86

الطارق

At-Tariq

The Morning Star

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ Da sunan Allah Mai rahama Mai jin kai
Ayoyi 17
Juzu'i 30
Shafi 591
Nau'i Makkiya
Tsarin Saukarwa 36
0:00 / 0:00
Aya: 1 / 17
1

وَٱلسَّمَآءِ وَٱلطَّارِقِ

wal-samāi wal-ṭāriqi

Inã rantsuwa da sama da mai aukõwa da dare.

2

وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا ٱلطَّارِقُ

wamā adrāka mā l-ṭāriqu

To, mẽ yã sanar da kai abin da ake cẽwa mai aukõwa da dare?

3

ٱلنَّجْمُ ٱلثَّاقِبُ

al-najmu l-thāqibu

Shi ne taurãron nan mai tsananin haske.1

4

إِن كُلُّ نَفْسٍۢ لَّمَّا عَلَيْهَا حَافِظٌۭ

in kullu nafsin lammā ʿalayhā ḥāfiẓun

Bãbu wani rai fãce a kansa akwai wani mai tsaro.

5

فَلْيَنظُرِ ٱلْإِنسَـٰنُ مِمَّ خُلِقَ

falyanẓuri l-insānu mimma khuliqa

To, mutum ya dũba, daga mẽ aka halittã shi?

6

خُلِقَ مِن مَّآءٍۢ دَافِقٍۢ

khuliqa min māin dāfiqin

An halittã shi daga wani ruwa mai tunkuɗar jũna.

7

يَخْرُجُ مِنۢ بَيْنِ ٱلصُّلْبِ وَٱلتَّرَآئِبِ

yakhruju min bayni l-ṣul'bi wal-tarāibi

Yanã fita daga tsakanin tsatso da karankarman ƙirji.

8

إِنَّهُۥ عَلَىٰ رَجْعِهِۦ لَقَادِرٌۭ

innahu ʿalā rajʿihi laqādirun

Lalle ne Shi (Allah), ga mayar da shi (mutum), tabbas Mai iyãwa ne.

9

يَوْمَ تُبْلَى ٱلسَّرَآئِرُ

yawma tub'lā l-sarāiru

Rãnar da ake jarrabawar asirai.

10

فَمَا لَهُۥ مِن قُوَّةٍۢ وَلَا نَاصِرٍۢ

famā lahu min quwwatin walā nāṣirin

Saboda haka, bã shi da wani ƙarfi, kuma bã shi da wani mai taimako (da zai iya kãre shi daga azãbar Allah).

11

وَٱلسَّمَآءِ ذَاتِ ٱلرَّجْعِ

wal-samāi dhāti l-rajʿi

Ina rantsuwa da sama ma'abũciyar ruwa mai kõmãwa yana yankẽwa.

12

وَٱلْأَرْضِ ذَاتِ ٱلصَّدْعِ

wal-arḍi dhāti l-ṣadʿi

Da ƙasa ma'abociyar tsãgẽwa,1

13

إِنَّهُۥ لَقَوْلٌۭ فَصْلٌۭ

innahu laqawlun faṣlun

Lalle ne shĩ (Alƙur'ãni), haƙĩƙa magana ce daki-daki1

14

وَمَا هُوَ بِٱلْهَزْلِ

wamā huwa bil-hazli

Kuma shĩ bã bananci1 bane

15

إِنَّهُمْ يَكِيدُونَ كَيْدًۭا

innahum yakīdūna kaydan

Lalle ne sũ, suna ƙulla kaidi na sõsai.

16

وَأَكِيدُ كَيْدًۭا

wa-akīdu kaydan

Kuma Ni, Ina mayar da kaidi (gare su) kamar yadda suke ƙulla kaidi.

17

فَمَهِّلِ ٱلْكَـٰفِرِينَ أَمْهِلْهُمْ رُوَيْدًۢا

famahhili l-kāfirīna amhil'hum ruwaydan

Saboda haka, ka yi wa kafirai jinkiri, ka dakata musu, sannu-sannu.

Game da Wannan Sura