78

النبأ

An-Naba

The Tidings

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ Da sunan Allah Mai rahama Mai jin kai
Ayoyi 40
Juzu'i 30
Shafi 582-583
Nau'i Makkiya
Tsarin Saukarwa 80
0:00 / 0:00
Aya: 1 / 40
1

عَمَّ يَتَسَآءَلُونَ

ʿamma yatasāalūna

A kan mẽ suke tambayar jũna?

2

عَنِ ٱلنَّبَإِ ٱلْعَظِيمِ

ʿani l-naba-i l-ʿaẓīmi

A kan muhimmin lãbãri mai girma (Alƙur'ãni)?

3

ٱلَّذِى هُمْ فِيهِ مُخْتَلِفُونَ

alladhī hum fīhi mukh'talifūna

Wanda suke sãɓa wa jũna a cikinsa?

4

كَلَّا سَيَعْلَمُونَ

kallā sayaʿlamūna

A'aha! Zã su sani.

5

ثُمَّ كَلَّا سَيَعْلَمُونَ

thumma kallā sayaʿlamūna

Kuma, a'aha! Zã su sani.

6

أَلَمْ نَجْعَلِ ٱلْأَرْضَ مِهَـٰدًۭا

alam najʿali l-arḍa mihādan

Ashe, ba Mu sanya ƙasa shimfiɗa ba?

7

وَٱلْجِبَالَ أَوْتَادًۭا

wal-jibāla awtādan

Da duwãtsu turaku (ga riƙe ƙasa)?

8

وَخَلَقْنَـٰكُمْ أَزْوَٰجًۭا

wakhalaqnākum azwājan

Kuma, Mun halitta ku mazã da mãtã?

9

وَجَعَلْنَا نَوْمَكُمْ سُبَاتًۭا

wajaʿalnā nawmakum subātan

Kuma, Muka sanya barcinku hũtãwa?

10

وَجَعَلْنَا ٱلَّيْلَ لِبَاسًۭا

wajaʿalnā al-layla libāsan

Kuma, Muka sanya dare (ya zama) sutura?

11

وَجَعَلْنَا ٱلنَّهَارَ مَعَاشًۭا

wajaʿalnā l-nahāra maʿāshan

Kuma, Muka sanya yini (yazama) lõkacin nẽman abinci?

12

وَبَنَيْنَا فَوْقَكُمْ سَبْعًۭا شِدَادًۭا

wabanaynā fawqakum sabʿan shidādan

Kuma, Muka gina, a samanku, sammai bakwai mãsu ƙarfi?

13

وَجَعَلْنَا سِرَاجًۭا وَهَّاجًۭا

wajaʿalnā sirājan wahhājan

Kuma, Muka sanya fitila mai tsanin haske (rãnã)?

14

وَأَنزَلْنَا مِنَ ٱلْمُعْصِرَٰتِ مَآءًۭ ثَجَّاجًۭا

wa-anzalnā mina l-muʿ'ṣirāti māan thajjājan

Kuma, Muka saukar daga cikakkun girãgizai, ruwa mai yawan zuba?

15

لِّنُخْرِجَ بِهِۦ حَبًّۭا وَنَبَاتًۭا

linukh'rija bihi ḥabban wanabātan

Dõmin, Mu fitar da ƙwaya da tsiri game da shi?

16

وَجَنَّـٰتٍ أَلْفَافًا

wajannātin alfāfan

Da itãcen lambuna mãsu lillibniya?

17

إِنَّ يَوْمَ ٱلْفَصْلِ كَانَ مِيقَـٰتًۭا

inna yawma l-faṣli kāna mīqātan

Lalle ne, rãnar rarrabẽwa tã kasance abin ƙayyadẽ wa lõkaci.

18

يَوْمَ يُنفَخُ فِى ٱلصُّورِ فَتَأْتُونَ أَفْوَاجًۭا

yawma yunfakhu fī l-ṣūri fatatūna afwājan

Rãnar da zã a yi bũsa a cikin ƙaho, sai ku zo, jama'a jama'a.

19

وَفُتِحَتِ ٱلسَّمَآءُ فَكَانَتْ أَبْوَٰبًۭا

wafutiḥati l-samāu fakānat abwāban

Kuma, aka buɗe sama, sai ta kasance ƙõfõfi.

20

وَسُيِّرَتِ ٱلْجِبَالُ فَكَانَتْ سَرَابًا

wasuyyirati l-jibālu fakānat sarāban

Kuma, aka tafiyar da duwãtsu, sai suka kasance ƙũra.

21

إِنَّ جَهَنَّمَ كَانَتْ مِرْصَادًۭا

inna jahannama kānat mir'ṣādan

Lalle ne, Jahannama tã kasance madãkata.

22

لِّلطَّـٰغِينَ مَـَٔابًۭا

lilṭṭāghīna maāban

Ga mãsu ƙẽtare iyãkõki, tã zama makõma.

23

لَّـٰبِثِينَ فِيهَآ أَحْقَابًۭا

lābithīna fīhā aḥqāban

Sunã, mãsu zama a cikinta, zãmunna.

24

لَّا يَذُوقُونَ فِيهَا بَرْدًۭا وَلَا شَرَابًا

lā yadhūqūna fīhā bardan walā sharāban

Bã su ɗanɗanãwar wani sanyi a cikinta, kuma bã su ɗanɗana abin sha.

25

إِلَّا حَمِيمًۭا وَغَسَّاقًۭا

illā ḥamīman waghassāqan

Fãce tafasasshen ruwa da ruɓaɓɓen jini.

26

جَزَآءًۭ وِفَاقًا

jazāan wifāqan

Sakamako mai dãcẽwa.

27

إِنَّهُمْ كَانُوا۟ لَا يَرْجُونَ حِسَابًۭا

innahum kānū lā yarjūna ḥisāban

Lalle ne, sũ, sun kasance bã su fãtar sauƙin wani hisãbi.

28

وَكَذَّبُوا۟ بِـَٔايَـٰتِنَا كِذَّابًۭا

wakadhabū biāyātinā kidhāban

Kuma, suka ƙaryata game da ãyõyin Mu, ƙaryatãwa!

29

وَكُلَّ شَىْءٍ أَحْصَيْنَـٰهُ كِتَـٰبًۭا

wakulla shayin aḥṣaynāhu kitāban

Alhãli, kõwane abu Mun ƙididdigẽ shi, a rubũce.

30

فَذُوقُوا۟ فَلَن نَّزِيدَكُمْ إِلَّا عَذَابًا

fadhūqū falan nazīdakum illā ʿadhāban

Sabõda haka, ku ɗanɗana domin haka, bã zã Mu ƙara muku kõme ba fãce azãba.

31

إِنَّ لِلْمُتَّقِينَ مَفَازًا

inna lil'muttaqīna mafāzan

Lalle ne, mãsu taƙawã nã da wani wurin sãmun babban rabo.

32

حَدَآئِقَ وَأَعْنَـٰبًۭا

ḥadāiqa wa-aʿnāban

Lambuna da inabõbi.

33

وَكَوَاعِبَ أَتْرَابًۭا

wakawāʿiba atrāban

Da yan Mata tsaraikun Juna

34

وَكَأْسًۭا دِهَاقًۭا

wakasan dihāqan

Da hinjãlan giya cikakku.

35

لَّا يَسْمَعُونَ فِيهَا لَغْوًۭا وَلَا كِذَّٰبًۭا

lā yasmaʿūna fīhā laghwan walā kidhāban

Bã su jin yãsassar magana, a cikinta, kuma bã su jin ƙaryatãwa.

36

جَزَآءًۭ مِّن رَّبِّكَ عَطَآءً حِسَابًۭا

jazāan min rabbika ʿaṭāan ḥisāban

Dõmin sakamako daga Ubangijinka, kyautã mai yawa.

37

رَّبِّ ٱلسَّمَـٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ وَمَا بَيْنَهُمَا ٱلرَّحْمَـٰنِ ۖ لَا يَمْلِكُونَ مِنْهُ خِطَابًۭا

rabbi l-samāwāti wal-arḍi wamā baynahumā l-raḥmāni lā yamlikūna min'hu khiṭāban

Ubangijin sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu, Mai rahama, bã su da ikon yin wata magana daga gare Shi.

38

يَوْمَ يَقُومُ ٱلرُّوحُ وَٱلْمَلَـٰٓئِكَةُ صَفًّۭا ۖ لَّا يَتَكَلَّمُونَ إِلَّا مَنْ أَذِنَ لَهُ ٱلرَّحْمَـٰنُ وَقَالَ صَوَابًۭا

yawma yaqūmu l-rūḥu wal-malāikatu ṣaffan lā yatakallamūna illā man adhina lahu l-raḥmānu waqāla ṣawāban

Rãnar da Rũhi da malã'iku zã su tsaya a cikin safu, bã su magana, sai wanda Allah Ya yi masa izni, kuma ya faɗi abin da ke daidai.

39

ذَٰلِكَ ٱلْيَوْمُ ٱلْحَقُّ ۖ فَمَن شَآءَ ٱتَّخَذَ إِلَىٰ رَبِّهِۦ مَـَٔابًا

dhālika l-yawmu l-ḥaqu faman shāa ittakhadha ilā rabbihi maāban

Wancan, shi ne yini na gaskiya; to wanda ya so, ya riƙa makõma zuwa ga Ubangijinsa.

40

إِنَّآ أَنذَرْنَـٰكُمْ عَذَابًۭا قَرِيبًۭا يَوْمَ يَنظُرُ ٱلْمَرْءُ مَا قَدَّمَتْ يَدَاهُ وَيَقُولُ ٱلْكَافِرُ يَـٰلَيْتَنِى كُنتُ تُرَٰبًۢا

innā andharnākum ʿadhāban qarīban yawma yanẓuru l-maru mā qaddamat yadāhu wayaqūlu l-kāfiru yālaytanī kuntu turāban

Lalle ne, Mũ, Mun yi muku gargaɗin azãba makusanciya, rãnar da mutum ke dũbi zuwa ga abin da hannãyensa suka aikata, kuma kafiri ya ce: "Kaitona, dã dai nã zama turɓãya!"

Game da Wannan Sura