69

الحاقة

Al-Haqqah

The Reality

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ Da sunan Allah Mai rahama Mai jin kai
Ayoyi 52
Juzu'i 29
Shafi 566-568
Nau'i Makkiya
Tsarin Saukarwa 78
0:00 / 0:00
Aya: 1 / 52
1

ٱلْحَآقَّةُ

al-ḥāqatu

Kiran gaskiya!

2

مَا ٱلْحَآقَّةُ

mā l-ḥāqatu

Mẽne ne kiran gaskiya?

3

وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا ٱلْحَآقَّةُ

wamā adrāka mā l-ḥāqatu

Kuma mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽwa kiran gaskiya?

4

كَذَّبَتْ ثَمُودُ وَعَادٌۢ بِٱلْقَارِعَةِ

kadhabat thamūdu waʿādun bil-qāriʿati

Samũdãwa da Ãdãwa sun ƙaryatar da kiran gaskiya mai dũkar zũciya!

5

فَأَمَّا ثَمُودُ فَأُهْلِكُوا۟ بِٱلطَّاغِيَةِ

fa-ammā thamūdu fa-uh'likū bil-ṭāghiyati

To, amma Samũdãwa to, an halakãsu da tsãwa mai tsanani.

6

وَأَمَّا عَادٌۭ فَأُهْلِكُوا۟ بِرِيحٍۢ صَرْصَرٍ عَاتِيَةٍۢ

wa-ammā ʿādun fa-uh'likū birīḥin ṣarṣarin ʿātiyatin

Kuma amma Ãdãwa to, an halaka su da wata iska mai tsananin sauti wadda ta ƙẽtare haddi.

7

سَخَّرَهَا عَلَيْهِمْ سَبْعَ لَيَالٍۢ وَثَمَـٰنِيَةَ أَيَّامٍ حُسُومًۭا فَتَرَى ٱلْقَوْمَ فِيهَا صَرْعَىٰ كَأَنَّهُمْ أَعْجَازُ نَخْلٍ خَاوِيَةٍۢ

sakharahā ʿalayhim sabʿa layālin wathamāniyata ayyāmin ḥusūman fatarā l-qawma fīhā ṣarʿā ka-annahum aʿjāzu nakhlin khāwiyatin

(Allah) Ya hõre ta a kansu a cikin dare bakwai da yini takwas, biye da jũna, sabõda haka, kana ganin mutãne a cikinta kwance. Kamar sũ ƙirãruwan dabĩno ne, waɗanda suka fãɗi.

8

فَهَلْ تَرَىٰ لَهُم مِّنۢ بَاقِيَةٍۢ

fahal tarā lahum min bāqiyatin

To, kõ kanã ganin abin da ya yi saurã daga cikinsu?

9

وَجَآءَ فِرْعَوْنُ وَمَن قَبْلَهُۥ وَٱلْمُؤْتَفِكَـٰتُ بِٱلْخَاطِئَةِ

wajāa fir'ʿawnu waman qablahu wal-mu'tafikātu bil-khāṭi-ati

Kuma Fir'auna yã zo da waɗanda ke gabãninsa, da waɗannan da aka kife ƙasarsu, sabõda laifi.

10

فَعَصَوْا۟ رَسُولَ رَبِّهِمْ فَأَخَذَهُمْ أَخْذَةًۭ رَّابِيَةً

faʿaṣaw rasūla rabbihim fa-akhadhahum akhdhatan rābiyatan

Dõmin sun sãɓã wa manzon Ubangijinsu, sabõda haka ya kãmã su da wani irin kãmu mai ƙãruwar (tsanani).

11

إِنَّا لَمَّا طَغَا ٱلْمَآءُ حَمَلْنَـٰكُمْ فِى ٱلْجَارِيَةِ

innā lammā ṭaghā l-māu ḥamalnākum fī l-jāriyati

Lalle ne, Mũ, a lõkacin da ruwa ya ƙẽtare haddi, Munɗauke aaku a cikin jirgin ruwan nan.

12

لِنَجْعَلَهَا لَكُمْ تَذْكِرَةًۭ وَتَعِيَهَآ أُذُنٌۭ وَٰعِيَةٌۭ

linajʿalahā lakum tadhkiratan wataʿiyahā udhunun wāʿiyatun

Dõmin Mu sanya shi, gare ku abin tunãwa kuma wani kunne mai kiyayewa ya kiyaye (shi).

13

فَإِذَا نُفِخَ فِى ٱلصُّورِ نَفْخَةٌۭ وَٰحِدَةٌۭ

fa-idhā nufikha fī l-ṣūri nafkhatun wāḥidatun

To, idan an yi bũsa a cikin ƙaho, bũsa ɗaya.

14

وَحُمِلَتِ ٱلْأَرْضُ وَٱلْجِبَالُ فَدُكَّتَا دَكَّةًۭ وَٰحِدَةًۭ

waḥumilati l-arḍu wal-jibālu fadukkatā dakkatan wāḥidatan

Kuma aka ɗauki ƙasa da duwãtsu, kuma aka niƙa su niƙãwa ɗaya.

15

فَيَوْمَئِذٍۢ وَقَعَتِ ٱلْوَاقِعَةُ

fayawma-idhin waqaʿati l-wāqiʿatu

A ran nan, mai aukuwa zã ta auku.

16

وَٱنشَقَّتِ ٱلسَّمَآءُ فَهِىَ يَوْمَئِذٍۢ وَاهِيَةٌۭ

wa-inshaqqati l-samāu fahiya yawma-idhin wāhiyatun

Kuma sama zã ta tsãge, dõmin ita a ran nan, mai rauni ce.

17

وَٱلْمَلَكُ عَلَىٰٓ أَرْجَآئِهَا ۚ وَيَحْمِلُ عَرْشَ رَبِّكَ فَوْقَهُمْ يَوْمَئِذٍۢ ثَمَـٰنِيَةٌۭ

wal-malaku ʿalā arjāihā wayaḥmilu ʿarsha rabbika fawqahum yawma-idhin thamāniyatun

Kuma malã'iku (su bayyana) a kan sãsanninta, kuma wasu (malã'iku) takwas na ɗauke da Al'arshin Ubangijinka, a sama da su, a wannan rãnar.

18

يَوْمَئِذٍۢ تُعْرَضُونَ لَا تَخْفَىٰ مِنكُمْ خَافِيَةٌۭ

yawma-idhin tuʿ'raḍūna lā takhfā minkum khāfiyatun

A rãnar nan zã a bijirã ku (dõmin hisãbi), bãbu wani rai, mai ɓoyewa, daga cikinku, wanda zai iya ɓõyẽwa.

19

فَأَمَّا مَنْ أُوتِىَ كِتَـٰبَهُۥ بِيَمِينِهِۦ فَيَقُولُ هَآؤُمُ ٱقْرَءُوا۟ كِتَـٰبِيَهْ

fa-ammā man ūtiya kitābahu biyamīnihi fayaqūlu hāumu iq'raū kitābiyah

To, amma wanda aka bai wa littãfinsa a dãmansa, sai ya ce wa (makusantansa), "Ku karɓa, ku karanta littafina."

20

إِنِّى ظَنَنتُ أَنِّى مُلَـٰقٍ حِسَابِيَهْ

innī ẓanantu annī mulāqin ḥisābiyah

"Lalle ne ni, nã tabbata cewa ni mai haɗuwa da hisãbina ne."

21

فَهُوَ فِى عِيشَةٍۢ رَّاضِيَةٍۢ

fahuwa fī ʿīshatin rāḍiyatin

Sabõda haka, shi yana cikin wata rãyuwa yardadda.

22

فِى جَنَّةٍ عَالِيَةٍۢ

fī jannatin ʿāliyatin

A cikin Aljanna maɗaukakiya.

23

قُطُوفُهَا دَانِيَةٌۭ

quṭūfuhā dāniyatun

Nunannun 'yã'yan itãcenta makusantã ne (ga mai son ɗĩba),

24

كُلُوا۟ وَٱشْرَبُوا۟ هَنِيٓـًٔۢا بِمَآ أَسْلَفْتُمْ فِى ٱلْأَيَّامِ ٱلْخَالِيَةِ

kulū wa-ish'rabū hanīan bimā aslaftum fī l-ayāmi l-khāliyati

(Ana ce musu) "Ku ci, kuma ku sha a cikin ni'ima, sabõda abin da kuka gabãtar a cikin kwãnukan da suka shige."

25

وَأَمَّا مَنْ أُوتِىَ كِتَـٰبَهُۥ بِشِمَالِهِۦ فَيَقُولُ يَـٰلَيْتَنِى لَمْ أُوتَ كِتَـٰبِيَهْ

wa-ammā man ūtiya kitābahu bishimālihi fayaqūlu yālaytanī lam ūta kitābiyah

Kuma wanda aka bai wa littãfinsa ga hagunsa, sai ya ce: "Kaitona, ba a kãwo mini littãfina ba!"

26

وَلَمْ أَدْرِ مَا حِسَابِيَهْ

walam adri mā ḥisābiyah

"Kuma ban san abin da (ke sakamakon) hisãbina ba!"

27

يَـٰلَيْتَهَا كَانَتِ ٱلْقَاضِيَةَ

yālaytahā kānati l-qāḍiyata

"In dã dai ita, tã kasance mai halakã ni gabã ɗaya ce!

28

مَآ أَغْنَىٰ عَنِّى مَالِيَهْ ۜ

mā aghnā ʿannī māliyah

"Dukiyãta ba ta wadatar da ni ba!"

29

هَلَكَ عَنِّى سُلْطَـٰنِيَهْ

halaka ʿannī sul'ṭāniyah

"Ĩkona ya ɓace mini!"

30

خُذُوهُ فَغُلُّوهُ

khudhūhu faghullūhu

(Sai a ce wa malã'iku) "Ku kãmã shi, sa'an nan ku sanyã shi a cikin ƙuƙumi."

31

ثُمَّ ٱلْجَحِيمَ صَلُّوهُ

thumma l-jaḥīma ṣallūhu

"Sa'an nan, a cikin Jahĩm, ku ƙõna shi."

32

ثُمَّ فِى سِلْسِلَةٍۢ ذَرْعُهَا سَبْعُونَ ذِرَاعًۭا فَٱسْلُكُوهُ

thumma fī sil'silatin dharʿuhā sabʿūna dhirāʿan fa-us'lukūhu

"Sa'an nan, acikin sarƙa, tsawonta zirã'i saba'in, sai ku sanya shi."

33

إِنَّهُۥ كَانَ لَا يُؤْمِنُ بِٱللَّهِ ٱلْعَظِيمِ

innahu kāna lā yu'minu bil-lahi l-ʿaẓīmi

"Lalle ne, shi ya kasance ba ya yin ĩmãni da Allah, Mai girma!"

34

وَلَا يَحُضُّ عَلَىٰ طَعَامِ ٱلْمِسْكِينِ

walā yaḥuḍḍu ʿalā ṭaʿāmi l-mis'kīni

"Kuma ba ya kwaɗaitarwa ga (bãyar da) abincin matalauci!"

35

فَلَيْسَ لَهُ ٱلْيَوْمَ هَـٰهُنَا حَمِيمٌۭ

falaysa lahu l-yawma hāhunā ḥamīmun

"Sabõda haka, a yau, a nan, bã ya da masõyi."

36

وَلَا طَعَامٌ إِلَّا مِنْ غِسْلِينٍۢ

walā ṭaʿāmun illā min ghis'līnin

"Kuma bãbu wani abinci, sai daga (itãcen) gislĩn."

37

لَّا يَأْكُلُهُۥٓ إِلَّا ٱلْخَـٰطِـُٔونَ

lā yakuluhu illā l-khāṭiūna

"Bãbu mai cin sa sai mãsu ganganci."

38

فَلَآ أُقْسِمُ بِمَا تُبْصِرُونَ

falā uq'simu bimā tub'ṣirūna

To, ba sai Nã yi rantsuwa da abin da kuke iya gani ba,

39

وَمَا لَا تُبْصِرُونَ

wamā lā tub'ṣirūna

Da abin da bã ku iya gani.

40

إِنَّهُۥ لَقَوْلُ رَسُولٍۢ كَرِيمٍۢ

innahu laqawlu rasūlin karīmin

Lalle ne, shi (Alƙur'ani) tabbas maganar wani manzo (Jibirilu) mai daraja ne.

41

وَمَا هُوَ بِقَوْلِ شَاعِرٍۢ ۚ قَلِيلًۭا مَّا تُؤْمِنُونَ

wamā huwa biqawli shāʿirin qalīlan mā tu'minūna

Kuma shi ba maganar wani mawãƙi ba ne. Kaɗan ƙwarai zã ku gaskata.

42

وَلَا بِقَوْلِ كَاهِنٍۢ ۚ قَلِيلًۭا مَّا تَذَكَّرُونَ

walā biqawli kāhinin qalīlan mā tadhakkarūna

Kuma bã maganar bõka ba ne. Kaɗan ƙwarai zã ku iya tunãwa.

43

تَنزِيلٌۭ مِّن رَّبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ

tanzīlun min rabbi l-ʿālamīna

Abin saukarwã ne daga Ubangijin halitta duka.

44

وَلَوْ تَقَوَّلَ عَلَيْنَا بَعْضَ ٱلْأَقَاوِيلِ

walaw taqawwala ʿalaynā baʿḍa l-aqāwīli

Kuma dã (Muhammadu) yã faɗi wata maganã, yã jingina ta garẽ Mu.

45

لَأَخَذْنَا مِنْهُ بِٱلْيَمِينِ

la-akhadhnā min'hu bil-yamīni

Dã Mun kãma shi da dãma.

46

ثُمَّ لَقَطَعْنَا مِنْهُ ٱلْوَتِينَ

thumma laqaṭaʿnā min'hu l-watīna

sa'an nan, lalle ne, dã Mun kãtse masa lakã.

47

فَمَا مِنكُم مِّنْ أَحَدٍ عَنْهُ حَـٰجِزِينَ

famā minkum min aḥadin ʿanhu ḥājizīna

Kuma daga cikinku bãbu wasu mãsu iya kãre (azãbar Mu) daga gare shi.

48

وَإِنَّهُۥ لَتَذْكِرَةٌۭ لِّلْمُتَّقِينَ

wa-innahu latadhkiratun lil'muttaqīna

Kuma lalle ne shi (Alƙur'ãni) tanãtarwa ce ga mãsu taƙawa.

49

وَإِنَّا لَنَعْلَمُ أَنَّ مِنكُم مُّكَذِّبِينَ

wa-innā lanaʿlamu anna minkum mukadhibīna

Kuma lalle, ne Mũ, wallahi Munã sane da cẽwa daga cikinku alwwai mãsu ƙaryatãwa.

50

وَإِنَّهُۥ لَحَسْرَةٌ عَلَى ٱلْكَـٰفِرِينَ

wa-innahu laḥasratun ʿalā l-kāfirīna

Kuma lalle ne shi (Alƙarãni) wallahi baƙin ciki ne ga kãfirai.

51

وَإِنَّهُۥ لَحَقُّ ٱلْيَقِينِ

wa-innahu laḥaqqu l-yaqīni

Kuma lalle, ne shi gaskiya ce ta yaƙini.

52

فَسَبِّحْ بِٱسْمِ رَبِّكَ ٱلْعَظِيمِ

fasabbiḥ bi-is'mi rabbika l-ʿaẓīmi

Sabõda haka, ka tsarkake sũnan Ubangjinka, mai girma.

Game da Wannan Sura