74

المدثر

Al-Muddaththir

The Cloaked One

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ Da sunan Allah Mai rahama Mai jin kai
Ayoyi 56
Juzu'i 29
Shafi 575-577
Nau'i Makkiya
Tsarin Saukarwa 4
0:00 / 0:00
Aya: 1 / 56
1

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلْمُدَّثِّرُ

yāayyuhā l-mudathiru

Yã wanda ya lulluɓa da mayãfi.

2

قُمْ فَأَنذِرْ

qum fa-andhir

Ka tãshi dõmin ka yi gargaɗi

3

وَرَبَّكَ فَكَبِّرْ

warabbaka fakabbir

Kuma Ubangijinka, sai ka girmama Shi,

4

وَثِيَابَكَ فَطَهِّرْ

wathiyābaka faṭahhir

Kuma tutãfinka, sai ka tsarkake su,

5

وَٱلرُّجْزَ فَٱهْجُرْ

wal-ruj'za fa-uh'jur

Kuma gumãka, sai ka ƙaurace musu.

6

وَلَا تَمْنُن تَسْتَكْثِرُ

walā tamnun tastakthiru

Kada ka yi kyauta kana nẽman ƙãri

7

وَلِرَبِّكَ فَٱصْبِرْ

walirabbika fa-iṣ'bir

Kuma sabõda Ubangijinka? Sai ka yi haƙure

8

فَإِذَا نُقِرَ فِى ٱلنَّاقُورِ

fa-idhā nuqira fī l-nāqūri

To, idan aka yi bũsa a cikin ƙaho.

9

فَذَٰلِكَ يَوْمَئِذٍۢ يَوْمٌ عَسِيرٌ

fadhālika yawma-idhin yawmun ʿasīrun

To, wannan, a rãnar nan, yini ne mai wuya

10

عَلَى ٱلْكَـٰفِرِينَ غَيْرُ يَسِيرٍۢ

ʿalā l-kāfirīna ghayru yasīrin

A kan kãfirai, bã mai sauƙi ba ne.

11

ذَرْنِى وَمَنْ خَلَقْتُ وَحِيدًۭا

dharnī waman khalaqtu waḥīdan

Ka bar Ni da wanda Na halitta, yana shi kaɗai,

12

وَجَعَلْتُ لَهُۥ مَالًۭا مَّمْدُودًۭا

wajaʿaltu lahu mālan mamdūdan

Kuma Na sanya masa dũkiya shimfiɗaɗɗiya

13

وَبَنِينَ شُهُودًۭا

wabanīna shuhūdan

Da ɗiyã halartattu,

14

وَمَهَّدتُّ لَهُۥ تَمْهِيدًۭا

wamahhadttu lahu tamhīdan

Kuma Na shimfiɗa? masa kõme shimfiɗãwa.

15

ثُمَّ يَطْمَعُ أَنْ أَزِيدَ

thumma yaṭmaʿu an azīda

Sa'an nan, yanã kwaɗayin in yi masa ƙãri!

16

كَلَّآ ۖ إِنَّهُۥ كَانَ لِـَٔايَـٰتِنَا عَنِيدًۭا

kallā innahu kāna liāyātinā ʿanīdan

Faufau! Lalle ne, shĩ yã kasance, ga ãyõyin Mu, mai tsaurin kai.

17

سَأُرْهِقُهُۥ صَعُودًا

sa-ur'hiquhu ṣaʿūdan

Zã Ni kallafa masa wahala mai hauhawa.

18

إِنَّهُۥ فَكَّرَ وَقَدَّرَ

innahu fakkara waqaddara

Lalle ne, Shi, yã yi tunãni, kuma yã ƙaddara (abin da zai faɗã game da Alƙur'ãni)

19

فَقُتِلَ كَيْفَ قَدَّرَ

faqutila kayfa qaddara

Sabõda haka, aka la'ane shi, kamar yadda ya ƙaddara.

20

ثُمَّ قُتِلَ كَيْفَ قَدَّرَ

thumma qutila kayfa qaddara

Sa'an nan, aka la'ane shi kamar yadda ya ƙaddara.

21

ثُمَّ نَظَرَ

thumma naẓara

Sa'an nan, ya yi tunãni

22

ثُمَّ عَبَسَ وَبَسَرَ

thumma ʿabasa wabasara

Sa'an nan, ya gintse huska? kuma ya yi murtuk.

23

ثُمَّ أَدْبَرَ وَٱسْتَكْبَرَ

thumma adbara wa-is'takbara

Sa'an nan, ya jũya bãya, kuma ya bunƙãsa,

24

فَقَالَ إِنْ هَـٰذَآ إِلَّا سِحْرٌۭ يُؤْثَرُ

faqāla in hādhā illā siḥ'run yu'tharu

Sai ya ce: "Wannan abu dai bã kõme ba ne fãce wani sihiri, wanda aka ruwaito."

25

إِنْ هَـٰذَآ إِلَّا قَوْلُ ٱلْبَشَرِ

in hādhā illā qawlu l-bashari

"Wannan maganar mutum dai ce."

26

سَأُصْلِيهِ سَقَرَ

sa-uṣ'līhi saqara

Zã Ni ƙõna shi da Saƙar.

27

وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا سَقَرُ

wamā adrāka mā saqaru

Kuma mẽ ya sanar da kai abin da akẽ cẽwa Saƙar!

28

لَا تُبْقِى وَلَا تَذَرُ

lā tub'qī walā tadharu

Bã ta ragẽwa, kuma bã ta bari.

29

لَوَّاحَةٌۭ لِّلْبَشَرِ

lawwāḥatun lil'bashari

Mai nãcẽwa ga jiki ce (da (ƙũna).

30

عَلَيْهَا تِسْعَةَ عَشَرَ

ʿalayhā tis'ʿata ʿashara

A kanta akwai (matsara) gõma shã tara.

31

وَمَا جَعَلْنَآ أَصْحَـٰبَ ٱلنَّارِ إِلَّا مَلَـٰٓئِكَةًۭ ۙ وَمَا جَعَلْنَا عِدَّتَهُمْ إِلَّا فِتْنَةًۭ لِّلَّذِينَ كَفَرُوا۟ لِيَسْتَيْقِنَ ٱلَّذِينَ أُوتُوا۟ ٱلْكِتَـٰبَ وَيَزْدَادَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓا۟ إِيمَـٰنًۭا ۙ وَلَا يَرْتَابَ ٱلَّذِينَ أُوتُوا۟ ٱلْكِتَـٰبَ وَٱلْمُؤْمِنُونَ ۙ وَلِيَقُولَ ٱلَّذِينَ فِى قُلُوبِهِم مَّرَضٌۭ وَٱلْكَـٰفِرُونَ مَاذَآ أَرَادَ ٱللَّهُ بِهَـٰذَا مَثَلًۭا ۚ كَذَٰلِكَ يُضِلُّ ٱللَّهُ مَن يَشَآءُ وَيَهْدِى مَن يَشَآءُ ۚ وَمَا يَعْلَمُ جُنُودَ رَبِّكَ إِلَّا هُوَ ۚ وَمَا هِىَ إِلَّا ذِكْرَىٰ لِلْبَشَرِ

wamā jaʿalnā aṣḥāba l-nāri illā malāikatan wamā jaʿalnā ʿiddatahum illā fit'natan lilladhīna kafarū liyastayqina alladhīna ūtū l-kitāba wayazdāda alladhīna āmanū īmānan walā yartāba alladhīna ūtū l-kitāba wal-mu'minūna waliyaqūla alladhīna fī qulūbihim maraḍun wal-kāfirūna mādhā arāda l-lahu bihādhā mathalan kadhālika yuḍillu l-lahu man yashāu wayahdī man yashāu wamā yaʿlamu junūda rabbika illā huwa wamā hiya illā dhik'rā lil'bashari

Kuma ba Mu sanya ma'abũta wutã (wãto matsaranta) ba, fãce malã'iku, kuma ba Mu sanya adadinsu (gõma sha tara) ba, fãce dõmin fitina ga waɗanda suka kãfirta domin waɗanda aka bai wa littãfi su sãmi yaƙĩni kuma waɗanda suka yi ĩmãni su ƙãra ĩmãni, kuma waɗanda aka bai wa littãfi da mũminai bã zã su yi shakka ba, kuma domin wa ɗanda a cikin zukatansu akwai wata cuta da kãfirai su ce: "Mẽ Allah Yake nufi da wannan, ya kasance misãli?" Haka dai Allah ke ɓatar da wanda Ya so, kuma Ya shiryar da wanda ya so. Kuma bãbu wanda ya san mayãƙan Ubangijinka fãce Shi, kuma ita (wutar) ba ta kasance ba fãce wata tunãtarwa ce ga mutum.

32

كَلَّا وَٱلْقَمَرِ

kallā wal-qamari

A'aha! Ina rantsuwa da watã.

33

وَٱلَّيْلِ إِذْ أَدْبَرَ

wa-al-layli idh adbara

Da dare a lõkacin da ya jũyar da baya.

34

وَٱلصُّبْحِ إِذَآ أَسْفَرَ

wal-ṣub'ḥi idhā asfara

Da sãfiya idan ta wãye.

35

إِنَّهَا لَإِحْدَى ٱلْكُبَرِ

innahā la-iḥ'dā l-kubari

Ita (wutar) ɗayan manyan masĩfũ? ce.

36

نَذِيرًۭا لِّلْبَشَرِ

nadhīran lil'bashari

Mai gargaɗĩ ce ga mutum.

37

لِمَن شَآءَ مِنكُمْ أَن يَتَقَدَّمَ أَوْ يَتَأَخَّرَ

liman shāa minkum an yataqaddama aw yata-akhara

Ga wanda ya so, daga cikinku, ya gabãta ko ya jinkirta.

38

كُلُّ نَفْسٍۭ بِمَا كَسَبَتْ رَهِينَةٌ

kullu nafsin bimā kasabat rahīnatun

Kõwane rai ga abin da ya aikata jingina ce.

39

إِلَّآ أَصْحَـٰبَ ٱلْيَمِينِ

illā aṣḥāba l-yamīni

Fãce mutãnen dãma.

40

فِى جَنَّـٰتٍۢ يَتَسَآءَلُونَ

fī jannātin yatasāalūna

A cikin Aljanna suna tambayar jũna.

41

عَنِ ٱلْمُجْرِمِينَ

ʿani l-muj'rimīna

Game da mãsu laifi.

42

مَا سَلَكَكُمْ فِى سَقَرَ

mā salakakum fī saqara

(Su ce musu) "Me ya shigar da ku a cikin Saƙar?"

43

قَالُوا۟ لَمْ نَكُ مِنَ ٱلْمُصَلِّينَ

qālū lam naku mina l-muṣalīna

Suka ce: "Ba mu kasance munã a cikin mãsu salla ba."

44

وَلَمْ نَكُ نُطْعِمُ ٱلْمِسْكِينَ

walam naku nuṭ'ʿimu l-mis'kīna

"Kuma ba mu kasance muna ciyar da matalautã ba."

45

وَكُنَّا نَخُوضُ مَعَ ٱلْخَآئِضِينَ

wakunnā nakhūḍu maʿa l-khāiḍīna

"Kuma mun kasance muna kũtsãwa tãre da mãsu kũtsãwa."

46

وَكُنَّا نُكَذِّبُ بِيَوْمِ ٱلدِّينِ

wakunnā nukadhibu biyawmi l-dīni

"Mun kasance munã ƙaryata rãnar sãkamako."

47

حَتَّىٰٓ أَتَىٰنَا ٱلْيَقِينُ

ḥattā atānā l-yaqīnu

"Har gaskiya (wãto mutuwa) ta zo mana."

48

فَمَا تَنفَعُهُمْ شَفَـٰعَةُ ٱلشَّـٰفِعِينَ

famā tanfaʿuhum shafāʿatu l-shāfiʿīna

Sabõda haka cẽton mãsu cẽto bã zai amfãne su ba.

49

فَمَا لَهُمْ عَنِ ٱلتَّذْكِرَةِ مُعْرِضِينَ

famā lahum ʿani l-tadhkirati muʿ'riḍīna

Haba! Me ya same su, suka zama mãsu bijirewa daga wa'azin gaskiya.

50

كَأَنَّهُمْ حُمُرٌۭ مُّسْتَنفِرَةٌۭ

ka-annahum ḥumurun mus'tanfiratun

Kamar dai sũ, jãkuna firgitattu ne.

51

فَرَّتْ مِن قَسْوَرَةٍۭ

farrat min qaswaratin

Sun gudu daga zãki.

52

بَلْ يُرِيدُ كُلُّ ٱمْرِئٍۢ مِّنْهُمْ أَن يُؤْتَىٰ صُحُفًۭا مُّنَشَّرَةًۭ

bal yurīdu kullu im'ri-in min'hum an yu'tā ṣuḥufan munasharatan

A'aha! Kõwãne mutum daga cikinsu yanã son a zo masa da takardu (da sũnansa) ana wãtsãwa

53

كَلَّا ۖ بَل لَّا يَخَافُونَ ٱلْـَٔاخِرَةَ

kallā bal lā yakhāfūna l-ākhirata

A'aha! Kai dai, bã su jin tsõron Lãhira.

54

كَلَّآ إِنَّهُۥ تَذْكِرَةٌۭ

kallā innahu tadhkiratun

A'aha! Lalle ne, shi (Alƙur'ãni) tunãtarwa ce.

55

فَمَن شَآءَ ذَكَرَهُۥ

faman shāa dhakarahu

Dõmin wanda ya so, ya tuna.

56

وَمَا يَذْكُرُونَ إِلَّآ أَن يَشَآءَ ٱللَّهُ ۚ هُوَ أَهْلُ ٱلتَّقْوَىٰ وَأَهْلُ ٱلْمَغْفِرَةِ

wamā yadhkurūna illā an yashāa l-lahu huwa ahlu l-taqwā wa-ahlu l-maghfirati

Kuma bã zã su tuna ba fãce idan Allah Ya so, Shi ne Ya cancanta a bi Shi da taƙawa kuma Ya cancanta ga Ya yi gãfara.

Game da Wannan Sura