70

المعارج

Al-Ma'arij

The Ascending Stairways

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ Da sunan Allah Mai rahama Mai jin kai
Ayoyi 44
Juzu'i 29
Shafi 568-570
Nau'i Makkiya
Tsarin Saukarwa 79
0:00 / 0:00
Aya: 1 / 44
1

سَأَلَ سَآئِلٌۢ بِعَذَابٍۢ وَاقِعٍۢ

sa-ala sāilun biʿadhābin wāqiʿin

Wani mai tambaya yã yi tambaya game da azãba, mai aukuwa.

2

لِّلْكَـٰفِرِينَ لَيْسَ لَهُۥ دَافِعٌۭ

lil'kāfirīna laysa lahu dāfiʿun

Ga kãfirai, bã ta da mai tunkuɗẽwa.

3

مِّنَ ٱللَّهِ ذِى ٱلْمَعَارِجِ

mina l-lahi dhī l-maʿāriji

Daga Allah Mai matãkala.

4

تَعْرُجُ ٱلْمَلَـٰٓئِكَةُ وَٱلرُّوحُ إِلَيْهِ فِى يَوْمٍۢ كَانَ مِقْدَارُهُۥ خَمْسِينَ أَلْفَ سَنَةٍۢ

taʿruju l-malāikatu wal-rūḥu ilayhi fī yawmin kāna miq'dāruhu khamsīna alfa sanatin

Malã'iku da Ruhi (Jibrila) sunã tãkãwa zuwa gare Shi, a cikin yini wanda gwargwadonsa, shẽkara dubu hamsin ne.

5

فَٱصْبِرْ صَبْرًۭا جَمِيلًا

fa-iṣ'bir ṣabran jamīlan

Sabõda haka, ka yi haƙuri, haƙuri mai kyãwo.

6

إِنَّهُمْ يَرَوْنَهُۥ بَعِيدًۭا

innahum yarawnahu baʿīdan

Lalle ne su, sunã ganin ta mai nĩsa.

7

وَنَرَىٰهُ قَرِيبًۭا

wanarāhu qarīban

Kuma Mu, Muna ganin ta a kusa.

8

يَوْمَ تَكُونُ ٱلسَّمَآءُ كَٱلْمُهْلِ

yawma takūnu l-samāu kal-muh'li

Rãnar da sama zã ta kasance kamar narkakkar azurfa.

9

وَتَكُونُ ٱلْجِبَالُ كَٱلْعِهْنِ

watakūnu l-jibālu kal-ʿih'ni

Kuma duwãtsu su zama kamar saɓin sũfi.

10

وَلَا يَسْـَٔلُ حَمِيمٌ حَمِيمًۭا

walā yasalu ḥamīmun ḥamīman

Kuma abõki bã ya tambayar inda wani abõki yake.

11

يُبَصَّرُونَهُمْ ۚ يَوَدُّ ٱلْمُجْرِمُ لَوْ يَفْتَدِى مِنْ عَذَابِ يَوْمِئِذٍۭ بِبَنِيهِ

yubaṣṣarūnahum yawaddu l-muj'rimu law yaftadī min ʿadhābi yawmi-idhin bibanīhi

Ana sanya su, su gajũna, mai laifi na gũrin dã zai iya yin fansa, daga azãbar rãnar nan, da ɗiyansa,

12

وَصَـٰحِبَتِهِۦ وَأَخِيهِ

waṣāḥibatihi wa-akhīhi

Da matarsa da ɗan'uwansa.

13

وَفَصِيلَتِهِ ٱلَّتِى تُـْٔوِيهِ

wafaṣīlatihi allatī tu'wīhi

Da danginsa, mãsu tattarã shi.

14

وَمَن فِى ٱلْأَرْضِ جَمِيعًۭا ثُمَّ يُنجِيهِ

waman fī l-arḍi jamīʿan thumma yunjīhi

Da wanda ke a cikin dũniya duka gabã ɗaya, sa'an nan fansar, ta tsĩrar da shi.

15

كَلَّآ ۖ إِنَّهَا لَظَىٰ

kallā innahā laẓā

A'aha! Lalle ne fa, ita ce Lazã,

16

نَزَّاعَةًۭ لِّلشَّوَىٰ

nazzāʿatan lilshawā

Mai twãle fãtar goshi.

17

تَدْعُوا۟ مَنْ أَدْبَرَ وَتَوَلَّىٰ

tadʿū man adbara watawallā

Tanã kiran wanda ya jũya bãya (daga addini) kuma ya kau da kai.

18

وَجَمَعَ فَأَوْعَىٰٓ

wajamaʿa fa-awʿā

Ya tãra (dũkiya), kuma ya sanya ta a cikin jaka.

19

۞ إِنَّ ٱلْإِنسَـٰنَ خُلِقَ هَلُوعًا

inna l-insāna khuliqa halūʿan

Lalle ne mutum an halitta shi mai ciwon kwaɗayi.

20

إِذَا مَسَّهُ ٱلشَّرُّ جَزُوعًۭا

idhā massahu l-sharu jazūʿan

Idan sharri ya shãfe shi, ya kãsa haƙuri.

21

وَإِذَا مَسَّهُ ٱلْخَيْرُ مَنُوعًا

wa-idhā massahu l-khayru manūʿan

Kuma idan alhẽri ya shãfe shi, ya yi rõwa.

22

إِلَّا ٱلْمُصَلِّينَ

illā l-muṣalīna

Sai mãsu yin salla,

23

ٱلَّذِينَ هُمْ عَلَىٰ صَلَاتِهِمْ دَآئِمُونَ

alladhīna hum ʿalā ṣalātihim dāimūna

Waɗanda suke, a kan sallarsu, su, mãsu dawwama ne.

24

وَٱلَّذِينَ فِىٓ أَمْوَٰلِهِمْ حَقٌّۭ مَّعْلُومٌۭ

wa-alladhīna fī amwālihim ḥaqqun maʿlūmun

Kuma waɗanda a cikin dũkiyarsu, akwai wani haƙƙi sananne.

25

لِّلسَّآئِلِ وَٱلْمَحْرُومِ

lilssāili wal-maḥrūmi

Ga (matalauci) mai rõƙo da wanda aka hanã wa roƙon.

26

وَٱلَّذِينَ يُصَدِّقُونَ بِيَوْمِ ٱلدِّينِ

wa-alladhīna yuṣaddiqūna biyawmi l-dīni

Da waɗannan da ke gaskata rãnar sakamako.

27

وَٱلَّذِينَ هُم مِّنْ عَذَابِ رَبِّهِم مُّشْفِقُونَ

wa-alladhīna hum min ʿadhābi rabbihim mush'fiqūna

Da waɗannan sabõda azãbar Ubangijinsu, suna jin tsõro.

28

إِنَّ عَذَابَ رَبِّهِمْ غَيْرُ مَأْمُونٍۢ

inna ʿadhāba rabbihim ghayru mamūnin

Lalle ne, azãbar Ubangijinsu bã wadda ake iya amincẽwaba ce.

29

وَٱلَّذِينَ هُمْ لِفُرُوجِهِمْ حَـٰفِظُونَ

wa-alladhīna hum lifurūjihim ḥāfiẓūna

Da waɗanda suke, ga farjojinsu, mãsu tsarewa ne.

30

إِلَّا عَلَىٰٓ أَزْوَٰجِهِمْ أَوْ مَا مَلَكَتْ أَيْمَـٰنُهُمْ فَإِنَّهُمْ غَيْرُ مَلُومِينَ

illā ʿalā azwājihim aw mā malakat aymānuhum fa-innahum ghayru malūmīna

Sai fa a kan matan aurensu da abin da hannayensu na dãma suka mallaka. To lalle ne sũkam ba waɗanda ake zargi ba ne.

31

فَمَنِ ٱبْتَغَىٰ وَرَآءَ ذَٰلِكَ فَأُو۟لَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلْعَادُونَ

famani ib'taghā warāa dhālika fa-ulāika humu l-ʿādūna

To, duk wanda ya nẽmi abin da yake a bayan wannan, to, waɗancan sũ ne mãsu ƙetare iyãka.

32

وَٱلَّذِينَ هُمْ لِأَمَـٰنَـٰتِهِمْ وَعَهْدِهِمْ رَٰعُونَ

wa-alladhīna hum li-amānātihim waʿahdihim rāʿūna

Kuma da waɗannan da suke ga amãnõninsu da alkawarinsu mãsu tsarẽwa ne.

33

وَٱلَّذِينَ هُم بِشَهَـٰدَٰتِهِمْ قَآئِمُونَ

wa-alladhīna hum bishahādātihim qāimūna

Kuma da waɗanda suke, ga shaidarsu, mãsu dãgẽwa ne.

34

وَٱلَّذِينَ هُمْ عَلَىٰ صَلَاتِهِمْ يُحَافِظُونَ

wa-alladhīna hum ʿalā ṣalātihim yuḥāfiẓūna

Kuma waɗanda suke, a kan sallarsu, mãsu tsarẽwa ne.

35

أُو۟لَـٰٓئِكَ فِى جَنَّـٰتٍۢ مُّكْرَمُونَ

ulāika fī jannātin muk'ramūna

Waɗannan, a cikin gidãjen Aljanna, waɗanda ake girmamãwa ne

36

فَمَالِ ٱلَّذِينَ كَفَرُوا۟ قِبَلَكَ مُهْطِعِينَ

famāli alladhīna kafarū qibalaka muh'ṭiʿīna

Mẽ yã sãmi waɗanda suka kãfirta, a wajenka, sunã gaugãwar (gudu).

37

عَنِ ٱلْيَمِينِ وَعَنِ ٱلشِّمَالِ عِزِينَ

ʿani l-yamīni waʿani l-shimāli ʿizīna

Daga jihar dãma, kuma daga jihar hagu, jama'a-jama'a!

38

أَيَطْمَعُ كُلُّ ٱمْرِئٍۢ مِّنْهُمْ أَن يُدْخَلَ جَنَّةَ نَعِيمٍۢ

ayaṭmaʿu kullu im'ri-in min'hum an yud'khala jannata naʿīmin

Shin kõwane mutum daga cikinsu yana nẽman a shigar da shi a Aljannar ni'ima ne (ba da wani aiki ba)?

39

كَلَّآ ۖ إِنَّا خَلَقْنَـٰهُم مِّمَّا يَعْلَمُونَ

kallā innā khalaqnāhum mimmā yaʿlamūna

A'aha! Lalle Mũ, Mun halitta su, daga abin da suka sani.

40

فَلَآ أُقْسِمُ بِرَبِّ ٱلْمَشَـٰرِقِ وَٱلْمَغَـٰرِبِ إِنَّا لَقَـٰدِرُونَ

falā uq'simu birabbi l-mashāriqi wal-maghāribi innā laqādirūna

Sabõda haka ba sai Na yi rantsuwa da Ubangijin wurãren ɓullõwar rãna da wurãren fãɗuwarta ba, lalle Mũ, Mãsu iyãwa ne.

41

عَلَىٰٓ أَن نُّبَدِّلَ خَيْرًۭا مِّنْهُمْ وَمَا نَحْنُ بِمَسْبُوقِينَ

ʿalā an nubaddila khayran min'hum wamā naḥnu bimasbūqīna

Ga Mu musanya waɗanda suke mafi alhẽri, daga gare su. Kuma ba Mu kasance waɗanda ake rinjãya ba.

42

فَذَرْهُمْ يَخُوضُوا۟ وَيَلْعَبُوا۟ حَتَّىٰ يُلَـٰقُوا۟ يَوْمَهُمُ ٱلَّذِى يُوعَدُونَ

fadharhum yakhūḍū wayalʿabū ḥattā yulāqū yawmahumu alladhī yūʿadūna

Sabõda haka ka bar su, su dulmuya, kuma su yi wãsã, har su haɗu da rãnarsu wadda ake yi musu alkawari (da ita).

43

يَوْمَ يَخْرُجُونَ مِنَ ٱلْأَجْدَاثِ سِرَاعًۭا كَأَنَّهُمْ إِلَىٰ نُصُبٍۢ يُوفِضُونَ

yawma yakhrujūna mina l-ajdāthi sirāʿan ka-annahum ilā nuṣubin yūfiḍūna

Rãnar da suke fitowa daga kaburbura da gaugãwa, kamar sũ, zuwa ga wata kafaffiyar (tuta), suke yin gaugãwa.

44

خَـٰشِعَةً أَبْصَـٰرُهُمْ تَرْهَقُهُمْ ذِلَّةٌۭ ۚ ذَٰلِكَ ٱلْيَوْمُ ٱلَّذِى كَانُوا۟ يُوعَدُونَ

khāshiʿatan abṣāruhum tarhaquhum dhillatun dhālika l-yawmu alladhī kānū yūʿadūna

Maƙaskanta ga idanunsu, wani walakanci yana rufe su. wannan shi ne yinin da suka kasance ana yi musa alkawari (a kansa.)

Game da Wannan Sura