89

الفجر

Al-Fajr

The Dawn

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ Da sunan Allah Mai rahama Mai jin kai
Ayoyi 30
Juzu'i 30
Shafi 593-594
Nau'i Makkiya
Tsarin Saukarwa 10
0:00 / 0:00
Aya: 1 / 30
1

وَٱلْفَجْرِ

wal-fajri

Inã rantsuwa da alfijiri.

2

وَلَيَالٍ عَشْرٍۢ

walayālin ʿashrin

Da darũruwa gõma.

3

وَٱلشَّفْعِ وَٱلْوَتْرِ

wal-shafʿi wal-watri

Da (adadi na) cikã da (na) mãrã.

4

وَٱلَّيْلِ إِذَا يَسْرِ

wa-al-layli idhā yasri

Da dare idan yana shũɗewa.

5

هَلْ فِى ذَٰلِكَ قَسَمٌۭ لِّذِى حِجْرٍ

hal fī dhālika qasamun lidhī ḥij'rin

Ko a cikin waɗannan akwai abin rantsuwa ga mai hankali (da yake kange shi daga zunubi)?

6

أَلَمْ تَرَ كَيْفَ فَعَلَ رَبُّكَ بِعَادٍ

alam tara kayfa faʿala rabbuka biʿādin

Ba ka ga yadda Ubangijinka Ya aikata da Ãdãwa ba?

7

إِرَمَ ذَاتِ ٱلْعِمَادِ

irama dhāti l-ʿimādi

Iramawa mãsu sakon1 ƙĩrar jiki.

8

ٱلَّتِى لَمْ يُخْلَقْ مِثْلُهَا فِى ٱلْبِلَـٰدِ

allatī lam yukh'laq mith'luhā fī l-bilādi

Waɗanda ba a halitta kwatankwacinsu ba a cikin garũruwa (na dũniya).

9

وَثَمُودَ ٱلَّذِينَ جَابُوا۟ ٱلصَّخْرَ بِٱلْوَادِ

wathamūda alladhīna jābū l-ṣakhra bil-wādi

Da samũdãwa waɗanda suka fasa duwãtsu a cikin Wadi1 suka yi gidãje)?

10

وَفِرْعَوْنَ ذِى ٱلْأَوْتَادِ

wafir'ʿawna dhī l-awtādi

Da Fir'auna mai turãku.

11

ٱلَّذِينَ طَغَوْا۟ فِى ٱلْبِلَـٰدِ

alladhīna ṭaghaw fī l-bilādi

Waɗanda suka ƙẽtare iyãkarsu, a cikin garũruwa?

12

فَأَكْثَرُوا۟ فِيهَا ٱلْفَسَادَ

fa-aktharū fīhā l-fasāda

Sabõda haka, suka yawaita yin ɓarna a cikinsu.

13

فَصَبَّ عَلَيْهِمْ رَبُّكَ سَوْطَ عَذَابٍ

faṣabba ʿalayhim rabbuka sawṭa ʿadhābin

Sabõda haka Ubangijinka Ya zuba musu bũlãlar azãba.

14

إِنَّ رَبَّكَ لَبِٱلْمِرْصَادِ

inna rabbaka labil-mir'ṣādi

Lalle ne, Ubangijinka Yana nan a mafaka.

15

فَأَمَّا ٱلْإِنسَـٰنُ إِذَا مَا ٱبْتَلَىٰهُ رَبُّهُۥ فَأَكْرَمَهُۥ وَنَعَّمَهُۥ فَيَقُولُ رَبِّىٓ أَكْرَمَنِ

fa-ammā l-insānu idhā mā ib'talāhu rabbuhu fa-akramahu wanaʿʿamahu fayaqūlu rabbī akramani

To, amma fa mutum idan Ubangijibsa Ya jarraba shi, wãto Yã girmama shi kuma Ya yi masa ni'ima, sai ya ce: "Ubangijina Ya girmama ni."

16

وَأَمَّآ إِذَا مَا ٱبْتَلَىٰهُ فَقَدَرَ عَلَيْهِ رِزْقَهُۥ فَيَقُولُ رَبِّىٓ أَهَـٰنَنِ

wa-ammā idhā mā ib'talāhu faqadara ʿalayhi riz'qahu fayaqūlu rabbī ahānani

Kuma idan Ya jarraba shi, wãto Ya ƙuntata masa abincinsa, sai ya ce: "Ubangijina Ya walãkanta ni."

17

كَلَّا ۖ بَل لَّا تُكْرِمُونَ ٱلْيَتِيمَ

kallā bal lā tuk'rimūna l-yatīma

A'aha! Bari wannan, ai bã ku girmama marãya!

18

وَلَا تَحَـٰٓضُّونَ عَلَىٰ طَعَامِ ٱلْمِسْكِينِ

walā taḥāḍḍūna ʿalā ṭaʿāmi l-mis'kīni

Bã ku kwaɗaitã wa jũnanku ga (tattalin) abincin matalauci!

19

وَتَأْكُلُونَ ٱلتُّرَاثَ أَكْلًۭا لَّمًّۭا

watakulūna l-turātha aklan lamman

Kuma kuna cin dũkiyar gãdo, ci na tãrãwa.

20

وَتُحِبُّونَ ٱلْمَالَ حُبًّۭا جَمًّۭا

watuḥibbūna l-māla ḥubban jamman

Kuma kuna son dũkiya, so mai yawa.

21

كَلَّآ إِذَا دُكَّتِ ٱلْأَرْضُ دَكًّۭا دَكًّۭا

kallā idhā dukkati l-arḍu dakkan dakkan

A'aha! Idan aka niƙa ƙasa niƙewa sosai.

22

وَجَآءَ رَبُّكَ وَٱلْمَلَكُ صَفًّۭا صَفًّۭا

wajāa rabbuka wal-malaku ṣaffan ṣaffan

Kuma Ubangijinka Ya zo, alhãli malã'iku na jẽre, sahu- sahu.

23

وَجِا۟ىٓءَ يَوْمَئِذٍۭ بِجَهَنَّمَ ۚ يَوْمَئِذٍۢ يَتَذَكَّرُ ٱلْإِنسَـٰنُ وَأَنَّىٰ لَهُ ٱلذِّكْرَىٰ

wajīa yawma-idhin bijahannama yawma-idhin yatadhakkaru l-insānu wa-annā lahu l-dhik'rā

Kuma a ranar nan aka zo da Jahannama. A ranar nan mutum zai yi tunãni. To, inã fa tunãni yake a gare shi!

24

يَقُولُ يَـٰلَيْتَنِى قَدَّمْتُ لِحَيَاتِى

yaqūlu yālaytanī qaddamtu liḥayātī

Yana dinga cẽwa, "Kaitona, dã na gabatar (da aikin ƙwarai) domin rãyuwata!"

25

فَيَوْمَئِذٍۢ لَّا يُعَذِّبُ عَذَابَهُۥٓ أَحَدٌۭ

fayawma-idhin lā yuʿadhibu ʿadhābahu aḥadun

To, a rãnar nan bãbu wani mai yin azãba irin azãbar Allah.

26

وَلَا يُوثِقُ وَثَاقَهُۥٓ أَحَدٌۭ

walā yūthiqu wathāqahu aḥadun

Kuma bãbu wani mai ɗauri irin ɗaurin Sa.

27

يَـٰٓأَيَّتُهَا ٱلنَّفْسُ ٱلْمُطْمَئِنَّةُ

yāayyatuhā l-nafsu l-muṭ'ma-inatu

Yã kai rai mai natsuwa!

28

ٱرْجِعِىٓ إِلَىٰ رَبِّكِ رَاضِيَةًۭ مَّرْضِيَّةًۭ

ir'jiʿī ilā rabbiki rāḍiyatan marḍiyyatan

Ka koma zuwa ga Ubangijinka, alhãli kana mai yarda (da abin da Ya ƙaddara maka a dũniya) abar yardarwa (da sakamakon da zã a ba ka a Lãhira).

29

فَٱدْخُلِى فِى عِبَـٰدِى

fa-ud'khulī fī ʿibādī

Sabõbda haka, ka shiga cikin bãyi Na (mãsu bin umurui a dũniya).

30

وَٱدْخُلِى جَنَّتِى

wa-ud'khulī jannatī

Kuma ka shiga AljannaTa (a Lãhira).

Game da Wannan Sura