الشمس
Ash-Shams
The Sun
وَٱلشَّمْسِ وَضُحَىٰهَا
wal-shamsi waḍuḥāhā
Ina rantsuwa da rãnã da hantsinta.
وَٱلْقَمَرِ إِذَا تَلَىٰهَا
wal-qamari idhā talāhā
Kuma da wata idan ya bi ta.
وَٱلنَّهَارِ إِذَا جَلَّىٰهَا
wal-nahāri idhā jallāhā
Da yini a lõkacin da ya bayyana ta.
وَٱلَّيْلِ إِذَا يَغْشَىٰهَا
wa-al-layli idhā yaghshāhā
Da dare a lõkacin da ya ke rufe ta.
وَٱلسَّمَآءِ وَمَا بَنَىٰهَا
wal-samāi wamā banāhā
Da sama da abin da ya gina ta.
وَٱلْأَرْضِ وَمَا طَحَىٰهَا
wal-arḍi wamā ṭaḥāhā
Da ƙasã da abin da ya shimfiɗa ta.
وَنَفْسٍۢ وَمَا سَوَّىٰهَا
wanafsin wamā sawwāhā
Da rai da abin da ya daidaita shi.
فَأَلْهَمَهَا فُجُورَهَا وَتَقْوَىٰهَا
fa-alhamahā fujūrahā wataqwāhā
Sa'an nan ya yi masa Ilhamar fãjircinsa da shiryuwarsa.
قَدْ أَفْلَحَ مَن زَكَّىٰهَا
qad aflaḥa man zakkāhā
Lalle ne wanda ya tsarkake1 shi (rai) ya sãmi babban rabo.
وَقَدْ خَابَ مَن دَسَّىٰهَا
waqad khāba man dassāhā
Kuma lalle ne wanda ya turbuɗe1 shi (da laifi) ya tãɓe.
كَذَّبَتْ ثَمُودُ بِطَغْوَىٰهَآ
kadhabat thamūdu biṭaghwāhā
Samũdãwa sun ƙaryata (Annabinsu), dõmin girman kansu.
إِذِ ٱنۢبَعَثَ أَشْقَىٰهَا
idhi inbaʿatha ashqāhā
A lõkacin da mafi shaƙãwarsu ya tafi (wurin sõke rãkumar sãlihu).
فَقَالَ لَهُمْ رَسُولُ ٱللَّهِ نَاقَةَ ٱللَّهِ وَسُقْيَـٰهَا
faqāla lahum rasūlu l-lahi nāqata l-lahi wasuq'yāhā
Sai Manzon Allah ya gaya musu cewa: "Ina tsõratar da ku ga rãƙumar Allah da ruwan shanta!"
فَكَذَّبُوهُ فَعَقَرُوهَا فَدَمْدَمَ عَلَيْهِمْ رَبُّهُم بِذَنۢبِهِمْ فَسَوَّىٰهَا
fakadhabūhu faʿaqarūhā fadamdama ʿalayhim rabbuhum bidhanbihim fasawwāhā
Sai suka ƙaryata shi, sa'an nan suka sõke ta. Sabõda haka Ubangijinsu Ya darkãke su, sabõda zunubinsu. Sa'an nan Ya daidaita ta (azãbar ga mai laifi da maras laifi).
وَلَا يَخَافُ عُقْبَـٰهَا
walā yakhāfu ʿuq'bāhā
Kuma bã ya tsõron ãƙibarta (ita halakãwar).