68

القلم

Al-Qalam

The Pen

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ Da sunan Allah Mai rahama Mai jin kai
Ayoyi 52
Juzu'i 29
Shafi 564-566
Nau'i Makkiya
Tsarin Saukarwa 2
0:00 / 0:00
Aya: 1 / 52
1

نٓ ۚ وَٱلْقَلَمِ وَمَا يَسْطُرُونَ

noon wal-qalami wamā yasṭurūna

Ñ. Na rantse da alƙalami da abin da (marubũta) suke rubũtãwa.

2

مَآ أَنتَ بِنِعْمَةِ رَبِّكَ بِمَجْنُونٍۢ

mā anta biniʿ'mati rabbika bimajnūnin

Kai, sabõda ni'imar Ubangijinka, bã mahaukaci kake ba.

3

وَإِنَّ لَكَ لَأَجْرًا غَيْرَ مَمْنُونٍۢ

wa-inna laka la-ajran ghayra mamnūnin

Kuma, lalle, haƙĩƙa kanã da lãdar da bã ta yankewa.

4

وَإِنَّكَ لَعَلَىٰ خُلُقٍ عَظِيمٍۢ

wa-innaka laʿalā khuluqin ʿaẓīmin

Kuma, lalle haƙiƙa kana a kan hãlãyen kirki, manya.

5

فَسَتُبْصِرُ وَيُبْصِرُونَ

fasatub'ṣiru wayub'ṣirūna

Don haka, zã ka gani, sũ kuma zã su gani.

6

بِأَييِّكُمُ ٱلْمَفْتُونُ

bi-ayyikumu l-maftūnu

Ga wanenku haukã take.

7

إِنَّ رَبَّكَ هُوَ أَعْلَمُ بِمَن ضَلَّ عَن سَبِيلِهِۦ وَهُوَ أَعْلَمُ بِٱلْمُهْتَدِينَ

inna rabbaka huwa aʿlamu biman ḍalla ʿan sabīlihi wahuwa aʿlamu bil-muh'tadīna

Lalle Ubangijinka Shi ne Mafi sani ga wanda ya ɓace daga tafarkin Sa. Kuma Shi ne Mafi sani ga mãsu shiryuwa.

8

فَلَا تُطِعِ ٱلْمُكَذِّبِينَ

falā tuṭiʿi l-mukadhibīna

Saboda haka kada ka bi mãsu ƙaryatãwa.

9

وَدُّوا۟ لَوْ تُدْهِنُ فَيُدْهِنُونَ

waddū law tud'hinu fayud'hinūna

Sunã fatar ka sassauta, su kuma sũ sassauta.

10

وَلَا تُطِعْ كُلَّ حَلَّافٍۢ مَّهِينٍ

walā tuṭiʿ kulla ḥallāfin mahīnin

Kada ka bi dukkan mai yawan rantsuwa, walãkantacce.

11

هَمَّازٍۢ مَّشَّآءٍۭ بِنَمِيمٍۢ

hammāzin mashāin binamīmin

Mai zunɗe, mai yãwo da gulma.

12

مَّنَّاعٍۢ لِّلْخَيْرِ مُعْتَدٍ أَثِيمٍ

mannāʿin lil'khayri muʿ'tadin athīmin

Mai hana alhẽri mai zãlunci, mai zunubi.

13

عُتُلٍّۭ بَعْدَ ذَٰلِكَ زَنِيمٍ

ʿutullin baʿda dhālika zanīmin

Mai girman kai, bãyan haka kuma la'ĩmi (bã ya son alhẽri).

14

أَن كَانَ ذَا مَالٍۢ وَبَنِينَ

an kāna dhā mālin wabanīna

Sabõda yã kasance mai dũkiya da ɗiya.

15

إِذَا تُتْلَىٰ عَلَيْهِ ءَايَـٰتُنَا قَالَ أَسَـٰطِيرُ ٱلْأَوَّلِينَ

idhā tut'lā ʿalayhi āyātunā qāla asāṭīru l-awalīna

Idan ana karanta masa ãyõyin Mu, sai ya ce: "Tatsũniyõyin mutãnen farko ne."

16

سَنَسِمُهُۥ عَلَى ٱلْخُرْطُومِ

sanasimuhu ʿalā l-khur'ṭūmi

Zã Mu yi masa alãma a kan hanci.

17

إِنَّا بَلَوْنَـٰهُمْ كَمَا بَلَوْنَآ أَصْحَـٰبَ ٱلْجَنَّةِ إِذْ أَقْسَمُوا۟ لَيَصْرِمُنَّهَا مُصْبِحِينَ

innā balawnāhum kamā balawnā aṣḥāba l-janati idh aqsamū layaṣrimunnahā muṣ'biḥīna

Lalle Mun jarrabe su kamar yadda Muka jarrabi mãsu gonar lambu, a lokacin da suka yi rantsuwa, wai lalle zã su girbe amfãninta, suna mãsu asubanci.

18

وَلَا يَسْتَثْنُونَ

walā yastathnūna

Kuma (suka yi niyya), bã su kõ tõgẽwa.

19

فَطَافَ عَلَيْهَا طَآئِفٌۭ مِّن رَّبِّكَ وَهُمْ نَآئِمُونَ

faṭāfa ʿalayhā ṭāifun min rabbika wahum nāimūna

Wani mai kẽwayãwa daga Ubangijinka ya kẽwayã a kanta, (ya ƙone ta,) alhãli sunã barci.

20

فَأَصْبَحَتْ كَٱلصَّرِيمِ

fa-aṣbaḥat kal-ṣarīmi

Sai ta wãyi gari (baƙa ƙirin) kamar dare.

21

فَتَنَادَوْا۟ مُصْبِحِينَ

fatanādaw muṣ'biḥīna

Sai suka kirãyi jũna, sunã mãsu yin asubanci.

22

أَنِ ٱغْدُوا۟ عَلَىٰ حَرْثِكُمْ إِن كُنتُمْ صَـٰرِمِينَ

ani igh'dū ʿalā ḥarthikum in kuntum ṣārimīna

Cẽwa ku yi sammakõ ga amfãnin gõnarku, idan kun kasance mãsu girbewa.

23

فَٱنطَلَقُوا۟ وَهُمْ يَتَخَـٰفَتُونَ

fa-inṭalaqū wahum yatakhāfatūna

Sai suka tafi sunã shãwara a ɓõye (sunã cẽwa).

24

أَن لَّا يَدْخُلَنَّهَا ٱلْيَوْمَ عَلَيْكُم مِّسْكِينٌۭ

an lā yadkhulannahā l-yawma ʿalaykum mis'kīnun

"Lalle kada wani miskĩni ya shigar muku ita a yau!"

25

وَغَدَوْا۟ عَلَىٰ حَرْدٍۢ قَـٰدِرِينَ

waghadaw ʿalā ḥardin qādirīna

Kuma suka yi sammako akan (niyyar) rõwa, matuƙar iyãwarsu.

26

فَلَمَّا رَأَوْهَا قَالُوٓا۟ إِنَّا لَضَآلُّونَ

falammā ra-awhā qālū innā laḍāllūna

Lõkacin da suka gan ta, sai suka ce: "Lalle, mun saki hanya (mun ɓace)!"

27

بَلْ نَحْنُ مَحْرُومُونَ

bal naḥnu maḥrūmūna

"Ba haka ba, mũ dai, an hana mu ne."

28

قَالَ أَوْسَطُهُمْ أَلَمْ أَقُل لَّكُمْ لَوْلَا تُسَبِّحُونَ

qāla awsaṭuhum alam aqul lakum lawlā tusabbiḥūna

Mafificinsu (hankali) ya ce: "Ban gaya muku ba, yã kamata ku tsarkake Allah?"

29

قَالُوا۟ سُبْحَـٰنَ رَبِّنَآ إِنَّا كُنَّا ظَـٰلِمِينَ

qālū sub'ḥāna rabbinā innā kunnā ẓālimīna

Suka ce: "Tsarki ya tabbata ga Ubangijinmu! Lalle, mu mun kasance azzãlumai."

30

فَأَقْبَلَ بَعْضُهُمْ عَلَىٰ بَعْضٍۢ يَتَلَـٰوَمُونَ

fa-aqbala baʿḍuhum ʿalā baʿḍin yatalāwamūna

Sai suka fuskanci jũna, sunã zargin kansu.

31

قَالُوا۟ يَـٰوَيْلَنَآ إِنَّا كُنَّا طَـٰغِينَ

qālū yāwaylanā innā kunnā ṭāghīna

Suka ce: "Kaitonmu! Lalle, mũ ne muka kasance mãsu ƙẽtare iyãka."

32

عَسَىٰ رَبُّنَآ أَن يُبْدِلَنَا خَيْرًۭا مِّنْهَآ إِنَّآ إِلَىٰ رَبِّنَا رَٰغِبُونَ

ʿasā rabbunā an yub'dilanā khayran min'hā innā ilā rabbinā rāghibūna

"Mai yiwuwa ne Ubangijinmu Ya musanya mana da wani abu da yã fi ta. Lalle, mũ (ba mu yanke ƙauna ba) zuwa ga Ubangijinmu, mãsu kwaɗayi ne."

33

كَذَٰلِكَ ٱلْعَذَابُ ۖ وَلَعَذَابُ ٱلْـَٔاخِرَةِ أَكْبَرُ ۚ لَوْ كَانُوا۟ يَعْلَمُونَ

kadhālika l-ʿadhābu walaʿadhābu l-ākhirati akbaru law kānū yaʿlamūna

Haka dai azãbar1 take, kuma lalle ne azãbar Lãhira ta fi girma, in da sun kasance zã su iya gãnẽwã.

34

إِنَّ لِلْمُتَّقِينَ عِندَ رَبِّهِمْ جَنَّـٰتِ ٱلنَّعِيمِ

inna lil'muttaqīna ʿinda rabbihim jannāti l-naʿīmi

Lalle ne mãsu taƙawa nã da a wurin Ubangijinsu, gidãjen Aljanna na ni'ima.

35

أَفَنَجْعَلُ ٱلْمُسْلِمِينَ كَٱلْمُجْرِمِينَ

afanajʿalu l-mus'limīna kal-muj'rimīna

Shin ko zã Mu sanya waɗanda ke bi da ɗa'a kamar mãsu laifi?

36

مَا لَكُمْ كَيْفَ تَحْكُمُونَ

mā lakum kayfa taḥkumūna

Me ya sãme ku, yãya kuke yin hukunci (da haka)?

37

أَمْ لَكُمْ كِتَـٰبٌۭ فِيهِ تَدْرُسُونَ

am lakum kitābun fīhi tadrusūna

Ko kuna da wani littafi, wanda a cikinsa, kuke karantãwa?

38

إِنَّ لَكُمْ فِيهِ لَمَا تَخَيَّرُونَ

inna lakum fīhi lamā takhayyarūna

Cẽwã kunã da, a cikinsa lalle (duk) abin da rãyukanku suka zãɓa?

39

أَمْ لَكُمْ أَيْمَـٰنٌ عَلَيْنَا بَـٰلِغَةٌ إِلَىٰ يَوْمِ ٱلْقِيَـٰمَةِ ۙ إِنَّ لَكُمْ لَمَا تَحْكُمُونَ

am lakum aymānun ʿalaynā bālighatun ilā yawmi l-qiyāmati inna lakum lamā taḥkumūna

Kõ kunã (riƙe) da wasu rantsuwõyin alkawari a kan Mu, har ya zuwa Rãnar ¡iyãma, cẽwa lalle ne kunã da abin da kuke hukuntã wa kanku?

40

سَلْهُمْ أَيُّهُم بِذَٰلِكَ زَعِيمٌ

salhum ayyuhum bidhālika zaʿīmun

Ka tambaye su, wãne, a cikinsu, ke lãmuncewã ga sãmun wannan (hukuncin)?

41

أَمْ لَهُمْ شُرَكَآءُ فَلْيَأْتُوا۟ بِشُرَكَآئِهِمْ إِن كَانُوا۟ صَـٰدِقِينَ

am lahum shurakāu falyatū bishurakāihim in kānū ṣādiqīna

Kõ sunã da abõkan tãrẽwa (ga wannan ra'ayi)? To, sai su kãwo abõkan tãrayyarsu, idan sun kasance mãsu gaskiya.

42

يَوْمَ يُكْشَفُ عَن سَاقٍۢ وَيُدْعَوْنَ إِلَى ٱلسُّجُودِ فَلَا يَسْتَطِيعُونَ

yawma yuk'shafu ʿan sāqin wayud'ʿawna ilā l-sujūdi falā yastaṭīʿūna

Ranar da zã a kuranye ƙwabri, kuma a kira su zuwa ga yin sujada, sai bã zã su iyãwa ba.

43

خَـٰشِعَةً أَبْصَـٰرُهُمْ تَرْهَقُهُمْ ذِلَّةٌۭ ۖ وَقَدْ كَانُوا۟ يُدْعَوْنَ إِلَى ٱلسُّجُودِ وَهُمْ سَـٰلِمُونَ

khāshiʿatan abṣāruhum tarhaquhum dhillatun waqad kānū yud'ʿawna ilā l-sujūdi wahum sālimūna

Su fito da idãnu ƙasƙantattu, wulãkanci yana rufe su. Lalle ne a dã sun kasance anã kiran su zuwa, yin sujũdar, alhãli kuwa sunã lãfiya lau, (suka ƙi yi).

44

فَذَرْنِى وَمَن يُكَذِّبُ بِهَـٰذَا ٱلْحَدِيثِ ۖ سَنَسْتَدْرِجُهُم مِّنْ حَيْثُ لَا يَعْلَمُونَ

fadharnī waman yukadhibu bihādhā l-ḥadīthi sanastadrijuhum min ḥaythu lā yaʿlamūna

Sabõda haka ka bar Ni da mai ƙaryata wanna lãbãri (Alƙur'ãni). Zã Mu yi musu istidrãji daga inda ba su sani ba.

45

وَأُمْلِى لَهُمْ ۚ إِنَّ كَيْدِى مَتِينٌ

wa-um'lī lahum inna kaydī matīnun

Ina jinkirtã musu, lalle kaidi Na mai ƙarfi ne.

46

أَمْ تَسْـَٔلُهُمْ أَجْرًۭا فَهُم مِّن مَّغْرَمٍۢ مُّثْقَلُونَ

am tasaluhum ajran fahum min maghramin muth'qalūna

Kõ kana tambayar su wata la'ada ne, sabõda haka sũ, daga wannan tãrar, suke jin an nauyaya musu?

47

أَمْ عِندَهُمُ ٱلْغَيْبُ فَهُمْ يَكْتُبُونَ

am ʿindahumu l-ghaybu fahum yaktubūna

Ko kuma sunã da ilmin gaibu ne, wãto sunã yin rubũtun (abin da suke faɗã daga gare shi) ne?

48

فَٱصْبِرْ لِحُكْمِ رَبِّكَ وَلَا تَكُن كَصَاحِبِ ٱلْحُوتِ إِذْ نَادَىٰ وَهُوَ مَكْظُومٌۭ

fa-iṣ'bir liḥuk'mi rabbika walā takun kaṣāḥibi l-ḥūti idh nādā wahuwa makẓūmun

Sabõda haka, ka yi haƙuri da hukuncin Ubangijinka, kada ka zama kamar Ma'abũcin kĩfi, alõkacin da ya yi kira, alhãli yana cike da hushi.

49

لَّوْلَآ أَن تَدَٰرَكَهُۥ نِعْمَةٌۭ مِّن رَّبِّهِۦ لَنُبِذَ بِٱلْعَرَآءِ وَهُوَ مَذْمُومٌۭ

lawlā an tadārakahu niʿ'matun min rabbihi lanubidha bil-ʿarāi wahuwa madhmūmun

Ba dõmin ni'ima daga wajen Ubangijinsa tã riske shi ba, lalle ne da an jẽfa shi a cikin wõfintacciyar ƙasa, alhãli yanã abin zargi.

50

فَٱجْتَبَـٰهُ رَبُّهُۥ فَجَعَلَهُۥ مِنَ ٱلصَّـٰلِحِينَ

fa-ij'tabāhu rabbuhu fajaʿalahu mina l-ṣāliḥīna

Sai Ubangijinsa Ya zãɓe shi, sa'an nan Ya sanya shi a cikin mutãnen kirki.

51

وَإِن يَكَادُ ٱلَّذِينَ كَفَرُوا۟ لَيُزْلِقُونَكَ بِأَبْصَـٰرِهِمْ لَمَّا سَمِعُوا۟ ٱلذِّكْرَ وَيَقُولُونَ إِنَّهُۥ لَمَجْنُونٌۭ

wa-in yakādu alladhīna kafarū layuz'liqūnaka bi-abṣārihim lammā samiʿū l-dhik'ra wayaqūlūna innahu lamajnūnun

Kuma lalle, ne waɗanda suka kãfirta sunã yin kamar su kãyar da kai sabõ da kallonsu (kallon mãmãki), a lokacin da suke jin karãtun Alƙur'ãni, kuma sunã cẽwa, "Lalle ne shi mahaukaci ne!"

52

وَمَا هُوَ إِلَّا ذِكْرٌۭ لِّلْعَـٰلَمِينَ

wamā huwa illā dhik'run lil'ʿālamīna

Shi (Alƙur'ãni) bai kasance ba, fãce abin tunãtarwa ne ga duka dũniya.

Game da Wannan Sura