80

عبس

Abasa

He Frowned

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ Da sunan Allah Mai rahama Mai jin kai
Ayoyi 42
Juzu'i 30
Shafi 585-586
Nau'i Makkiya
Tsarin Saukarwa 24
0:00 / 0:00
Aya: 1 / 42
1

عَبَسَ وَتَوَلَّىٰٓ

ʿabasa watawallā

Yã game huska1 kuma ya jũya bãya.

2

أَن جَآءَهُ ٱلْأَعْمَىٰ

an jāahu l-aʿmā

Sabõda makãho yã je masa.

3

وَمَا يُدْرِيكَ لَعَلَّهُۥ يَزَّكَّىٰٓ

wamā yud'rīka laʿallahu yazzakkā

To, me ya sanar da kai cẽwa watakila shi ne zai tsarkaka.

4

أَوْ يَذَّكَّرُ فَتَنفَعَهُ ٱلذِّكْرَىٰٓ

aw yadhakkaru fatanfaʿahu l-dhik'rā

Ko ya tuna, dõmin tunãwar ta amfane shi?

5

أَمَّا مَنِ ٱسْتَغْنَىٰ

ammā mani is'taghnā

Amma wanda ya wadãtu da dũkiya.

6

فَأَنتَ لَهُۥ تَصَدَّىٰ

fa-anta lahu taṣaddā

Sa'an nan kai kuma ka ɗora bijira zuwa gare shi!

7

وَمَا عَلَيْكَ أَلَّا يَزَّكَّىٰ

wamā ʿalayka allā yazzakkā

To, me zai cũce ka idan bai tsarkaka ba?

8

وَأَمَّا مَن جَآءَكَ يَسْعَىٰ

wa-ammā man jāaka yasʿā

Kuma, amma wanda ya zomaka yana gaugãwa.

9

وَهُوَ يَخْشَىٰ

wahuwa yakhshā

Alhãli shĩ yanã jin tsõrõn Allah.

10

فَأَنتَ عَنْهُ تَلَهَّىٰ

fa-anta ʿanhu talahhā

Kai kuma kã shagala ga barinsa!

11

كَلَّآ إِنَّهَا تَذْكِرَةٌۭ

kallā innahā tadhkiratun

A'aha! Lalle ne, wannan tunãtarwa ce.

12

فَمَن شَآءَ ذَكَرَهُۥ

faman shāa dhakarahu

Sabõda wanda ya so ya tuna Shi (Allah).

13

فِى صُحُفٍۢ مُّكَرَّمَةٍۢ

fī ṣuḥufin mukarramatin

(Tunãtarwa ce) ta cikin littafai abãban girmamãwa,

14

مَّرْفُوعَةٍۢ مُّطَهَّرَةٍۭ

marfūʿatin muṭahharatin

Abãban ɗaukakãwa, abãban tsarkakẽwa.

15

بِأَيْدِى سَفَرَةٍۢ

bi-aydī safaratin

A cikin hannãyen mala'iku marubũta.

16

كِرَامٍۭ بَرَرَةٍۢ

kirāmin bararatin

Mãsu daraja, mãsu ɗã'a ga Allah.

17

قُتِلَ ٱلْإِنسَـٰنُ مَآ أَكْفَرَهُۥ

qutila l-insānu mā akfarahu

An la'ani mutum (kafiri). Mẽ yã yi kãfircinsa!

18

مِنْ أَىِّ شَىْءٍ خَلَقَهُۥ

min ayyi shayin khalaqahu

Daga wane abu, (Allah) Ya halitta shi?

19

مِن نُّطْفَةٍ خَلَقَهُۥ فَقَدَّرَهُۥ

min nuṭ'fatin khalaqahu faqaddarahu

Daga ɗigon maniyyi, Ya halitta shi sa'an nan Ya ƙaddarã shi (ga halaye).

20

ثُمَّ ٱلسَّبِيلَ يَسَّرَهُۥ

thumma l-sabīla yassarahu

Sa'an nan, hanyarsa ta fita Ya sauƙaƙe masa.

21

ثُمَّ أَمَاتَهُۥ فَأَقْبَرَهُۥ

thumma amātahu fa-aqbarahu

Sa'an nan, Ya matar da shi sai Ya sanya shi a cikin kabari.

22

ثُمَّ إِذَا شَآءَ أَنشَرَهُۥ

thumma idhā shāa ansharahu

Sa'an nan, idan Ya so lalle ne zai tãyar da shi.

23

كَلَّا لَمَّا يَقْضِ مَآ أَمَرَهُۥ

kallā lammā yaqḍi mā amarahu

Haƙĩƙa bai i da aikata abin da Allah Ya umurce shi ba (lõkacin sanya shi a cikin kabari).

24

فَلْيَنظُرِ ٱلْإِنسَـٰنُ إِلَىٰ طَعَامِهِۦٓ

falyanẓuri l-insānu ilā ṭaʿāmihi

To, mutum ya dũba zuwa ga abincinsa.

25

اَنَّا صَبَبْنَا ٱلْمَآءَ صَبًّۭا

annā ṣababnā l-māa ṣabban

Lalle ne Mũ, Mun zuo ruwa, zubõwa.

26

ثُمَّ شَقَقْنَا ٱلْأَرْضَ شَقًّۭا

thumma shaqaqnā l-arḍa shaqqan

Sa'an nan, Muka tsattsãge ƙasa tsattsagewa.

27

فَأَنۢبَتْنَا فِيهَا حَبًّۭا

fa-anbatnā fīhā ḥabban

Sa'an nan, Muka tsirar da ƙwaya, a cikinta.

28

وَعِنَبًۭا وَقَضْبًۭا

waʿinaban waqaḍban

Da inabi da ciyãwa.

29

وَزَيْتُونًۭا وَنَخْلًۭا

wazaytūnan wanakhlan

Da zaitũni da itãcen dabĩno.

30

وَحَدَآئِقَ غُلْبًۭا

waḥadāiqa ghul'ban

Da lambuna, mãsu yawan itãce.

31

وَفَـٰكِهَةًۭ وَأَبًّۭا

wafākihatan wa-abban

Da 'yã'yan itãcen marmari, da makiyãyã ta dabbõbi.

32

مَّتَـٰعًۭا لَّكُمْ وَلِأَنْعَـٰمِكُمْ

matāʿan lakum wali-anʿāmikum

Domin jin dãɗi a gare ku, ku da dabbobinku.

33

فَإِذَا جَآءَتِ ٱلصَّآخَّةُ

fa-idhā jāati l-ṣākhatu

To, idan mai tsãwa (busa ta biyu) ta zo.

34

يَوْمَ يَفِرُّ ٱلْمَرْءُ مِنْ أَخِيهِ

yawma yafirru l-maru min akhīhi

Rãnar da mutum yake gudu daga ɗan'uwansa.

35

وَأُمِّهِۦ وَأَبِيهِ

wa-ummihi wa-abīhi

Da uwarsa da ubansa.

36

وَصَـٰحِبَتِهِۦ وَبَنِيهِ

waṣāḥibatihi wabanīhi

Da mãtarsa da ɗiyansa.

37

لِكُلِّ ٱمْرِئٍۢ مِّنْهُمْ يَوْمَئِذٍۢ شَأْنٌۭ يُغْنِيهِ

likulli im'ri-in min'hum yawma-idhin shanun yugh'nīhi

Ga kõwane mutum daga cikinsu, a rãnar nan akwai wani sha'ani da ya ishe shi.

38

وُجُوهٌۭ يَوْمَئِذٍۢ مُّسْفِرَةٌۭ

wujūhun yawma-idhin mus'firatun

Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu haske ne.

39

ضَاحِكَةٌۭ مُّسْتَبْشِرَةٌۭ

ḍāḥikatun mus'tabshiratun

Mãsu dãriya ne, mãsu bushãra.

40

وَوُجُوهٌۭ يَوْمَئِذٍ عَلَيْهَا غَبَرَةٌۭ

wawujūhun yawma-idhin ʿalayhā ghabaratun

Wasu huskõki, a rãnar nan, akwai ƙũra a kansu.

41

تَرْهَقُهَا قَتَرَةٌ

tarhaquhā qataratun

Baƙi zai rufe su.

42

أُو۟لَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلْكَفَرَةُ ٱلْفَجَرَةُ

ulāika humu l-kafaratu l-fajaratu

Waɗannan sũ ne kãfirai fãjirai (ga ayyukansu).

Game da Wannan Sura