُوعَدُونَ لَصَادِقٌۭ

innamā tūʿadūna laṣādiqun

Lalle abin da ake yi muku alkawari (da zuwansa), haƙĩƙa gaskiya ne.

6

وَإِنَّ ٱلدِّينَ لَوَٰقِعٌۭ

wa-inna l-dīna lawāqiʿun

Kuma lalle sakamako (ga ayyukanku), haƙĩƙa, mai aukuwa ne

7

وَٱلسَّمَآءِ ذَاتِ ٱلْحُبُكِ

wal-samāi dhāti l-ḥubuki

Inã rantsuwa da samã ma'abũciyar hanyõyi (na tafiyar taurãri da sautin rediyo).

8

إِنَّكُمْ لَفِى قَوْلٍۢ مُّخْتَلِفٍۢ

innakum lafī qawlin mukh'talifin

Lalle kũ, haƙĩƙa, kunã cikin magana mai sãɓa wa juna (game da Alƙur'ani).

9

يُؤْفَكُ عَنْهُ مَنْ أُفِكَ

yu'faku ʿanhu man ufika

Anã karkatar da wanda aka jũyar (daga gaskiya).

10

قُتِلَ ٱلْخَرَّٰصُونَ

qutila l-kharāṣūna

An la'ani mãsu ƙiri-faɗi.

11

ٱلَّذِينَ هُمْ فِى غَمْرَةٍۢ سَاهُونَ

alladhīna hum fī ghamratin sāhūna

Waɗanda suke shagala a cikin zurfin jãhilci.

12

يَسْـَٔلُونَ أَيَّانَ يَوْمُ ٱلدِّينِ

yasalūna ayyāna yawmu l-dīni

Sunã tambaya: "Yaushe ne rãnar sakamako zã ta auku?"

13

يَوْمَ هُمْ عَلَى ٱلنَّارِ يُفْتَنُونَ

yawma hum ʿalā l-nāri yuf'tanūna

Ranar da suke a kan wuta anã fitinar su.

14

ذُوقُوا۟ فِتْنَتَكُمْ هَـٰذَا ٱلَّذِى كُنتُم بِهِۦ تَسْتَعْجِلُونَ

dhūqū fit'natakum hādhā alladhī kuntum bihi tastaʿjilūna

(A ce musu): "Ku ɗanɗani fitinarku, wannan shĩ ne abin da kuka kasance kunã nẽman zuwansa da gaggãwa."

15

إِنَّ ٱلْمُتَّقِينَ فِى جَنَّـٰتٍۢ وَعُيُونٍ

inna l-mutaqīna fī jannātin waʿuyūnin

Lalle mãsu taƙawa, sunã a cikin lambunan itãce da marẽmari.

16

ءَاخِذِينَ مَآ ءَاتَىٰهُمْ رَبُّهُمْ ۚ إِنَّهُمْ كَانُوا۟ قَبْلَ ذَٰلِكَ مُحْسِنِينَ

ākhidhīna mā ātāhum rabbuhum innahum kānū qabla dhālika muḥ'sinīna

Sunã mãsu dĩbar abin da Ubangijinsu Ya bã su. Lalle sũ, sun kasance mãsu kyautatãwa a gabãnin haka (a dũniya).

17

كَانُوا۟ قَلِيلًۭا مِّنَ ٱلَّيْلِ مَا يَهْجَعُونَ

kānū qalīlan mina al-layli mā yahjaʿūna

Sun kasance a lõkaci kaɗan na dare suke yin barci.

18

وَبِٱلْأَسْحَارِ هُمْ يَسْتَغْفِرُونَ

wabil-asḥāri hum yastaghfirūna

Kuma a lõkutan asuba sunã ta yin istigfãri.

19

وَفِىٓ أَمْوَٰلِهِمْ حَقٌّۭ لِّلسَّآئِلِ وَٱلْمَحْرُومِ

wafī amwālihim ḥaqqun lilssāili wal-maḥrūmi

Kuma a cikin dũkiyarsu akwai hakki ga (matalauci) mai rõƙo da wanda aka hana wa rõƙo.

20

وَفِى ٱلْأَرْضِ ءَايَـٰتٌۭ لِّلْمُوقِنِينَ

wafī l-arḍi āyātun lil'mūqinīna

Kuma a cikin ƙasã akwai ãyõyi ga mãsu yaƙĩni.

21

وَفِىٓ أَنفُسِكُمْ ۚ أَفَلَا تُبْصِرُونَ

wafī anfusikum afalā tub'ṣirūna

Kuma a cikin rãyukanku (akwai ãyõyi). To, bã zã ku dũbã ba?

22

وَفِى ٱلسَّمَآءِ رِزْقُكُمْ وَمَا تُوعَدُونَ

wafī l-samāi riz'qukum wamā tūʿadūna

Kuma a cikin sama arzikinku (yake fitõwa) da abin da ake yi muku alkawari.

23

فَوَرَبِّ ٱلسَّمَآءِ وَٱلْأَرْضِ إِنَّهُۥ لَحَقٌّۭ مِّثْلَ مَآ أَنَّكُمْ تَنطِقُونَ

fawarabbi l-samāi wal-arḍi innahu laḥaqqun mith'la mā annakum tanṭiqūna

To, kuma Ina rantsuwa da Ubangijin sama da ƙasã, lalle shĩ (abin da ake yi muku alkawari), haƙĩƙa gaskiya ne, kamar abin da kuka zamo kunã karantãwa na magana,

24

هَلْ أَتَىٰكَ حَدِيثُ ضَيْفِ إِبْرَٰهِيمَ ٱلْمُكْرَمِينَ

hal atāka ḥadīthu ḍayfi ib'rāhīma l-muk'ramīna

Shin, lãbãrin Bãƙin Ibrãhĩm, waɗanda aka girmama, ya zo maka?

25

إِذْ دَخَلُوا۟ عَلَيْهِ فَقَالُوا۟ سَلَـٰمًۭا ۖ قَالَ سَلَـٰمٌۭ قَوْمٌۭ مُّنكَرُونَ

idh dakhalū ʿalayhi faqālū salāman qāla salāmun qawmun munkarūna

A lõkacin da suka shiga gare shi, sai suka yi sallama; ya ce "Aminci ya tabbata a gare ku, mutãne bãƙi!"

26

فَرَاغَ إِلَىٰٓ أَهْلِهِۦ فَجَآءَ بِعِجْلٍۢ سَمِينٍۢ

farāgha ilā ahlihi fajāa biʿij'lin samīnin

Sai ya jũya zuwa ga iyãlinsa, sa'an nan ya zo da maraƙi tutturna,

27

فَقَرَّبَهُۥٓ إِلَيْهِمْ قَالَ أَلَا تَأْكُلُونَ

faqarrabahu ilayhim qāla alā takulūna

Sai ya kusantar da shi zuwa gare su, ya ce: "Bã zã ku ci ba?"

28

فَأَوْجَسَ مِنْهُمْ خِيفَةًۭ ۖ قَالُوا۟ لَا تَخَفْ ۖ وَبَشَّرُوهُ بِغُلَـٰمٍ عَلِيمٍۢ

fa-awjasa min'hum khīfatan qālū lā takhaf wabasharūhu bighulāmin ʿalīmin

Sai ya ji tsõro daga gare su. Suka ce: "Kada kaji tsõro." Kuma suka yi masa bushãra da (haihuwar) wani yaro mai ilmi.

29

فَأَقْبَلَتِ ٱمْرَأَتُهُۥ فِى صَرَّةٍۢ فَصَكَّتْ وَجْهَهَا وَقَالَتْ عَجُوزٌ عَقِيمٌۭ

fa-aqbalati im'ra-atuhu fī ṣarratin faṣakkat wajhahā waqālat ʿajūzun ʿaqīmun

Sai matarsa ta fuskanta cikin ƙyallõwa, har ta mari fuskarta kuma ta ce: "Tsõhuwa bakarãriya (zã ta haihu)!"

30

قَالُوا۟ كَذَٰلِكِ قَالَ رَبُّكِ ۖ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلْحَكِيمُ ٱلْعَلِيمُ

qālū kadhāliki qāla rabbuki innahu huwa l-ḥakīmu l-ʿalīmu

Suka ce: "Kamar haka Ubangijinki Ya faɗa. Lalle Shĩ, Shĩ ne Mai hikima, Mai ilmi."

31

۞ قَالَ فَمَا خَطْبُكُمْ أَيُّهَا ٱلْمُرْسَلُونَ

qāla famā khaṭbukum ayyuhā l-mur'salūna

(Ibrãĩm) ya ce: "To mẽne ne babban al'almarinku, yã kũ Manzanni!"

32

قَالُوٓا۟ إِنَّآ أُرْسِلْنَآ إِلَىٰ قَوْمٍۢ مُّجْرِمِينَ

qālū innā ur'sil'nā ilā qawmin muj'rimīna

Suka ce: "Lalle mũ, an aike mu zuwa ga waɗansu mutãne, mãsu laifi.

33

لِنُرْسِلَ عَلَيْهِمْ حِجَارَةًۭ مِّن طِينٍۢ

linur'sila ʿalayhim ḥijāratan min ṭīnin

"Dõmin mu saka musu waɗansu duwãtsu na wani yumɓu (bom).

34

مُّسَوَّمَةً عِندَ رَبِّكَ لِلْمُسْرِفِينَ

musawwamatan ʿinda rabbika lil'mus'rifīna

"Waɗanda aka yi wa alãma daga wajen Ubangijinka, dõmin mãsu ɓarna."

35

فَأَخْرَجْنَا مَن كَانَ فِيهَا مِنَ ٱلْمُؤْمِنِينَ

fa-akhrajnā man kāna fīhā mina l-mu'minīna

Sa'an, nan Muka fitar da wanda ya kasance a cikinta daga mũminai.

36

فَمَا وَجَدْنَا فِيهَا غَيْرَ بَيْتٍۢ مِّنَ ٱلْمُسْلِمِينَ

famā wajadnā fīhā ghayra baytin mina l-mus'limīna

Sai dai ba mu sãmu ba, a cikinta, fãce gida guda na Musulmi.

37

وَتَرَكْنَا فِيهَآ ءَايَةًۭ لِّلَّذِينَ يَخَافُونَ ٱلْعَذَابَ ٱلْأَلِيمَ

wataraknā fīhā āyatan lilladhīna yakhāfūna l-ʿadhāba l-alīma

Kuma Muka bar wata ãyã, a cikinta, ga waɗanda ke jin tsõron azãba, mai raɗaɗi.

38

وَفِى مُوسَىٰٓ إِذْ أَرْسَلْنَـٰهُ إِلَىٰ فِرْعَوْنَ بِسُلْطَـٰنٍۢ مُّبِينٍۢ

wafī mūsā idh arsalnāhu ilā fir'ʿawna bisul'ṭānin mubīnin

Kuma ga Mũsã, a lõkacin da Muka aiko shi zuwa ga Fir'auna da wani dalĩli bayyananne.

39

فَتَوَلَّىٰ بِرُكْنِهِۦ وَقَالَ سَـٰحِرٌ أَوْ مَجْنُونٌۭ

fatawallā biruk'nihi waqāla sāḥirun aw majnūnun

Sai ya jũya bãya tãre da ƙarfinsa, kuma ya ce: "Mai sihiri ne kõ kuwa mahaukaci!"

40

فَأَخَذْنَـٰهُ وَجُنُودَهُۥ فَنَبَذْنَـٰهُمْ فِى ٱلْيَمِّ وَهُوَ مُلِيمٌۭ

fa-akhadhnāhu wajunūdahu fanabadhnāhum fī l-yami wahuwa mulīmun

Sabõda haka, Muka kama shi tãre da rundunarsa, sa'an nan Muka jẽfa su a cikin tẽku, alhãli kuwa yanã wanda ake zargi.

41

وَفِى عَادٍ إِذْ أَرْسَلْنَا عَلَيْهِمُ ٱلرِّيحَ ٱلْعَقِيمَ

wafī ʿādin idh arsalnā ʿalayhimu l-rīḥa l-ʿaqīma

Kuma ga Ãdãwa, a lõkacin da Muka aika iska ƙẽƙasasshiya a kansu.

42

مَا تَذَرُ مِن شَىْءٍ أَتَتْ عَلَيْهِ إِلَّا جَعَلَتْهُ كَٱلرَّمِيمِ

mā tadharu min shayin atat ʿalayhi illā jaʿalathu kal-ramīmi

Bã ta barin kõme da ta jẽ a kansa, fãce ta mayar da shi kamar rududdugaggun ƙasũsuwa.

43

وَفِى ثَمُودَ إِذْ قِيلَ لَهُمْ تَمَتَّعُوا۟ حَتَّىٰ حِينٍۢ

wafī thamūda idh qīla lahum tamattaʿū ḥattā ḥīnin

Kuma ga Samũdãwa, a lõkacin da aka ce musu: "Ku ji ɗan dãɗi har wani ɗan lõkaci,"

44

فَعَتَوْا۟ عَنْ أَمْرِ رَبِّهِمْ فَأَخَذَتْهُمُ ٱلصَّـٰعِقَةُ وَهُمْ يَنظُرُونَ

faʿataw ʿan amri rabbihim fa-akhadhathumu l-ṣāʿiqatu wahum yanẓurūna

Sai suka yi girman kai ga umurnin Ubangijinsu, sabõda haka tsãwa ta kãma su, alhãli kuwa sunã kallo.

45

فَمَا ٱسْتَطَـٰعُوا۟ مِن قِيَامٍۢ وَمَا كَانُوا۟ مُنتَصِرِينَ

famā is'taṭāʿū min qiyāmin wamā kānū muntaṣirīna

Ba su kõ sãmu dãmar tsayãwa ba, kuma ba su kasance mãsu nẽman ãgaji ba.

46

وَقَوْمَ نُوحٍۢ مِّن قَبْلُ ۖ إِنَّهُمْ كَانُوا۟ قَوْمًۭا فَـٰسِقِينَ

waqawma nūḥin min qablu innahum kānū qawman fāsiqīna

Da mutãnen Nũhu a gabãnin haka, lalle sun kasance waɗansu irin mutãne ne fãsiƙai.

47

وَٱلسَّمَآءَ بَنَيْنَـٰهَا بِأَيْي۟دٍۢ وَإِنَّا لَمُوسِعُونَ

wal-samāa banaynāhā bi-aydin wa-innā lamūsiʿūna

Kuma sama, mun gina ta da wani irin ƙarfi, alhãli kuwa lalle Mũ ne Mãsu yalwatãwa.

48

وَٱلْأَرْضَ فَرَشْنَـٰهَا فَنِعْمَ ٱلْمَـٰهِدُونَ

wal-arḍa farashnāhā faniʿ'ma l-māhidūna

Kuma ƙasã Mun shimfiɗa ta, To, madalla da mãsu shimfiɗãwa, Mũ,

49

وَمِن كُلِّ شَىْءٍ خَلَقْنَا زَوْجَيْنِ لَعَلَّكُمْ تَذَكَّرُونَ

wamin kulli shayin khalaqnā zawjayni laʿallakum tadhakkarūna

Kuma daga kõme Mun halitta nau'i biyu, watakila zã ku yi tunãni.

50

فَفِرُّوٓا۟ إِلَى ٱللَّهِ ۖ إِنِّى لَكُم مِّنْهُ نَذِيرٌۭ مُّبِينٌۭ

fafirrū ilā l-lahi innī lakum min'hu nadhīrun mubīnun

Sabõda haka ku gudu zuwa ga Allah, lalle nĩ mai gargaɗi kawai ne a gare ku, mai bayyanannen gargaɗi.

51

وَلَا تَجْعَلُوا۟ مَعَ ٱللَّهِ إِلَـٰهًا ءَاخَرَ ۖ إِنِّى لَكُم مِّنْهُ نَذِيرٌۭ مُّبِينٌۭ

walā tajʿalū maʿa l-lahi ilāhan ākhara innī lakum min'hu nadhīrun mubīnun

Kuma kada ku sanya, tãre da Allah wani abin bautãwa na dabam, lalle nĩ, mai gargaɗi kawai ne a gare ku, mai bayyanannen gargaɗi.

52

كَذَٰلِكَ مَآ أَتَى ٱلَّذِينَ مِن قَبْلِهِم مِّن رَّسُولٍ إِلَّا قَالُوا۟ سَاحِرٌ أَوْ مَجْنُونٌ

kadhālika mā atā alladhīna min qablihim min rasūlin illā qālū sāḥirun aw majnūnun

Kamar haka dai wani Manzo bai jẽ wa waɗanda ke gabãninsu ba fãce sun ce: "Mai sihiri ne kõ mahaukaci."

53

أَتَوَاصَوْا۟ بِهِۦ ۚ بَلْ هُمْ قَوْمٌۭ طَاغُونَ

atawāṣaw bihi bal hum qawmun ṭāghūna

shin, sunã yi wa jũna wasiyya da shi ne? Ã'a, sũ dai mutãne ne mãsu girman kai.

54

فَتَوَلَّ عَنْهُمْ فَمَآ أَنتَ بِمَلُومٍۢ

fatawalla ʿanhum famā anta bimalūmin

Sai ka jũya daga barinsu, kuma kai ba abin zargi ba ne.

55

وَذَكِّرْ فَإِنَّ ٱلذِّكْرَىٰ تَنفَعُ ٱلْمُؤْمِنِينَ

wadhakkir fa-inna l-dhik'rā tanfaʿu l-mu'minīna

Kuma ka tunãtar, dõmin tunãtarwa tanã amfãnin mũminai.

56

وَمَا خَلَقْتُ ٱلْجِنَّ وَٱلْإِنسَ إِلَّا لِيَعْبُدُونِ

wamā khalaqtu l-jina wal-insa illā liyaʿbudūni

Kuma Ban halitta aljannu da mutãne ba sai dõmin su bauta Mini.

57

مَآ أُرِيدُ مِنْهُم مِّن رِّزْقٍۢ وَمَآ أُرِيدُ أَن يُطْعِمُونِ

mā urīdu min'hum min riz'qin wamā urīdu an yuṭ'ʿimūni

Bã Ni nufln (sãmun) wani arziki daga gare su, Bã Ni nufin su (yi Mini hidimar) ciyar da Ni.1

58

إِنَّ ٱللَّهَ هُوَ ٱلرَّزَّاقُ ذُو ٱلْقُوَّةِ ٱلْمَتِينُ

inna l-laha huwa l-razāqu dhū l-quwati l-matīnu

Lalle Allah, Shĩ ne Mai azurtãwa, Mai ĩkon yi, Mai cikakken ƙarfi.

59

فَإِنَّ لِلَّذِينَ ظَلَمُوا۟ ذَنُوبًۭا مِّثْلَ ذَنُوبِ أَصْحَـٰبِهِمْ فَلَا يَسْتَعْجِلُونِ

fa-inna lilladhīna ẓalamū dhanūban mith'la dhanūbi aṣḥābihim falā yastaʿjilūni

To, lalle waɗanda suka yi zãlunci sunã da masaki (na ɗĩban zunubi) kamar masakin abõkansu, sabõda haka kada su yi Mini gaggãwa.

60

فَوَيْلٌۭ لِّلَّذِينَ كَفَرُوا۟ مِن يَوْمِهِمُ ٱلَّذِى يُوعَدُونَ

fawaylun lilladhīna kafarū min yawmihimu alladhī yūʿadūna

Sabõda haka, bone ya tabbata ga waɗanda suka kãfirta, daga rãnar su wadda aka yi musu alkawari.

Game da Wannan Sura