75

القيامة

Al-Qiyamah

The Resurrection

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ Da sunan Allah Mai rahama Mai jin kai
Ayoyi 40
Juzu'i 29
Shafi 577-578
Nau'i Makkiya
Tsarin Saukarwa 31
0:00 / 0:00
Aya: 1 / 40
1

لَآ أُقْسِمُ بِيَوْمِ ٱلْقِيَـٰمَةِ

lā uq'simu biyawmi l-qiyāmati

Bã sai Nã yi rantsuwa1 da Rãnar ¡iyãma ba.

2

وَلَآ أُقْسِمُ بِٱلنَّفْسِ ٱللَّوَّامَةِ

walā uq'simu bil-nafsi l-lawāmati

Bã sai Nã yi rantsuwa da rai mai yawan zargin1 kansa ba.

3

أَيَحْسَبُ ٱلْإِنسَـٰنُ أَلَّن نَّجْمَعَ عِظَامَهُۥ

ayaḥsabu l-insānu allan najmaʿa ʿiẓāmahu

Sin, mutum yana zaton cẽwa bã zã Mu tãra ƙasusuwansa ba?

4

بَلَىٰ قَـٰدِرِينَ عَلَىٰٓ أَن نُّسَوِّىَ بَنَانَهُۥ

balā qādirīna ʿalā an nusawwiya banānahu

Na'am! Mãsu ĩkon yi Muke a kan Mu daidaita gaɓõɓin yãtsunsa.

5

بَلْ يُرِيدُ ٱلْإِنسَـٰنُ لِيَفْجُرَ أَمَامَهُۥ

bal yurīdu l-insānu liyafjura amāmahu

Ba haka ba! Mutum so yake, ya yi fãjirci, ya ƙaryata abin da yake a gabansa.

6

يَسْـَٔلُ أَيَّانَ يَوْمُ ٱلْقِيَـٰمَةِ

yasalu ayyāna yawmu l-qiyāmati

Yanã tambaya: "Yaushe ne Rãnar ¡iyãma?"

7

فَإِذَا بَرِقَ ٱلْبَصَرُ

fa-idhā bariqa l-baṣaru

To, idan gani ya ɗimauta (ya yi ƙyalli).

8

وَخَسَفَ ٱلْقَمَرُ

wakhasafa l-qamaru

Kuma, watã ya yi husũfi (haskensa ya dushe).

9

وَجُمِعَ ٱلشَّمْسُ وَٱلْقَمَرُ

wajumiʿa l-shamsu wal-qamaru

Aka tãra rãnã da watã

10

يَقُولُ ٱلْإِنسَـٰنُ يَوْمَئِذٍ أَيْنَ ٱلْمَفَرُّ

yaqūlu l-insānu yawma-idhin ayna l-mafaru

Mutum zai ce a rãn nan "Ina wurin gudu?"

11

كَلَّا لَا وَزَرَ

kallā lā wazara

A'aha! bãbu mafaka.

12

إِلَىٰ رَبِّكَ يَوْمَئِذٍ ٱلْمُسْتَقَرُّ

ilā rabbika yawma-idhin l-mus'taqaru

zuwa ga Ubangijinka wurin tabbata, a rãnar nan, yake.

13

يُنَبَّؤُا۟ ٱلْإِنسَـٰنُ يَوْمَئِذٍۭ بِمَا قَدَّمَ وَأَخَّرَ

yunabba-u l-insānu yawma-idhin bimā qaddama wa-akhara

Ana gayã wa mutum, a rãnar nan, abin da ya gabatar da wanda ya jinkirtar.

14

بَلِ ٱلْإِنسَـٰنُ عَلَىٰ نَفْسِهِۦ بَصِيرَةٌۭ

bali l-insānu ʿalā nafsihi baṣīratun

Ba haka ba! Mutum, ga abin da ya shafi kansa, masani ne.

15

وَلَوْ أَلْقَىٰ مَعَاذِيرَهُۥ

walaw alqā maʿādhīrahu

Kuma ko da yã jẽfa uzurorinsa (bã zã a saurãre shi ba).

16

لَا تُحَرِّكْ بِهِۦ لِسَانَكَ لِتَعْجَلَ بِهِۦٓ

lā tuḥarrik bihi lisānaka litaʿjala bihi

Kada ka mõtsar1 da harshenka game da shi dõmin ka yi gaugãwar riƙe shi (Alƙur'ãni).

17

إِنَّ عَلَيْنَا جَمْعَهُۥ وَقُرْءَانَهُۥ

inna ʿalaynā jamʿahu waqur'ānahu

Lalle ne, wãjibi ne a gare Mu, Mu tãra shi. Mu (tsare maka) karãtunsa.

18

فَإِذَا قَرَأْنَـٰهُ فَٱتَّبِعْ قُرْءَانَهُۥ

fa-idhā qaranāhu fa-ittabiʿ qur'ānahu

To idan Muka karanta shi sai ka bi karatunsa.

19

ثُمَّ إِنَّ عَلَيْنَا بَيَانَهُۥ

thumma inna ʿalaynā bayānahu

sa'an nan, lalle wãjibi ne a gare Mu, bayãninsa.

20

كَلَّا بَلْ تُحِبُّونَ ٱلْعَاجِلَةَ

kallā bal tuḥibbūna l-ʿājilata

A'aha! Bã haka ba kunã son mai gaugawar nan (duniya) ne.

21

وَتَذَرُونَ ٱلْـَٔاخِرَةَ

watadharūna l-ākhirata

Kunã barin ta ƙarshen (Lãhira).

22

وُجُوهٌۭ يَوْمَئِذٍۢ نَّاضِرَةٌ

wujūhun yawma-idhin nāḍiratun

Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu annuri ne.

23

إِلَىٰ رَبِّهَا نَاظِرَةٌۭ

ilā rabbihā nāẓiratun

Zuwa ga Ubangijinsu mãsu kallo ne.

24

وَوُجُوهٌۭ يَوْمَئِذٍۭ بَاسِرَةٌۭ

wawujūhun yawma-idhin bāsiratun

Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu gintsẽwa ne.

25

تَظُنُّ أَن يُفْعَلَ بِهَا فَاقِرَةٌۭ

taẓunnu an yuf'ʿala bihā fāqiratun

Sunã zaton a sako musu masĩfa mai karya tsatso.

26

كَلَّآ إِذَا بَلَغَتِ ٱلتَّرَاقِىَ

kallā idhā balaghati l-tarāqiya

A'aha! Iadan (rai) ya kai ga karankarmai.

27

وَقِيلَ مَنْ ۜ رَاقٍۢ

waqīla man rāqin

kuma aka ce: "Wãne ne mai tawada?"

28

وَظَنَّ أَنَّهُ ٱلْفِرَاقُ

waẓanna annahu l-firāqu

Kuma ya tabbata cẽwa rabuwa dai ce.

29

وَٱلْتَفَّتِ ٱلسَّاقُ بِٱلسَّاقِ

wal-tafati l-sāqu bil-sāqi

Kuma ƙwabri ya lauye da wani ƙwabri.

30

إِلَىٰ رَبِّكَ يَوْمَئِذٍ ٱلْمَسَاقُ

ilā rabbika yawma-idhin l-masāqu

Zuwa ga Ubangijinka, a rãnar nan, magargaɗa1 take.

31

فَلَا صَدَّقَ وَلَا صَلَّىٰ

falā ṣaddaqa walā ṣallā

To, bai gaskatã ba, kuma bai yi salla ba!

32

وَلَـٰكِن كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰ

walākin kadhaba watawallā

Amma dai ya ƙaryata, kuma ya jũya baya!

33

ثُمَّ ذَهَبَ إِلَىٰٓ أَهْلِهِۦ يَتَمَطَّىٰٓ

thumma dhahaba ilā ahlihi yatamaṭṭā

Sa'an nan, ya tafi zuwa ga mutãnensa, yana tãƙama.

34

أَوْلَىٰ لَكَ فَأَوْلَىٰ

awlā laka fa-awlā

Halaka tã tabbata a gare ka, sa'an nan ita ce mafi dãcewa.

35

ثُمَّ أَوْلَىٰ لَكَ فَأَوْلَىٰٓ

thumma awlā laka fa-awlā

Sa'an nan, wata halaka tã tabbata a gare ka dõmin tã fi dãce wa.

36

أَيَحْسَبُ ٱلْإِنسَـٰنُ أَن يُتْرَكَ سُدًى

ayaḥsabu l-insānu an yut'raka sudan

Shin, mutum nã zaton a bar shi sagaga (wãto bãbu nufin kõme game da shi)?

37

أَلَمْ يَكُ نُطْفَةًۭ مِّن مَّنِىٍّۢ يُمْنَىٰ

alam yaku nuṭ'fatan min maniyyin yum'nā

Bai kasance ɗigo na maniyyi ba, wanda ake jefarwa (a cikin mahaifa)

38

ثُمَّ كَانَ عَلَقَةًۭ فَخَلَقَ فَسَوَّىٰ

thumma kāna ʿalaqatan fakhalaqa fasawwā

Sa'an nan, ya zama gudan jini, sa'an nan Allah Ya halitta shi, sa'an nan Ya daidaita gaɓõɓinsa;

39

فَجَعَلَ مِنْهُ ٱلزَّوْجَيْنِ ٱلذَّكَرَ وَٱلْأُنثَىٰٓ

fajaʿala min'hu l-zawjayni l-dhakara wal-unthā

Sa'an nan, Ya sanya daga gare shi, nau'i biyu: namiji damace?

40

أَلَيْسَ ذَٰلِكَ بِقَـٰدِرٍ عَلَىٰٓ أَن يُحْـِۧىَ ٱلْمَوْتَىٰ

alaysa dhālika biqādirin ʿalā an yuḥ'yiya l-mawtā

Ashẽ wannan bai zama Mai iko ba bisa ga rãyar da matattu?1

Game da Wannan Sura