88

الغاشية

Al-Ghashiyah

The Overwhelming

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ Da sunan Allah Mai rahama Mai jin kai
Ayoyi 26
Juzu'i 30
Shafi 592
Nau'i Makkiya
Tsarin Saukarwa 68
0:00 / 0:00
Aya: 1 / 26
1

هَلْ أَتَىٰكَ حَدِيثُ ٱلْغَـٰشِيَةِ

hal atāka ḥadīthu l-ghāshiyati

Lalle ne labãrin (¡iyãma) mai rufe mutãne da tsoronta yã zo maka?

2

وُجُوهٌۭ يَوْمَئِذٍ خَـٰشِعَةٌ

wujūhun yawma-idhin khāshiʿatun

Wasu huskõki a rãnar nan ƙasƙantattu ne.

3

عَامِلَةٌۭ نَّاصِبَةٌۭ

ʿāmilatun nāṣibatun

Mãsu aikin wahala ne, mãsu gajiya.

4

تَصْلَىٰ نَارًا حَامِيَةًۭ

taṣlā nāran ḥāmiyatan

Zã su shiga wata wuta mai zãfi.

5

تُسْقَىٰ مِنْ عَيْنٍ ءَانِيَةٍۢ

tus'qā min ʿaynin āniyatin

Ana shãyar da su daga wani marmaro mai zãfin ruwa.

6

لَّيْسَ لَهُمْ طَعَامٌ إِلَّا مِن ضَرِيعٍۢ

laysa lahum ṭaʿāmun illā min ḍarīʿin

Ba su da wani abinci fãce dai daga danyi.

7

لَّا يُسْمِنُ وَلَا يُغْنِى مِن جُوعٍۢ

lā yus'minu walā yugh'nī min jūʿin

Bã ya sanya ƙiba, kuma bã zai wadãtar daga yunwa ba.

8

وُجُوهٌۭ يَوْمَئِذٍۢ نَّاعِمَةٌۭ

wujūhun yawma-idhin nāʿimatun

Wasu huskõki a rãnar nan mãsu ni'ima ne.

9

لِّسَعْيِهَا رَاضِيَةٌۭ

lisaʿyihā rāḍiyatun

Game da aikinsu, masu yarda ne.

10

فِى جَنَّةٍ عَالِيَةٍۢ

fī jannatin ʿāliyatin

(Suna) a cikin Aljanna maɗaukakiya.

11

لَّا تَسْمَعُ فِيهَا لَـٰغِيَةًۭ

lā tasmaʿu fīhā lāghiyatan

Bã zã su ji yãsassar magana ba, a cikinta.

12

فِيهَا عَيْنٌۭ جَارِيَةٌۭ

fīhā ʿaynun jāriyatun

A cikinta akwai marmaro mai gudãna.

13

فِيهَا سُرُرٌۭ مَّرْفُوعَةٌۭ

fīhā sururun marfūʿatun

A cikinta akwai gadãje maɗaukaka.

14

وَأَكْوَابٌۭ مَّوْضُوعَةٌۭ

wa-akwābun mawḍūʿatun

Da kõfuna ar'aje.

15

وَنَمَارِقُ مَصْفُوفَةٌۭ

wanamāriqu maṣfūfatun

Da filõli1 jẽre,

16

وَزَرَابِىُّ مَبْثُوثَةٌ

wazarābiyyu mabthūthatun

Da katifu shimfiɗe.

17

أَفَلَا يَنظُرُونَ إِلَى ٱلْإِبِلِ كَيْفَ خُلِقَتْ

afalā yanẓurūna ilā l-ibili kayfa khuliqat

Ashe to bã zã su dũbãwa ba ga rãƙumã yadda aka halitta su?

18

وَإِلَى ٱلسَّمَآءِ كَيْفَ رُفِعَتْ

wa-ilā l-samāi kayfa rufiʿat

Da zuwa ga sama yadda aka ɗaukaka ta?

19

وَإِلَى ٱلْجِبَالِ كَيْفَ نُصِبَتْ

wa-ilā l-jibāli kayfa nuṣibat

Da zuwa ga duwãtsu yadda aka kafa su?

20

وَإِلَى ٱلْأَرْضِ كَيْفَ سُطِحَتْ

wa-ilā l-arḍi kayfa suṭiḥat

Da zuwa ga ƙasa yadda aka shimfiɗã ta?

21

فَذَكِّرْ إِنَّمَآ أَنتَ مُذَكِّرٌۭ

fadhakkir innamā anta mudhakkirun

sabõda haka, ka yi wa'azi, kai mai yin wa'azi ne kawai.

22

لَّسْتَ عَلَيْهِم بِمُصَيْطِرٍ

lasta ʿalayhim bimuṣayṭirin

Ba ka zama mai ĩkon tanƙwasãwa a kansu ba.

23

إِلَّا مَن تَوَلَّىٰ وَكَفَرَ

illā man tawallā wakafara

Fãce dai duk wanda ya jũya bãya, kuma ya kãfirta.

24

فَيُعَذِّبُهُ ٱللَّهُ ٱلْعَذَابَ ٱلْأَكْبَرَ

fayuʿadhibuhu l-lahu l-ʿadhāba l-akbara

To, Allah zai yi masa azãba, azãbar nan da take mafi girma.

25

إِنَّ إِلَيْنَآ إِيَابَهُمْ

inna ilaynā iyābahum

Lalle ne, zuwa gare Mu kõmõwarsu take.

26

ثُمَّ إِنَّ عَلَيْنَا حِسَابَهُم

thumma inna ʿalaynā ḥisābahum

Sa'an nan lalle ne aikinMu ne Mu yi musu hisãbi.

Game da Wannan Sura