96

العلق

Al-Alaq

The Clot

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ Da sunan Allah Mai rahama Mai jin kai
Ayoyi 19
Juzu'i 30
Shafi 597
Nau'i Makkiya
Tsarin Saukarwa 1
0:00 / 0:00
Aya: 1 / 19
1

ٱقْرَأْ بِٱسْمِ رَبِّكَ ٱلَّذِى خَلَقَ

iq'ra bi-is'mi rabbika alladhī khalaqa

Ka yi karatu da sunan Ubangijinka, wanda Ya yi halitta.

2

خَلَقَ ٱلْإِنسَـٰنَ مِنْ عَلَقٍ

khalaqa l-insāna min ʿalaqin

Ya hahitta mutum daga gudan jini.

3

ٱقْرَأْ وَرَبُّكَ ٱلْأَكْرَمُ

iq'ra warabbuka l-akramu

Ka yi karatu, kuma Ubangijinka shi ne Mafi karimci.

4

ٱلَّذِى عَلَّمَ بِٱلْقَلَمِ

alladhī ʿallama bil-qalami

Wanda Ya sanar (da mutum) game da alƙalami.

5

عَلَّمَ ٱلْإِنسَـٰنَ مَا لَمْ يَعْلَمْ

ʿallama l-insāna mā lam yaʿlam

Ya sanar da mutum abin da bai sani ba.

6

كَلَّآ إِنَّ ٱلْإِنسَـٰنَ لَيَطْغَىٰٓ

kallā inna l-insāna layaṭghā

A'aha! Lalle, ne mutum haƙĩƙa, yana girman kai (ya ƙi karatu).

7

أَن رَّءَاهُ ٱسْتَغْنَىٰٓ

an raāhu is'taghnā

Dõmin yã ga kansa, yã wadãta.

8

إِنَّ إِلَىٰ رَبِّكَ ٱلرُّجْعَىٰٓ

inna ilā rabbika l-ruj'ʿā

Lalle ne zuwa ga Ubangijinka makoma take.

9

أَرَءَيْتَ ٱلَّذِى يَنْهَىٰ

ara-ayta alladhī yanhā

Shin, kã ga wanda ke hana.

10

عَبْدًا إِذَا صَلَّىٰٓ

ʿabdan idhā ṣallā

Bãwã idan yã yi salla?

11

أَرَءَيْتَ إِن كَانَ عَلَى ٱلْهُدَىٰٓ

ara-ayta in kāna ʿalā l-hudā

Ashe, kã gani, idan (shi bãwan) ya kasance a kan shiriya?

12

أَوْ أَمَرَ بِٱلتَّقْوَىٰٓ

aw amara bil-taqwā

Ko ya yi umurni da taƙawa?

13

أَرَءَيْتَ إِن كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰٓ

ara-ayta in kadhaba watawallā

Ashe, kã gani, idan (shi mai hanin) ya ƙaryata, kuma ya jũya bãya?

14

أَلَمْ يَعْلَم بِأَنَّ ٱللَّهَ يَرَىٰ

alam yaʿlam bi-anna l-laha yarā

Ashe, bai sani ba cewa Allah Yanã gani?

15

كَلَّا لَئِن لَّمْ يَنتَهِ لَنَسْفَعًۢا بِٱلنَّاصِيَةِ

kallā la-in lam yantahi lanasfaʿan bil-nāṣiyati

A'aha! Lalle ne, idan bai hanu ba, lalle ne zã Mu ja gãshin makwarkwaɗa.

16

نَاصِيَةٍۢ كَـٰذِبَةٍ خَاطِئَةٍۢ

nāṣiyatin kādhibatin khāṭi-atin

Makwarkwaɗa maƙaryaciya, mai laifi.

17

فَلْيَدْعُ نَادِيَهُۥ

falyadʿu nādiyahu

Sai ya kirayi ƙungiyarsa.

18

سَنَدْعُ ٱلزَّبَانِيَةَ

sanadʿu l-zabāniyata

Zã Mu kirayi zabaniyãwa (mala'iku mãsu girma).

19

كَلَّا لَا تُطِعْهُ وَٱسْجُدْ وَٱقْتَرِب ۩

kallā lā tuṭiʿ'hu wa-us'jud wa-iq'tarib

A'aha kada ka bĩ shi. Kuma ka yi tawali'u,1 kuma ka nemi kusanta (zuwa ga Ubangijinka).

Sujada

Game da Wannan Sura