79

النازعات

An-Nazi'at

Those Who Drag Forth

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ Da sunan Allah Mai rahama Mai jin kai
Ayoyi 46
Juzu'i 30
Shafi 583-584
Nau'i Makkiya
Tsarin Saukarwa 81
0:00 / 0:00
Aya: 1 / 46
1

وَٱلنَّـٰزِعَـٰتِ غَرْقًۭا

wal-nāziʿāti gharqan

Ina rantsuwa da mala'iku mãsu fisgar rãyuka (na kafirai) da ƙarfi.

2

وَٱلنَّـٰشِطَـٰتِ نَشْطًۭا

wal-nāshiṭāti nashṭan

Da mãsu ɗibar rãyuka (na mũminai) da sauƙi a cikin nishãɗi.

3

وَٱلسَّـٰبِحَـٰتِ سَبْحًۭا

wal-sābiḥāti sabḥan

Da mãsu sauka daga sama da umurnin Allah kamar suna iyo.

4

فَٱلسَّـٰبِقَـٰتِ سَبْقًۭا

fal-sābiqāti sabqan

Sa'an nan, su zama mãsu gaugãwa (da umarnin Allah) kamar suna tsẽre.

5

فَٱلْمُدَبِّرَٰتِ أَمْرًۭا

fal-mudabirāti amran

Sa, an nan, su kasance masu shirya gudanar da umarni.

6

يَوْمَ تَرْجُفُ ٱلرَّاجِفَةُ

yawma tarjufu l-rājifatu

Rãnar da mai girgiza abũbuwa (bũsar farko) zã ta kaɗa.

7

تَتْبَعُهَا ٱلرَّادِفَةُ

tatbaʿuhā l-rādifatu

Mai biyar ta (bũsa ta biyu) nã biye.

8

قُلُوبٌۭ يَوْمَئِذٍۢ وَاجِفَةٌ

qulūbun yawma-idhin wājifatun

Wasu zukãta, a rãnar nan, mãsu jin tsõro ne.

9

أَبْصَـٰرُهَا خَـٰشِعَةٌۭ

abṣāruhā khāshiʿatun

Alhãli idãnunsu na ƙasƙantattu.

10

يَقُولُونَ أَءِنَّا لَمَرْدُودُونَ فِى ٱلْحَافِرَةِ

yaqūlūna a-innā lamardūdūna fī l-ḥāfirati

Sunã cẽwa "Ashe lalle zã a iya mayar da mu a kan sãwunmu?

11

أَءِذَا كُنَّا عِظَـٰمًۭا نَّخِرَةًۭ

a-idhā kunnā ʿiẓāman nakhiratan

"Ashe, idan muka zama ƙasusuwa rududdugaggu?"

12

قَالُوا۟ تِلْكَ إِذًۭا كَرَّةٌ خَاسِرَةٌۭ

qālū til'ka idhan karratun khāsiratun

Suka ce: "Waccan kam kõmãwa ce, tãɓaɓɓiya!"

13

فَإِنَّمَا هِىَ زَجْرَةٌۭ وَٰحِدَةٌۭ

fa-innamā hiya zajratun wāḥidatun

To, ita kam, tsãwa guda kawai ce.

14

فَإِذَا هُم بِٱلسَّاهِرَةِ

fa-idhā hum bil-sāhirati

Sai kawai gã su a bãyan ƙasa.

15

هَلْ أَتَىٰكَ حَدِيثُ مُوسَىٰٓ

hal atāka ḥadīthu mūsā

Shin, lãbãrin Mũsã ya zo maka?

16

إِذْ نَادَىٰهُ رَبُّهُۥ بِٱلْوَادِ ٱلْمُقَدَّسِ طُوًى

idh nādāhu rabbuhu bil-wādi l-muqadasi ṭuwan

A lõkacin da Ubangijinsa Ya kirãye shi, a cikin kwari mai tsarki, wato Duwã?

17

ٱذْهَبْ إِلَىٰ فِرْعَوْنَ إِنَّهُۥ طَغَىٰ

idh'hab ilā fir'ʿawna innahu ṭaghā

Ka tafi zuwa ga Fir'auna, lalle ne shi, ya ƙẽtare haddi.

18

فَقُلْ هَل لَّكَ إِلَىٰٓ أَن تَزَكَّىٰ

faqul hal laka ilā an tazakkā

"Sai ka ce masa, Kõ zã ka so ka tsarkaka.

19

وَأَهْدِيَكَ إِلَىٰ رَبِّكَ فَتَخْشَىٰ

wa-ahdiyaka ilā rabbika fatakhshā

"Kuma in shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka domin ka ji tsoron Sa?"

20

فَأَرَىٰهُ ٱلْـَٔايَةَ ٱلْكُبْرَىٰ

fa-arāhu l-āyata l-kub'rā

Sai ya nũna masa ãyar1 nan mafi girma.

21

فَكَذَّبَ وَعَصَىٰ

fakadhaba waʿaṣā

Sai ya ƙaryata, kuma ya sãɓa (umurni),

22

ثُمَّ أَدْبَرَ يَسْعَىٰ

thumma adbara yasʿā

Sa'an nan ya jũya bãya, yanã tafiya da sauri.

23

فَحَشَرَ فَنَادَىٰ

faḥashara fanādā

Sai ya yi gayya, sa'an nan ya yi kira.

24

فَقَالَ أَنَا۠ رَبُّكُمُ ٱلْأَعْلَىٰ

faqāla anā rabbukumu l-aʿlā

Sai ya ce: "Nĩ ne Ubangijinku mafi ɗaudaka."

25

فَأَخَذَهُ ٱللَّهُ نَكَالَ ٱلْـَٔاخِرَةِ وَٱلْأُولَىٰٓ

fa-akhadhahu l-lahu nakāla l-ākhirati wal-ūlā

Sabõda haka Allah Ya kama shi, dõmin azãbar maganar ƙarshe da ta farko.

26

إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَعِبْرَةًۭ لِّمَن يَخْشَىٰٓ

inna fī dhālika laʿib'ratan liman yakhshā

Lalle ne, a cikin wannan haƙiƙa akwai abin kula ga wanda yake tsõron Allah.

27

ءَأَنتُمْ أَشَدُّ خَلْقًا أَمِ ٱلسَّمَآءُ ۚ بَنَىٰهَا

a-antum ashaddu khalqan ami l-samāu banāhā

Shin, kũ ne mafi wuyar halitta ko sama? Allah Ya gina ta.

28

رَفَعَ سَمْكَهَا فَسَوَّىٰهَا

rafaʿa samkahā fasawwāhā

Ya ɗaukaka rufinta, sa'an nan Ya daidaita ta.

29

وَأَغْطَشَ لَيْلَهَا وَأَخْرَجَ ضُحَىٰهَا

wa-aghṭasha laylahā wa-akhraja ḍuḥāhā

Kuma Ya duhuntar da darenta, kuma Ya fitar da hantsinta.

30

وَٱلْأَرْضَ بَعْدَ ذَٰلِكَ دَحَىٰهَآ

wal-arḍa baʿda dhālika daḥāhā

Kuma, ƙasa a bayan haka Ya mulmula ta.

31

أَخْرَجَ مِنْهَا مَآءَهَا وَمَرْعَىٰهَا

akhraja min'hā māahā wamarʿāhā

Ya fitar da ruwanta daga gare ta da makiyãyarta.

32

وَٱلْجِبَالَ أَرْسَىٰهَا

wal-jibāla arsāhā

Da duwatsu, Yã kafe ta.

33

مَتَـٰعًۭا لَّكُمْ وَلِأَنْعَـٰمِكُمْ

matāʿan lakum wali-anʿāmikum

Domin jiyarwa dãɗi a gare ku, kuma ga dabbõbinku.

34

فَإِذَا جَآءَتِ ٱلطَّآمَّةُ ٱلْكُبْرَىٰ

fa-idhā jāati l-ṭāmatu l-kub'rā

To, idan uwar masĩfu, mafi girma, ta zo.

35

يَوْمَ يَتَذَكَّرُ ٱلْإِنسَـٰنُ مَا سَعَىٰ

yawma yatadhakkaru l-insānu mā saʿā

Rãnar da mutum zai yi tunãnin abin da ya aikata.

36

وَبُرِّزَتِ ٱلْجَحِيمُ لِمَن يَرَىٰ

waburrizati l-jaḥīmu liman yarā

Kuma, a bayyana Jahĩm ga mai gani.

37

فَأَمَّا مَن طَغَىٰ

fa-ammā man ṭaghā

To, amma wanda ya yi girman kai.

38

وَءَاثَرَ ٱلْحَيَوٰةَ ٱلدُّنْيَا

waāthara l-ḥayata l-dun'yā

Kuma, ya zãɓi rãyuwa ta kusa, (wato dũniya).

39

فَإِنَّ ٱلْجَحِيمَ هِىَ ٱلْمَأْوَىٰ

fa-inna l-jaḥīma hiya l-mawā

To, lalle ne Jahĩm, ita ce makõma.

40

وَأَمَّا مَنْ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِۦ وَنَهَى ٱلنَّفْسَ عَنِ ٱلْهَوَىٰ

wa-ammā man khāfa maqāma rabbihi wanahā l-nafsa ʿani l-hawā

Kuma, amma wanda ya ji tsõron tsayi a gaba ga Ubangijinsa, kuma ya kange kansa daga son rai.

41

فَإِنَّ ٱلْجَنَّةَ هِىَ ٱلْمَأْوَىٰ

fa-inna l-janata hiya l-mawā

To, lalle ne Aljanna ita ce makõma.

42

يَسْـَٔلُونَكَ عَنِ ٱلسَّاعَةِ أَيَّانَ مُرْسَىٰهَا

yasalūnaka ʿani l-sāʿati ayyāna mur'sāhā

Sunã tambayar ka game da sa'a, wai yaushe ne matabbatarta?

43

فِيمَ أَنتَ مِن ذِكْرَىٰهَآ

fīma anta min dhik'rāhā

Me ya haɗã ka da ambatonta?

44

إِلَىٰ رَبِّكَ مُنتَهَىٰهَآ

ilā rabbika muntahāhā

Zuwa ga Ubangijinka ƙarshen al'amarinta yake.

45

إِنَّمَآ أَنتَ مُنذِرُ مَن يَخْشَىٰهَا

innamā anta mundhiru man yakhshāhā

Kai mai gargaɗi kawai ne ga mai tsõron ta.

46

كَأَنَّهُمْ يَوْمَ يَرَوْنَهَا لَمْ يَلْبَثُوٓا۟ إِلَّا عَشِيَّةً أَوْ ضُحَىٰهَا

ka-annahum yawma yarawnahā lam yalbathū illā ʿashiyyatan aw ḍuḥāhā

Kamar sũ a rãnar da zã su gan ta, ba su zauna ba fãce a lõkacin marẽce ko hantsinsa.

Game da Wannan Sura