26

الشعراء

Ash-Shu'ara

The Poets

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ Da sunan Allah Mai rahama Mai jin kai
Ayoyi 227
Juzu'i 19
Shafi 367-376
Nau'i Makkiya
Tsarin Saukarwa 47
0:00 / 0:00
Aya: 1 / 227
1

طسٓمٓ

tta-seen-meem

T. S̃. M̃.

2

تِلْكَ ءَايَـٰتُ ٱلْكِتَـٰبِ ٱلْمُبِينِ

til'ka āyātu l-kitābi l-mubīni

Waɗancan ãyõyin Littãfi ne bayyananne.

3

لَعَلَّكَ بَـٰخِعٌۭ نَّفْسَكَ أَلَّا يَكُونُوا۟ مُؤْمِنِينَ

laʿallaka bākhiʿun nafsaka allā yakūnū mu'minīna

Tsammãninka kai mai zaka halakar da ranka ne, dõn ba su zamanto mũminai ba! 1

4

إِن نَّشَأْ نُنَزِّلْ عَلَيْهِم مِّنَ ٱلسَّمَآءِ ءَايَةًۭ فَظَلَّتْ أَعْنَـٰقُهُمْ لَهَا خَـٰضِعِينَ

in nasha nunazzil ʿalayhim mina l-samāi āyatan faẓallat aʿnāquhum lahā khāḍiʿīna

Idan Mun so zã Mu saukar, a kansu, da wata ãyã daga sama, sai wuyõyinsu su yini sabõda ita sunã mãsu ƙasƙantar da kai.

5

وَمَا يَأْتِيهِم مِّن ذِكْرٍۢ مِّنَ ٱلرَّحْمَـٰنِ مُحْدَثٍ إِلَّا كَانُوا۟ عَنْهُ مُعْرِضِينَ

wamā yatīhim min dhik'rin mina l-raḥmāni muḥ'dathin illā kānū ʿanhu muʿ'riḍīna

Kuma wata tunãtarwa ba ta jẽ musu ba, daga Mai rahama, sãbuwa, fãce sun kasance daga barinta sunã mãsu bijirẽwa.

6

فَقَدْ كَذَّبُوا۟ فَسَيَأْتِيهِمْ أَنۢبَـٰٓؤُا۟ مَا كَانُوا۟ بِهِۦ يَسْتَهْزِءُونَ

faqad kadhabū fasayatīhim anbāu mā kānū bihi yastahziūna

To, lalle ne, sun ƙaryata, to, lãbãran abin da suka kasance sunã yi na izgili da shi zã ya je musu.

7

أَوَلَمْ يَرَوْا۟ إِلَى ٱلْأَرْضِ كَمْ أَنۢبَتْنَا فِيهَا مِن كُلِّ زَوْجٍۢ كَرِيمٍ

awalam yaraw ilā l-arḍi kam anbatnā fīhā min kulli zawjin karīmin

Shin, ba su dũba ba zuwa ga ƙasa, da yawa Muka tsirar a cikinta, daga dukan nau'i mai kyau?

8

إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَـَٔايَةًۭ ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ

inna fī dhālika laāyatan wamā kāna aktharuhum mu'minīna

Lalle ne, a cikin wancan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mũminai ba.

9

وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلْعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ

wa-inna rabbaka lahuwa l-ʿazīzu l-raḥīmu

Kuma lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai rahama.

10

وَإِذْ نَادَىٰ رَبُّكَ مُوسَىٰٓ أَنِ ٱئْتِ ٱلْقَوْمَ ٱلظَّـٰلِمِينَ

wa-idh nādā rabbuka mūsā ani i'ti l-qawma l-ẓālimīna

Kuma a lõkacin da Ubangijinka Ya kirãyi Mũsã, "Ka je wa mutãnen nan azzãlumai.

11

قَوْمَ فِرْعَوْنَ ۚ أَلَا يَتَّقُونَ

qawma fir'ʿawna alā yattaqūna

"Mutãnen Fir'auna bã zã su yi taƙawa ba?"

12

قَالَ رَبِّ إِنِّىٓ أَخَافُ أَن يُكَذِّبُونِ

qāla rabbi innī akhāfu an yukadhibūni

Ya ce: "Ya Ubangijĩna, nĩ inã tsõron su ƙaryata ni.

13

وَيَضِيقُ صَدْرِى وَلَا يَنطَلِقُ لِسَانِى فَأَرْسِلْ إِلَىٰ هَـٰرُونَ

wayaḍīqu ṣadrī walā yanṭaliqu lisānī fa-arsil ilā hārūna

"Kuma ƙirjĩna ya yi ƙunci1 kuma harshẽna bã zai saku ba sabõda haka ka aika zuwa ga Harũna.

14

وَلَهُمْ عَلَىَّ ذَنۢبٌۭ فَأَخَافُ أَن يَقْتُلُونِ

walahum ʿalayya dhanbun fa-akhāfu an yaqtulūni

"Kuma sunã da wani laifi a kaina, sabõda haka inã tsõron kada su kashe ni."

15

قَالَ كَلَّا ۖ فَٱذْهَبَا بِـَٔايَـٰتِنَآ ۖ إِنَّا مَعَكُم مُّسْتَمِعُونَ

qāla kallā fa-idh'habā biāyātinā innā maʿakum mus'tamiʿūna

Ya ce: "Kayya! Ku tafi, kũ biyu, da ÃyõyinMu. Lalle ne, Munã tãre da ku Munã Mãsu saurãre."

16

فَأْتِيَا فِرْعَوْنَ فَقُولَآ إِنَّا رَسُولُ رَبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ

fatiyā fir'ʿawna faqūlā innā rasūlu rabbi l-ʿālamīna

"Sai ku je wa Fir'auna, sa'an nan ku ce, Lalle ne, mu, Manzannin Ubangijin halitta ne."

17

أَنْ أَرْسِلْ مَعَنَا بَنِىٓ إِسْرَٰٓءِيلَ

an arsil maʿanā banī is'rāīla

"Ka saki Banĩ Isrã'ila tãre da mu."

18

قَالَ أَلَمْ نُرَبِّكَ فِينَا وَلِيدًۭا وَلَبِثْتَ فِينَا مِنْ عُمُرِكَ سِنِينَ

qāla alam nurabbika fīnā walīdan walabith'ta fīnā min ʿumurika sinīna

Ya ce: "Shin, ba mu yi rẽnonka ba a cikinmu kanã jãrĩri, kuma ka zauna a cikinmu shẽkarudaga lõkacin rãyuwarka?"

19

وَفَعَلْتَ فَعْلَتَكَ ٱلَّتِى فَعَلْتَ وَأَنتَ مِنَ ٱلْكَـٰفِرِينَ

wafaʿalta faʿlataka allatī faʿalta wa-anta mina l-kāfirīna

"Kuma ka aikata aikinka wanda ka aikata alhãli kai kanã daga butulai?"

20

قَالَ فَعَلْتُهَآ إِذًۭا وَأَنَا۠ مِنَ ٱلضَّآلِّينَ

qāla faʿaltuhā idhan wa-anā mina l-ḍālīna

Ya ce: "Na aikata shi a lõkacin inã daga mãsu jãhilcin fushi."

21

فَفَرَرْتُ مِنكُمْ لَمَّا خِفْتُكُمْ فَوَهَبَ لِى رَبِّى حُكْمًۭا وَجَعَلَنِى مِنَ ٱلْمُرْسَلِينَ

fafarartu minkum lammā khif'tukum fawahaba lī rabbī ḥuk'man wajaʿalanī mina l-mur'salīna

"Sabõda haka na gudu daga gãre ku a lõkacin da na ji tsõronku, sai Ubangijĩna Ya bã ni hukunci, kuma Ya sanya ni daga Manzanni."

22

وَتِلْكَ نِعْمَةٌۭ تَمُنُّهَا عَلَىَّ أَنْ عَبَّدتَّ بَنِىٓ إِسْرَٰٓءِيلَ

watil'ka niʿ'matun tamunnuhā ʿalayya an ʿabbadtta banī is'rāīla

"Kuma waccan ni'ima ce, kanã gõrint a kaina, dõmin kã bautar da Banĩ Isrã'ĩla."

23

قَالَ فِرْعَوْنُ وَمَا رَبُّ ٱلْعَـٰلَمِينَ

qāla fir'ʿawnu wamā rabbu l-ʿālamīna

Fir'auna ya ce: "Kuma mene ne Ubangijin halittu?"

24

قَالَ رَبُّ ٱلسَّمَـٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ وَمَا بَيْنَهُمَآ ۖ إِن كُنتُم مُّوقِنِينَ

qāla rabbu l-samāwāti wal-arḍi wamā baynahumā in kuntum mūqinīna

Ya ce: "Ubangijin sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu, idan kun kasance mãsu ƙarfin ĩmãni."

25

قَالَ لِمَنْ حَوْلَهُۥٓ أَلَا تَسْتَمِعُونَ

qāla liman ḥawlahu alā tastamiʿūna

Ya ce wa waɗanda suke a gẽfensa, "Bã za ku saurãra ba?"

26

قَالَ رَبُّكُمْ وَرَبُّ ءَابَآئِكُمُ ٱلْأَوَّلِينَ

qāla rabbukum warabbu ābāikumu l-awalīna

Ya ce: "Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku na farko."

27

قَالَ إِنَّ رَسُولَكُمُ ٱلَّذِىٓ أُرْسِلَ إِلَيْكُمْ لَمَجْنُونٌۭ

qāla inna rasūlakumu alladhī ur'sila ilaykum lamajnūnun

Ya ce: "Lalle ne Manzonku, wanda aka aiko zuwa gare ku, haƙi ƙa, mahaukaci ne."

28

قَالَ رَبُّ ٱلْمَشْرِقِ وَٱلْمَغْرِبِ وَمَا بَيْنَهُمَآ ۖ إِن كُنتُمْ تَعْقِلُونَ

qāla rabbu l-mashriqi wal-maghribi wamā baynahumā in kuntum taʿqilūna

Ya ce: "Ubangijin mafitar rãnã da maɓũyarta da abin dayake a tsakaninsu, idan kun kasance kunã hankalta."

29

قَالَ لَئِنِ ٱتَّخَذْتَ إِلَـٰهًا غَيْرِى لَأَجْعَلَنَّكَ مِنَ ٱلْمَسْجُونِينَ

qāla la-ini ittakhadhta ilāhan ghayrī la-ajʿalannaka mina l-masjūnīna

Ya ce: "Lalle ne idan ka riƙi wani abin bautãwa wanĩna haƙĩƙa, inã sanyã ka daga ɗaurarru."

30

قَالَ أَوَلَوْ جِئْتُكَ بِشَىْءٍۢ مُّبِينٍۢ

qāla awalaw ji'tuka bishayin mubīnin

Ya ce: "Ashe, kuma kõ dã nã zõ maka da wani, abu mai bayyanãwa?"

31

قَالَ فَأْتِ بِهِۦٓ إِن كُنتَ مِنَ ٱلصَّـٰدِقِينَ

qāla fati bihi in kunta mina l-ṣādiqīna

Ya ce: "To, ka zõ da shi idan ka kasance daga, mãsu gaskiya."

32

فَأَلْقَىٰ عَصَاهُ فَإِذَا هِىَ ثُعْبَانٌۭ مُّبِينٌۭ

fa-alqā ʿaṣāhu fa-idhā hiya thuʿ'bānun mubīnun

Sai ya jẽfa sandarsa, sai ga ta kumurci bayyananne.

33

وَنَزَعَ يَدَهُۥ فَإِذَا هِىَ بَيْضَآءُ لِلنَّـٰظِرِينَ

wanazaʿa yadahu fa-idhā hiya bayḍāu lilnnāẓirīna

Kuma ya fizge hannunsa, sai ga shi fari ga mãsu kallo.

34

قَالَ لِلْمَلَإِ حَوْلَهُۥٓ إِنَّ هَـٰذَا لَسَـٰحِرٌ عَلِيمٌۭ

qāla lil'mala-i ḥawlahu inna hādhā lasāḥirun ʿalīmun

(Fir'auna) ya ce ga mashãwarta a gẽfensa, "Lalle ne, wannan haƙĩƙa, masihirci ne, mai ilmi!

35

يُرِيدُ أَن يُخْرِجَكُم مِّنْ أَرْضِكُم بِسِحْرِهِۦ فَمَاذَا تَأْمُرُونَ

yurīdu an yukh'rijakum min arḍikum bisiḥ'rihi famādhā tamurūna

"Yanã son ya fitar da ku daga ƙasarku game da sihirinSa. To mẽne ne kuke shãwartãwa?"

36

قَالُوٓا۟ أَرْجِهْ وَأَخَاهُ وَٱبْعَثْ فِى ٱلْمَدَآئِنِ حَـٰشِرِينَ

qālū arjih wa-akhāhu wa-ib'ʿath fī l-madāini ḥāshirīna

Suka ce: "Ka jinkirtar da shi, shĩ da ɗan'uwansa, kuma ka aika mãsu gayya a cikin birãne."

37

يَأْتُوكَ بِكُلِّ سَحَّارٍ عَلِيمٍۢ

yatūka bikulli saḥḥārin ʿalīmin

"Zã su zõ maka da dukkan mai yawan sihiri masani."

38

فَجُمِعَ ٱلسَّحَرَةُ لِمِيقَـٰتِ يَوْمٍۢ مَّعْلُومٍۢ

fajumiʿa l-saḥaratu limīqāti yawmin maʿlūmin

Sai aka tãra masihirta dõmin ajalin yini sananne.

39

وَقِيلَ لِلنَّاسِ هَلْ أَنتُم مُّجْتَمِعُونَ

waqīla lilnnāsi hal antum muj'tamiʿūna

Kuma aka ce wa mutãne "Kõ kũ mãsu tãruwã ne?

40

لَعَلَّنَا نَتَّبِعُ ٱلسَّحَرَةَ إِن كَانُوا۟ هُمُ ٱلْغَـٰلِبِينَ

laʿallanā nattabiʿu l-saḥarata in kānū humu l-ghālibīna

"Tsammãninmu mu bi masihirta, idan sun kasance sũ ne marinjãya."

41

فَلَمَّا جَآءَ ٱلسَّحَرَةُ قَالُوا۟ لِفِرْعَوْنَ أَئِنَّ لَنَا لَأَجْرًا إِن كُنَّا نَحْنُ ٱلْغَـٰلِبِينَ

falammā jāa l-saḥaratu qālū lifir'ʿawna a-inna lanā la-ajran in kunnā naḥnu l-ghālibīna

To, a lõkacin da masihirta suka jẽ suka ce wa Fir'auna,"Shin, lalle ne, haƙĩƙa munã da ijãra idan mun kasance mũ ne marinjãya?"

42

قَالَ نَعَمْ وَإِنَّكُمْ إِذًۭا لَّمِنَ ٱلْمُقَرَّبِينَ

qāla naʿam wa-innakum idhan lamina l-muqarabīna

Ya ce: "Na'am! Kuma lalle ne, kũ ne a lõkacin haƙĩƙa muƙarrabai."

43

قَالَ لَهُم مُّوسَىٰٓ أَلْقُوا۟ مَآ أَنتُم مُّلْقُونَ

qāla lahum mūsā alqū mā antum mul'qūna

Mũsã ya ce musu, "Ku jẽfa abin da kuke mãsu jẽfãwa."

44

فَأَلْقَوْا۟ حِبَالَهُمْ وَعِصِيَّهُمْ وَقَالُوا۟ بِعِزَّةِ فِرْعَوْنَ إِنَّا لَنَحْنُ ٱلْغَـٰلِبُونَ

fa-alqaw ḥibālahum waʿiṣiyyahum waqālū biʿizzati fir'ʿawna innā lanaḥnu l-ghālibūna

Sai suka jẽfa igiyõyinsu, da sandunansu, kuma suka ce: "Da ƙarfin Fir'auna lalle ne mũ, haƙĩƙa, mũ ne marinjãya."

45

فَأَلْقَىٰ مُوسَىٰ عَصَاهُ فَإِذَا هِىَ تَلْقَفُ مَا يَأْفِكُونَ

fa-alqā mūsā ʿaṣāhu fa-idhā hiya talqafu mā yafikūna

Sai Mũsa ya jẽfa sandarsa, sai ga ta tanã harhaɗe abin da suke yi na ƙarya.

46

فَأُلْقِىَ ٱلسَّحَرَةُ سَـٰجِدِينَ

fa-ul'qiya l-saḥaratu sājidīna

Sai aka jẽfar da masihirta sunã mãsu sujada.

47

قَالُوٓا۟ ءَامَنَّا بِرَبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ

qālū āmannā birabbi l-ʿālamīna

Suka ce: "Mun yi ĩmãni da Ubangijin halitta."

48

رَبِّ مُوسَىٰ وَهَـٰرُونَ

rabbi mūsā wahārūna

"Ubangijin Mũsa da Hãrũna."

49

قَالَ ءَامَنتُمْ لَهُۥ قَبْلَ أَنْ ءَاذَنَ لَكُمْ ۖ إِنَّهُۥ لَكَبِيرُكُمُ ٱلَّذِى عَلَّمَكُمُ ٱلسِّحْرَ فَلَسَوْفَ تَعْلَمُونَ ۚ لَأُقَطِّعَنَّ أَيْدِيَكُمْ وَأَرْجُلَكُم مِّنْ خِلَـٰفٍۢ وَلَأُصَلِّبَنَّكُمْ أَجْمَعِينَ

qāla āmantum lahu qabla an ādhana lakum innahu lakabīrukumu alladhī ʿallamakumu l-siḥ'ra falasawfa taʿlamūna la-uqaṭṭiʿanna aydiyakum wa-arjulakum min khilāfin wala-uṣallibannakum ajmaʿīna

Ya ce: "Ashe, kun yi ĩmãni sabõda shĩ, a gabãnin in yi muku izni? Lalle ne shi, haƙĩƙa babbanku ne wanda ya kõya muku sihirin, to, zã ku sani. Lalle ne haƙĩƙa, zan kakkãtse hannuwanku da kafãfunku a tarnaƙi, kuma haƙĩƙa, zan tsĩrẽ ku gabã ɗaya."

50

قَالُوا۟ لَا ضَيْرَ ۖ إِنَّآ إِلَىٰ رَبِّنَا مُنقَلِبُونَ

qālū lā ḍayra innā ilā rabbinā munqalibūna

Suka ce: "Bãbu wata cũta! Lalle ne mũ mãsu jũyãwa ne zuwa ga Ubangijinmu."

51

إِنَّا نَطْمَعُ أَن يَغْفِرَ لَنَا رَبُّنَا خَطَـٰيَـٰنَآ أَن كُنَّآ أَوَّلَ ٱلْمُؤْمِنِينَ

innā naṭmaʿu an yaghfira lanā rabbunā khaṭāyānā an kunnā awwala l-mu'minīna

"Lalle ne mu munã kwaɗayin Ubangijinmu, Ya gãfarta mana kurakuranmu dõmin mun kasance farkon mãsu ĩmãni."

52

۞ وَأَوْحَيْنَآ إِلَىٰ مُوسَىٰٓ أَنْ أَسْرِ بِعِبَادِىٓ إِنَّكُم مُّتَّبَعُونَ

wa-awḥaynā ilā mūsā an asri biʿibādī innakum muttabaʿūna

Kuma Muka aika zuwa ga Mũsã cẽwa ka yi tafiyar dare da bãyiNa, lalle ne kũ waɗanda ake biyã1 ne.

53

فَأَرْسَلَ فِرْعَوْنُ فِى ٱلْمَدَآئِنِ حَـٰشِرِينَ

fa-arsala fir'ʿawnu fī l-madāini ḥāshirīna

Sai Fir'auna ya aika mãsu gayya a cikin birãne.

54

إِنَّ هَـٰٓؤُلَآءِ لَشِرْذِمَةٌۭ قَلِيلُونَ

inna hāulāi lashir'dhimatun qalīlūna

"Lalle ne, waɗannan, haƙĩƙa, ƙungiya ce kaɗan."

55

وَإِنَّهُمْ لَنَا لَغَآئِظُونَ

wa-innahum lanā laghāiẓūna

"Kuma lalle ne sũ, a gare Mu, Mãsu fusãtarwa ne."

56

وَإِنَّا لَجَمِيعٌ حَـٰذِرُونَ

wa-innā lajamīʿun ḥādhirūna

"Kuma lalle ne mũ haƙĩƙa gabã ɗaya mãsu sauna ne."

57

فَأَخْرَجْنَـٰهُم مِّن جَنَّـٰتٍۢ وَعُيُونٍۢ

fa-akhrajnāhum min jannātin waʿuyūnin

Sai Muka fitar da su daga gonaki da marẽmari.

58

وَكُنُوزٍۢ وَمَقَامٍۢ كَرِيمٍۢ

wakunūzin wamaqāmin karīmin

Da taskõki da mazauni mai kyau.

59

كَذَٰلِكَ وَأَوْرَثْنَـٰهَا بَنِىٓ إِسْرَٰٓءِيلَ

kadhālika wa-awrathnāhā banī is'rāīla

Kamar haka! Kuma Muka gãdar da su ga Banĩ Isrãĩla.

60

فَأَتْبَعُوهُم مُّشْرِقِينَ

fa-atbaʿūhum mush'riqīna

Sai suka bĩ su sunã mãsu fita a lõkacin hũdõwar rãnã.

61

فَلَمَّا تَرَٰٓءَا ٱلْجَمْعَانِ قَالَ أَصْحَـٰبُ مُوسَىٰٓ إِنَّا لَمُدْرَكُونَ

falammā tarāā l-jamʿāni qāla aṣḥābu mūsā innā lamud'rakūna

Sa'an nan a lõkacin da jama'a biyu suka ga jũna, sai abõkan Mũsã suka ce: "Lalle ne mũ haƙĩ ƙa, waɗanda ake riska ne."

62

قَالَ كَلَّآ ۖ إِنَّ مَعِىَ رَبِّى سَيَهْدِينِ

qāla kallā inna maʿiya rabbī sayahdīni

Ya ce: "Kayya! Lalle ne Ubangijina Yanã tare da ni, zai shiryar da ni."

63

فَأَوْحَيْنَآ إِلَىٰ مُوسَىٰٓ أَنِ ٱضْرِب بِّعَصَاكَ ٱلْبَحْرَ ۖ فَٱنفَلَقَ فَكَانَ كُلُّ فِرْقٍۢ كَٱلطَّوْدِ ٱلْعَظِيمِ

fa-awḥaynā ilā mūsā ani iḍ'rib biʿaṣāka l-baḥra fa-infalaqa fakāna kullu fir'qin kal-ṭawdi l-ʿaẓīmi

Sai Muka yi wahayi zuwa ga Mũsã cẽwa "Ka dõki tẽku da sandarka." Sai tẽku ta tsãge,1 kõwane tsãgi ya kasance kamar falalen dũtse mai girma.

64

وَأَزْلَفْنَا ثَمَّ ٱلْـَٔاخَرِينَ

wa-azlafnā thamma l-ākharīna

Kuma Muka kusantar da waɗansu mutãne a can.

65

وَأَنجَيْنَا مُوسَىٰ وَمَن مَّعَهُۥٓ أَجْمَعِينَ

wa-anjaynā mūsā waman maʿahu ajmaʿīna

Kuma Muka tsĩrar da Mũsã da waɗanda suke tãre da shi gabã ɗaya.

66

ثُمَّ أَغْرَقْنَا ٱلْـَٔاخَرِينَ

thumma aghraqnā l-ākharīna

Sa'an nan kuma Muka nutsar da waɗansu mutãnen.

67

إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَـَٔايَةًۭ ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ

inna fī dhālika laāyatan wamā kāna aktharuhum mu'minīna

Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba.

68

وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلْعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ

wa-inna rabbaka lahuwa l-ʿazīzu l-raḥīmu

Kuma lalle ne Ubangijinka, kaƙĩƙa, Shĩ ne Mabũwayi, Mai jin ƙai.

69

وَٱتْلُ عَلَيْهِمْ نَبَأَ إِبْرَٰهِيمَ

wa-ut'lu ʿalayhim naba-a ib'rāhīma

Kuma ka karanta, a kansu, lãbãrin Ibrãhĩm.

70

إِذْ قَالَ لِأَبِيهِ وَقَوْمِهِۦ مَا تَعْبُدُونَ

idh qāla li-abīhi waqawmihi mā taʿbudūna

A sã'ilin da ya ce wa ubansa da mutãnensa, "Mẽne ne kuke bauta wa?"

71

قَالُوا۟ نَعْبُدُ أَصْنَامًۭا فَنَظَلُّ لَهَا عَـٰكِفِينَ

qālū naʿbudu aṣnāman fanaẓallu lahā ʿākifīna

Suka ce: "Munã bauta wa gumãka, sabõda haka munã yini mãsu lazimta a gare su."

72

قَالَ هَلْ يَسْمَعُونَكُمْ إِذْ تَدْعُونَ

qāla hal yasmaʿūnakum idh tadʿūna

Ya ce: "Shin, sunã jin ku, a lõkacin da kuke kira?"

73

أَوْ يَنفَعُونَكُمْ أَوْ يَضُرُّونَ

aw yanfaʿūnakum aw yaḍurrūna

"Kõ kuwa sunã amfãnin ku, kõ sunã cũtar ku?"

74

قَالُوا۟ بَلْ وَجَدْنَآ ءَابَآءَنَا كَذَٰلِكَ يَفْعَلُونَ

qālū bal wajadnā ābāanā kadhālika yafʿalūna

Suka ce: "Ã'a mun sãmĩ ubanninmu, kamar haka ne suke aikatãwa."

75

قَالَ أَفَرَءَيْتُم مَّا كُنتُمْ تَعْبُدُونَ

qāla afara-aytum mā kuntum taʿbudūna

Ya ce: "Shin to, kun ga abin da kuka kasance kunã bautã wa?"

76

أَنتُمْ وَءَابَآؤُكُمُ ٱلْأَقْدَمُونَ

antum waābāukumu l-aqdamūna

"Kũ da ubanninku mafi daɗẽwa?"

77

فَإِنَّهُمْ عَدُوٌّۭ لِّىٓ إِلَّا رَبَّ ٱلْعَـٰلَمِينَ

fa-innahum ʿaduwwun lī illā rabba l-ʿālamīna

"To lalle ne, sũ maƙiya ne a gare ni, fãce Ubangijin halittu."

78

ٱلَّذِى خَلَقَنِى فَهُوَ يَهْدِينِ

alladhī khalaqanī fahuwa yahdīni

"Wanda Ya halitta ni, sa'an nan Yanã shiryar da ni."

79

وَٱلَّذِى هُوَ يُطْعِمُنِى وَيَسْقِينِ

wa-alladhī huwa yuṭ'ʿimunī wayasqīni

"Kuma Wanda Yake Shĩ ne Yake ciyar da ni, kuma Yanã shãyar da ni."

80

وَإِذَا مَرِضْتُ فَهُوَ يَشْفِينِ

wa-idhā mariḍ'tu fahuwa yashfīni

"Kuma idan na yi jiyya, to, Shĩ ne Yake warkar da ni."

81

وَٱلَّذِى يُمِيتُنِى ثُمَّ يُحْيِينِ

wa-alladhī yumītunī thumma yuḥ'yīni

"Kuma wanda Yake matar da ni, sa'an nan Ya rãyar da ni."

82

وَٱلَّذِىٓ أَطْمَعُ أَن يَغْفِرَ لِى خَطِيٓـَٔتِى يَوْمَ ٱلدِّينِ

wa-alladhī aṭmaʿu an yaghfira lī khaṭīatī yawma l-dīni

"Kuma wanda Yake inã kwaɗayin Ya gãfarta mini kurãkuraina, a rãnar sãkamako."

83

رَبِّ هَبْ لِى حُكْمًۭا وَأَلْحِقْنِى بِٱلصَّـٰلِحِينَ

rabbi hab lī ḥuk'man wa-alḥiq'nī bil-ṣāliḥīna

"Ya Ubangijĩna! Ka ba ni hukunci, kuma Ka riskar da ni ga sãlihai."

84

وَٱجْعَل لِّى لِسَانَ صِدْقٍۢ فِى ٱلْـَٔاخِرِينَ

wa-ij'ʿal lī lisāna ṣid'qin fī l-ākhirīna

"Kuma Ka sanya mini harshen gaskiya1 a cikin mutãnen ƙarshe."

85

وَٱجْعَلْنِى مِن وَرَثَةِ جَنَّةِ ٱلنَّعِيمِ

wa-ij'ʿalnī min warathati jannati l-naʿīmi

"Kuma Ka sanya ni daga magãdan Aljannar ni'ima."

86

وَٱغْفِرْ لِأَبِىٓ إِنَّهُۥ كَانَ مِنَ ٱلضَّآلِّينَ

wa-igh'fir li-abī innahu kāna mina l-ḍālīna

"Kuma Ka gãfarta wa ubãna, lalle ne shi, ya kasance daga ɓatattu."

87

وَلَا تُخْزِنِى يَوْمَ يُبْعَثُونَ

walā tukh'zinī yawma yub'ʿathūna

"Kuma kada Ka kunyata ni a rãnar da ake tãyar da su."

88

يَوْمَ لَا يَنفَعُ مَالٌۭ وَلَا بَنُونَ

yawma lā yanfaʿu mālun walā banūna

"A rãnar da dũkiya bã ta amfãni, kuma ɗiya bã su yi."

89

إِلَّا مَنْ أَتَى ٱللَّهَ بِقَلْبٍۢ سَلِيمٍۢ

illā man atā l-laha biqalbin salīmin

"Fãce wanda ya jẽ wa Allah da zũciya mai tsarki."

90

وَأُزْلِفَتِ ٱلْجَنَّةُ لِلْمُتَّقِينَ

wa-uz'lifati l-janatu lil'muttaqīna

Kuma aka kusantar da Aljanna ga mãsu taƙawa.

91

وَبُرِّزَتِ ٱلْجَحِيمُ لِلْغَاوِينَ

waburrizati l-jaḥīmu lil'ghāwīna

Kuma aka fitar da wutã babba dõmin halakakku.

92

وَقِيلَ لَهُمْ أَيْنَ مَا كُنتُمْ تَعْبُدُونَ

waqīla lahum ayna mā kuntum taʿbudūna

Kuma aka ce musu, "Inã abin da kuka kasance kunã bautawa?"

93

مِن دُونِ ٱللَّهِ هَلْ يَنصُرُونَكُمْ أَوْ يَنتَصِرُونَ

min dūni l-lahi hal yanṣurūnakum aw yantaṣirūna

"Baicin Allah? Shin sunã tamakon ku kõ kuwa sunã tsare kansu?"

94

فَكُبْكِبُوا۟ فِيهَا هُمْ وَٱلْغَاوُۥنَ

fakub'kibū fīhā hum wal-ghāwūna

Sai aka kikkife su1 a cikinta, su da halakakkun.

95

وَجُنُودُ إِبْلِيسَ أَجْمَعُونَ

wajunūdu ib'līsa ajmaʿūna

Da rundunar Ibilĩsa gabã ɗaya.

96

قَالُوا۟ وَهُمْ فِيهَا يَخْتَصِمُونَ

qālū wahum fīhā yakhtaṣimūna

Suka ce: alhãli sunã a cikinta sunã yin husũma,

97

تَٱللَّهِ إِن كُنَّا لَفِى ضَلَـٰلٍۢ مُّبِينٍ

tal-lahi in kunnā lafī ḍalālin mubīnin

"Rantsuwa da Allah! Lalle ne mun kasance, haƙĩƙa, a cikin ɓata bayyananna."

98

إِذْ نُسَوِّيكُم بِرَبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ

idh nusawwīkum birabbi l-ʿālamīna

"A lõkacin da muke daidaita ku da Ubangijin halittu.

99

وَمَآ أَضَلَّنَآ إِلَّا ٱلْمُجْرِمُونَ

wamā aḍallanā illā l-muj'rimūna

"Kuma bãbu abin da ya ɓatar da mu fãce mãsu laifi."

100

فَمَا لَنَا مِن شَـٰفِعِينَ

famā lanā min shāfiʿīna

"Sabõda haka bã mu da waɗansu macẽta."

101

وَلَا صَدِيقٍ حَمِيمٍۢ

walā ṣadīqin ḥamīmin

"Kuma bã mu da abõki, masõyi."

102

فَلَوْ أَنَّ لَنَا كَرَّةًۭ فَنَكُونَ مِنَ ٱلْمُؤْمِنِينَ

falaw anna lanā karratan fanakūna mina l-mu'minīna

"Sabõda haka dã lalle munã da (dãmar) kõmawa, dõmin mu kasance daga mũminai!"

103

إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَـَٔايَةًۭ ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ

inna fī dhālika laāyatan wamā kāna aktharuhum mu'minīna

Lalle ne, a cikin wancan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, bã su kasance mũminai ba.

104

وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلْعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ

wa-inna rabbaka lahuwa l-ʿazīzu l-raḥīmu

Kuma lalle ne, Ubangijinka, Shi ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.

105

كَذَّبَتْ قَوْمُ نُوحٍ ٱلْمُرْسَلِينَ

kadhabat qawmu nūḥin l-mur'salīna

Mutãnen Nũhu sun ƙaryata Manzanni.

106

إِذْ قَالَ لَهُمْ أَخُوهُمْ نُوحٌ أَلَا تَتَّقُونَ

idh qāla lahum akhūhum nūḥun alā tattaqūna

A lõkacin da Dan uwansu Nuhu ya ce musu, "Bã zã ku ji tsoron Allah ba?"

107

إِنِّى لَكُمْ رَسُولٌ أَمِينٌۭ

innī lakum rasūlun amīnun

"Lalle ne, zuwa gare ku, ni Manzo ne amintacce."

108

فَٱتَّقُوا۟ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ

fa-ittaqū l-laha wa-aṭīʿūni

"To, ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."

109

وَمَآ أَسْـَٔلُكُمْ عَلَيْهِ مِنْ أَجْرٍ ۖ إِنْ أَجْرِىَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ

wamā asalukum ʿalayhi min ajrin in ajriya illā ʿalā rabbi l-ʿālamīna

"Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrãtã ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu."

110

فَٱتَّقُوا۟ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ

fa-ittaqū l-laha wa-aṭīʿūni

"Sabõda haka, ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."

111

۞ قَالُوٓا۟ أَنُؤْمِنُ لَكَ وَٱتَّبَعَكَ ٱلْأَرْذَلُونَ

qālū anu'minu laka wa-ittabaʿaka l-ardhalūna

Suka ce: "Ashe, zã mu yi ĩmãni sabõda kai alhãli kuwa mafiya ƙasƙanci sun bi ka?"

112

قَالَ وَمَا عِلْمِى بِمَا كَانُوا۟ يَعْمَلُونَ

qāla wamā ʿil'mī bimā kānū yaʿmalūna

Ya ce: "Kuma bã ni da sani ga abin da suka kasance sanã aikatãwa."

113

إِنْ حِسَابُهُمْ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّى ۖ لَوْ تَشْعُرُونَ

in ḥisābuhum illā ʿalā rabbī law tashʿurūna

"Hisãbinsu bai zama ba fãce ga Ubangijina, dã kunã sansancẽwa."

114

وَمَآ أَنَا۠ بِطَارِدِ ٱلْمُؤْمِنِينَ

wamā anā biṭāridi l-mu'minīna

"Ban zama mai kõre mũminai ba."

115

إِنْ أَنَا۠ إِلَّا نَذِيرٌۭ مُّبِينٌۭ

in anā illā nadhīrun mubīnun

"Nĩ ba kõwa ba ne sai mai gargaɗi mai bayyanãwa."

116

قَالُوا۟ لَئِن لَّمْ تَنتَهِ يَـٰنُوحُ لَتَكُونَنَّ مِنَ ٱلْمَرْجُومِينَ

qālū la-in lam tantahi yānūḥu latakūnanna mina l-marjūmīna

Suka ce: "Lalle ne, idan ba ka hanu ba, yã Nũhu, (daga maganarka,) haƙĩƙa, kanã kasancẽwa daga waɗanda ake jẽfewa"

117

قَالَ رَبِّ إِنَّ قَوْمِى كَذَّبُونِ

qāla rabbi inna qawmī kadhabūni

Ya ce: "Yã Ubangijĩna! Lalle ne mutãnena sun ƙaryatã ni."

118

فَٱفْتَحْ بَيْنِى وَبَيْنَهُمْ فَتْحًۭا وَنَجِّنِى وَمَن مَّعِىَ مِنَ ٱلْمُؤْمِنِينَ

fa-if'taḥ baynī wabaynahum fatḥan wanajjinī waman maʿiya mina l-mu'minīna

"Sai ka yi hukunci, a tsakãnĩna da tsakãninsu tabbataccen hukanci, kuma ka tsĩrar da ni, da waɗanda suke tãre da ni daga mũminai."

119

فَأَنجَيْنَـٰهُ وَمَن مَّعَهُۥ فِى ٱلْفُلْكِ ٱلْمَشْحُونِ

fa-anjaynāhu waman maʿahu fī l-ful'ki l-mashḥūni

Sai Muka tsĩrar da shi, shi da waɗanda suke tãre da shi, a cikin jirgi wanda aka yi wa lõdi.

120

ثُمَّ أَغْرَقْنَا بَعْدُ ٱلْبَاقِينَ

thumma aghraqnā baʿdu l-bāqīna

Sa'an nan Muka nutsar a bãyan haka, da sauran.

121

إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَـَٔايَةًۭ ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ

inna fī dhālika laāyatan wamā kāna aktharuhum mu'minīna

Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, ba su kasance mãsu ĩmãni ba.

122

وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلْعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ

wa-inna rabbaka lahuwa l-ʿazīzu l-raḥīmu

Kuma Lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai Rahama.

123

كَذَّبَتْ عَادٌ ٱلْمُرْسَلِينَ

kadhabat ʿādun l-mur'salīna

Ãdãwa sun ƙaryata Manzanni.

124

إِذْ قَالَ لَهُمْ أَخُوهُمْ هُودٌ أَلَا تَتَّقُونَ

idh qāla lahum akhūhum hūdun alā tattaqūna

A lõkacin da ɗan'uwansu, Hũdu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"

125

إِنِّى لَكُمْ رَسُولٌ أَمِينٌۭ

innī lakum rasūlun amīnun

"Lalle ne ni, zuwa gare ku, haƙĩƙa, Manzo ne, amintacce."

126

فَٱتَّقُوا۟ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ

fa-ittaqū l-laha wa-aṭīʿūni

"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."

127

وَمَآ أَسْـَٔلُكُمْ عَلَيْهِ مِنْ أَجْرٍ ۖ إِنْ أَجْرِىَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ

wamā asalukum ʿalayhi min ajrin in ajriya illā ʿalā rabbi l-ʿālamīna

"Kuma bã ni tambayar wata ijãra a kansa. Ijãrãta ba ta zama ba, fãce daga Ubangijin halittu."

128

أَتَبْنُونَ بِكُلِّ رِيعٍ ءَايَةًۭ تَعْبَثُونَ

atabnūna bikulli rīʿin āyatan taʿbathūna

"Shin, kunã yin ginin sitadiyo1 a kõwane tsauni ne, kunã yin wãsa?"

129

وَتَتَّخِذُونَ مَصَانِعَ لَعَلَّكُمْ تَخْلُدُونَ

watattakhidhūna maṣāniʿa laʿallakum takhludūna

"Kuma kunã riƙon matsãrar ruwa, tsammãninku, ku dawwama?1"

130

وَإِذَا بَطَشْتُم بَطَشْتُمْ جَبَّارِينَ

wa-idhā baṭashtum baṭashtum jabbārīna

"Kuma idan kun yi damƙa, sai ku yi damƙar kunã mãsu tanƙwasãwa."

131

فَٱتَّقُوا۟ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ

fa-ittaqū l-laha wa-aṭīʿūni

"To ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."

132

وَٱتَّقُوا۟ ٱلَّذِىٓ أَمَدَّكُم بِمَا تَعْلَمُونَ

wa-ittaqū alladhī amaddakum bimā taʿlamūna

"Ku ji tsõron wanda Ya taimake ku da abin da kuka sani."

133

أَمَدَّكُم بِأَنْعَـٰمٍۢ وَبَنِينَ

amaddakum bi-anʿāmin wabanīna

"Ya taimake ku da dabbõbin ni'ima da ɗiya."

134

وَجَنَّـٰتٍۢ وَعُيُونٍ

wajannātin waʿuyūnin

"Da gõnaki da marẽmari."

135

إِنِّىٓ أَخَافُ عَلَيْكُمْ عَذَابَ يَوْمٍ عَظِيمٍۢ

innī akhāfu ʿalaykum ʿadhāba yawmin ʿaẓīmin

"Lalle ne nĩ, inã ji muku tsõron azãbar wani yini mai girma."

136

قَالُوا۟ سَوَآءٌ عَلَيْنَآ أَوَعَظْتَ أَمْ لَمْ تَكُن مِّنَ ٱلْوَٰعِظِينَ

qālū sawāon ʿalaynā awaʿaẓta am lam takun mina l-wāʿiẓīna

Suka ce: "Daidai ne a kanmu: Kã yi wa'azi kõ ba ka kasance daga mãsu wa'azi ba."

137

إِنْ هَـٰذَآ إِلَّا خُلُقُ ٱلْأَوَّلِينَ

in hādhā illā khuluqu l-awalīna

"Wannan abu bai zamõ ba fãce hãlãyen1 mutãnen farko."

138

وَمَا نَحْنُ بِمُعَذَّبِينَ

wamā naḥnu bimuʿadhabīna

"Kuma mũ ba mu zama waɗanda ake yi wa azãba ba."

139

فَكَذَّبُوهُ فَأَهْلَكْنَـٰهُمْ ۗ إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَـَٔايَةًۭ ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ

fakadhabūhu fa-ahlaknāhum inna fī dhālika laāyatan wamā kāna aktharuhum mu'minīna

Sabõda haka suka ƙaryata shi, sai Muka halakar da sũ. Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba.

140

وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلْعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ

wa-inna rabbaka lahuwa l-ʿazīzu l-raḥīmu

Kuma lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shi ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.

141

كَذَّبَتْ ثَمُودُ ٱلْمُرْسَلِينَ

kadhabat thamūdu l-mur'salīna

Samũdãwa sun ƙaryata Manzanni.

142

إِذْ قَالَ لَهُمْ أَخُوهُمْ صَـٰلِحٌ أَلَا تَتَّقُونَ

idh qāla lahum akhūhum ṣāliḥun alā tattaqūna

A lõkacin da ɗan'uwansu Sãlihu ya ce: "Shin, bã zã ku bi Allah da taƙawa ba?"

143

إِنِّى لَكُمْ رَسُولٌ أَمِينٌۭ

innī lakum rasūlun amīnun

"Lalle ne nĩ zuwã gare ku, Manzo ne, amintacce."

144

فَٱتَّقُوا۟ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ

fa-ittaqū l-laha wa-aṭīʿūni

"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã.

145

وَمَآ أَسْـَٔلُكُمْ عَلَيْهِ مِنْ أَجْرٍ ۖ إِنْ أَجْرِىَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ

wamā asalukum ʿalayhi min ajrin in ajriya illā ʿalā rabbi l-ʿālamīna

"Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrãta ba ta zama ba fãce da a Ubangijin halittu."

146

أَتُتْرَكُونَ فِى مَا هَـٰهُنَآ ءَامِنِينَ

atut'rakūna fī mā hāhunā āminīna

"Shin, anã barin ku1 a cikin abin da yake a nan, kunã amintattu?"

147

فِى جَنَّـٰتٍۢ وَعُيُونٍۢ

fī jannātin waʿuyūnin

"A cikin gõnaki da marẽmari."

148

وَزُرُوعٍۢ وَنَخْلٍۢ طَلْعُهَا هَضِيمٌۭ

wazurūʿin wanakhlin ṭalʿuhā haḍīmun

"Da shuke-shuke da dabĩ nai, 'ya'yan itãcensu hirtsi1 mãsu narkẽwa a ciki?"

149

وَتَنْحِتُونَ مِنَ ٱلْجِبَالِ بُيُوتًۭا فَـٰرِهِينَ

watanḥitūna mina l-jibāli buyūtan fārihīna

"Kuma kunã sassaƙa gidãje daga duwãtsu, kunã mãsu alfãhari?"

150

فَٱتَّقُوا۟ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ

fa-ittaqū l-laha wa-aṭīʿūni

"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."

151

وَلَا تُطِيعُوٓا۟ أَمْرَ ٱلْمُسْرِفِينَ

walā tuṭīʿū amra l-mus'rifīna

"Kada ku yi ɗã'ã ga umurnin maɓarnata."

152

ٱلَّذِينَ يُفْسِدُونَ فِى ٱلْأَرْضِ وَلَا يُصْلِحُونَ

alladhīna yuf'sidūna fī l-arḍi walā yuṣ'liḥūna

"Waɗanda suke yin ɓarna a cikin ƙasa, kuma bã su kyautatãwa."

153

قَالُوٓا۟ إِنَّمَآ أَنتَ مِنَ ٱلْمُسَحَّرِينَ

qālū innamā anta mina l-musaḥarīna

Suka ce: "Kai daga mãsu sihiri kurum kake."

154

مَآ أَنتَ إِلَّا بَشَرٌۭ مِّثْلُنَا فَأْتِ بِـَٔايَةٍ إِن كُنتَ مِنَ ٱلصَّـٰدِقِينَ

mā anta illā basharun mith'lunā fati biāyatin in kunta mina l-ṣādiqīna

"Bã kõwa kake ba, fãce mutum kamarmu. To, kã zo da wata ãyã idan kã kasance daga mãsu gaskiya."

155

قَالَ هَـٰذِهِۦ نَاقَةٌۭ لَّهَا شِرْبٌۭ وَلَكُمْ شِرْبُ يَوْمٍۢ مَّعْلُومٍۢ

qāla hādhihi nāqatun lahā shir'bun walakum shir'bu yawmin maʿlūmin

Ya ce: "Wannan rãkuma ce tanã da shan1 yini, kuma kunã da shan yini sasanne."

156

وَلَا تَمَسُّوهَا بِسُوٓءٍۢ فَيَأْخُذَكُمْ عَذَابُ يَوْمٍ عَظِيمٍۢ

walā tamassūhā bisūin fayakhudhakum ʿadhābu yawmin ʿaẓīmin

"Kada ku shãfe ta da cũta har azãbar yini mai girmã ta shãfe ku."

157

فَعَقَرُوهَا فَأَصْبَحُوا۟ نَـٰدِمِينَ

faʿaqarūhā fa-aṣbaḥū nādimīna

Sai suka sõke ta sa'an nan suka wãyi gari sunã mãsu nadãma.

158

فَأَخَذَهُمُ ٱلْعَذَابُ ۗ إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَـَٔايَةًۭ ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ

fa-akhadhahumu l-ʿadhābu inna fī dhālika laāyatan wamā kāna aktharuhum mu'minīna

Sabõda haka azãba ta kãma su. Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, ba su kasance mãsu ĩmãni ba.

159

وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلْعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ

wa-inna rabbaka lahuwa l-ʿazīzu l-raḥīmu

Lalle ne Ubangijinka, haƙĩ ƙa, Shĩ ne Mabuwayi, Mai jin ƙai.

160

كَذَّبَتْ قَوْمُ لُوطٍ ٱلْمُرْسَلِينَ

kadhabat qawmu lūṭin l-mur'salīna

Mutãnen Lũɗu sun ƙaryata Manzanni.

161

إِذْ قَالَ لَهُمْ أَخُوهُمْ لُوطٌ أَلَا تَتَّقُونَ

idh qāla lahum akhūhum lūṭun alā tattaqūna

A lõkacin da ɗan'uwansu,1 Lũɗu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"

162

إِنِّى لَكُمْ رَسُولٌ أَمِينٌۭ

innī lakum rasūlun amīnun

"Lalle ne nĩ, zuwa gare ku, Manzõ ne, amintacce."

163

فَٱتَّقُوا۟ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ

fa-ittaqū l-laha wa-aṭīʿūni

"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."

164

وَمَآ أَسْـَٔلُكُمْ عَلَيْهِ مِنْ أَجْرٍ ۖ إِنْ أَجْرِىَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ

wamā asalukum ʿalayhi min ajrin in ajriya illā ʿalā rabbi l-ʿālamīna

"Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra, Ijãrãta ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu."

165

أَتَأْتُونَ ٱلذُّكْرَانَ مِنَ ٱلْعَـٰلَمِينَ

atatūna l-dhuk'rāna mina l-ʿālamīna

"Shin kunã jẽ wa maza daga cikin talikai?"

166

وَتَذَرُونَ مَا خَلَقَ لَكُمْ رَبُّكُم مِّنْ أَزْوَٰجِكُم ۚ بَلْ أَنتُمْ قَوْمٌ عَادُونَ

watadharūna mā khalaqa lakum rabbukum min azwājikum bal antum qawmun ʿādūna

"Kuma kunã barin abin da Ubangijinku Ya halitta muku daga mãtanku? Ã'a, ku mutãne ne mãsu ƙẽtarẽwa!"

167

قَالُوا۟ لَئِن لَّمْ تَنتَهِ يَـٰلُوطُ لَتَكُونَنَّ مِنَ ٱلْمُخْرَجِينَ

qālū la-in lam tantahi yālūṭu latakūnanna mina l-mukh'rajīna

Suka ce: "Lalle ne haƙĩƙa idan ba ka hanu ba, yã Lũɗu! Tĩlas ne kanã kasancẽwa daga waɗanda ake fitarwa (daga gari)."

168

قَالَ إِنِّى لِعَمَلِكُم مِّنَ ٱلْقَالِينَ

qāla innī liʿamalikum mina l-qālīna

Ya ce: "Lalle ne ga aikinku, haƙĩƙa, inã daga mãsu ƙinsa."

169

رَبِّ نَجِّنِى وَأَهْلِى مِمَّا يَعْمَلُونَ

rabbi najjinī wa-ahlī mimmā yaʿmalūna

"Ya Ubangijina! Ka tsĩrar da ni da iyãlĩna daga abin da suke aikatãwa."

170

فَنَجَّيْنَـٰهُ وَأَهْلَهُۥٓ أَجْمَعِينَ

fanajjaynāhu wa-ahlahu ajmaʿīna

Sabõda haka Muka tsĩrar da shi, Shi da mutãnensa gabã ɗaya.

171

إِلَّا عَجُوزًۭا فِى ٱلْغَـٰبِرِينَ

illā ʿajūzan fī l-ghābirīna

Fãce wata tsõhuwa a cikin mãsu wanzuwa.

172

ثُمَّ دَمَّرْنَا ٱلْـَٔاخَرِينَ

thumma dammarnā l-ākharīna

Sa'an nan kuma Muka hallaka wasu.

173

وَأَمْطَرْنَا عَلَيْهِم مَّطَرًۭا ۖ فَسَآءَ مَطَرُ ٱلْمُنذَرِينَ

wa-amṭarnā ʿalayhim maṭaran fasāa maṭaru l-mundharīna

Kuma Muka yi ruwan sama a kansu ruwa, sai dai ruwan waɗanda ake yi wa gargaɗi ya mũnana.

174

إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَـَٔايَةًۭ ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ

inna fī dhālika laāyatan wamā kāna aktharuhum mu'minīna

Lalle ne ga wannan, akwai ãyã, kuma mafi yawansu bã su kasance mãsu ĩmãni ba.

175

وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلْعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ

wa-inna rabbaka lahuwa l-ʿazīzu l-raḥīmu

Kuma lalle ne Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.

176

كَذَّبَ أَصْحَـٰبُ لْـَٔيْكَةِ ٱلْمُرْسَلِينَ

kadhaba aṣḥābu al'aykati l-mur'salīna

Ma'abũta ƙunci sun ƙaryata Manzanni.

177

إِذْ قَالَ لَهُمْ شُعَيْبٌ أَلَا تَتَّقُونَ

idh qāla lahum shuʿaybun alā tattaqūna

A lõkacin da Shu'aibu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"

178

إِنِّى لَكُمْ رَسُولٌ أَمِينٌۭ

innī lakum rasūlun amīnun

"Lalle ne ni, zuwa gare ku, Manzo ne, amintacce."

179

فَٱتَّقُوا۟ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ

fa-ittaqū l-laha wa-aṭīʿūni

"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa kuma ku yi mini ɗã'ã."

180

وَمَآ أَسْـَٔلُكُمْ عَلَيْهِ مِنْ أَجْرٍ ۖ إِنْ أَجْرِىَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ

wamā asalukum ʿalayhi min ajrin in ajriya illā ʿalā rabbi l-ʿālamīna

"Kuma ba ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrata ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu."

181

۞ أَوْفُوا۟ ٱلْكَيْلَ وَلَا تَكُونُوا۟ مِنَ ٱلْمُخْسِرِينَ

awfū l-kayla walā takūnū mina l-mukh'sirīna

"Ku cika mũdu, kuma kada ku kasance daga mãsu sanyãwar hasãra (ga mutãne)."

182

وَزِنُوا۟ بِٱلْقِسْطَاسِ ٱلْمُسْتَقِيمِ

wazinū bil-qis'ṭāsi l-mus'taqīmi

"Kuma ku yi awo da sikẽli daidaitacce."

183

وَلَا تَبْخَسُوا۟ ٱلنَّاسَ أَشْيَآءَهُمْ وَلَا تَعْثَوْا۟ فِى ٱلْأَرْضِ مُفْسِدِينَ

walā tabkhasū l-nāsa ashyāahum walā taʿthaw fī l-arḍi muf'sidīna

"Kuma kada ku nakasa wa mutãne abũbuwansu kuma kada ku yi fasãdi a cikin ƙasa kuna mãsu ɓarna."

184

وَٱتَّقُوا۟ ٱلَّذِى خَلَقَكُمْ وَٱلْجِبِلَّةَ ٱلْأَوَّلِينَ

wa-ittaqū alladhī khalaqakum wal-jibilata l-awalīna

"Kuma ku ji tsõron Allah wanda Ya halitta ku, kũ da jama'ar farko."

185

قَالُوٓا۟ إِنَّمَآ أَنتَ مِنَ ٱلْمُسَحَّرِينَ

qālū innamā anta mina l-musaḥarīna

Suka ce: "Kai dai daga waɗanda suke sihirtattu kawai ne."

186

وَمَآ أَنتَ إِلَّا بَشَرٌۭ مِّثْلُنَا وَإِن نَّظُنُّكَ لَمِنَ ٱلْكَـٰذِبِينَ

wamā anta illā basharun mith'lunā wa-in naẓunnuka lamina l-kādhibīna

"Kuma bã kõwa kake ba, fãce mutum kamarmu kuma lalle ne munã zaton ka, haƙĩƙa, daga maƙaryata."

187

فَأَسْقِطْ عَلَيْنَا كِسَفًۭا مِّنَ ٱلسَّمَآءِ إِن كُنتَ مِنَ ٱلصَّـٰدِقِينَ

fa-asqiṭ ʿalaynā kisafan mina l-samāi in kunta mina l-ṣādiqīna

"To ka jẽfo wani ɓaɓɓake daga sama a kanmu, idan ka kasance daga mãsu gaskiya."

188

قَالَ رَبِّىٓ أَعْلَمُ بِمَا تَعْمَلُونَ

qāla rabbī aʿlamu bimā taʿmalūna

Ya ce: "Ubangijĩna ne Mafi sani ga abin da kuke aikatãwa."

189

فَكَذَّبُوهُ فَأَخَذَهُمْ عَذَابُ يَوْمِ ٱلظُّلَّةِ ۚ إِنَّهُۥ كَانَ عَذَابَ يَوْمٍ عَظِيمٍ

fakadhabūhu fa-akhadhahum ʿadhābu yawmi l-ẓulati innahu kāna ʿadhāba yawmin ʿaẓīmin

Sai suka ƙaiyatã shi, sabõda haka, azãbar rãnar girgije1 ta kãma su. Lalle ne ita, tã kasance azãbar yini mai girma.

190

إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَـَٔايَةًۭ ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ

inna fī dhālika laāyatan wamā kāna aktharuhum mu'minīna

Lalle a cikin wancan haƙĩka akwai ãya, amma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba.

191

وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلْعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ

wa-inna rabbaka lahuwa l-ʿazīzu l-raḥīmu

Kuma lalle Ubangijĩnka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.

192

وَإِنَّهُۥ لَتَنزِيلُ رَبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ

wa-innahu latanzīlu rabbi l-ʿālamīna

Kuma lalle shi (Alƙur'ãni), haƙĩƙa, saukarwar Ubangijinhalittu ne.

193

نَزَلَ بِهِ ٱلرُّوحُ ٱلْأَمِينُ

nazala bihi l-rūḥu l-amīnu

Rũhi1 amintacce ne ya sauka da shi.

194

عَلَىٰ قَلْبِكَ لِتَكُونَ مِنَ ٱلْمُنذِرِينَ

ʿalā qalbika litakūna mina l-mundhirīna

A kan zũciyarka, dõmin ka kasance daga mãsu gargaɗi.

195

بِلِسَانٍ عَرَبِىٍّۢ مُّبِينٍۢ

bilisānin ʿarabiyyin mubīnin

Da harshe na Larabci mai bayãni.

196

وَإِنَّهُۥ لَفِى زُبُرِ ٱلْأَوَّلِينَ

wa-innahu lafī zuburi l-awalīna

Kuma lalle shin, haƙĩƙa, yanã a cikin litattafan (Manzannin) farko.

197

أَوَلَمْ يَكُن لَّهُمْ ءَايَةً أَن يَعْلَمَهُۥ عُلَمَـٰٓؤُا۟ بَنِىٓ إِسْرَٰٓءِيلَ

awalam yakun lahum āyatan an yaʿlamahu ʿulamāu banī is'rāīla

Ashe, bai kasance ãyã ba a gare su, ya zama Mãlaman Banĩ Isrã'ĩla sun san shi?

198

وَلَوْ نَزَّلْنَـٰهُ عَلَىٰ بَعْضِ ٱلْأَعْجَمِينَ

walaw nazzalnāhu ʿalā baʿḍi l-aʿjamīna

Kuma dã mun saukar da shi a kan sãshen Ajamãwa,

199

فَقَرَأَهُۥ عَلَيْهِم مَّا كَانُوا۟ بِهِۦ مُؤْمِنِينَ

faqara-ahu ʿalayhim mā kānū bihi mu'minīna

Ya karanta shi a kansu, ba su kasance sabõda shi mãsu ĩmãni ba.

200

كَذَٰلِكَ سَلَكْنَـٰهُ فِى قُلُوبِ ٱلْمُجْرِمِينَ

kadhālika salaknāhu fī qulūbi l-muj'rimīna

Kamar wancan ne! Muka shigar da shi a cikin zukãtan mãsu laifi.

201

لَا يُؤْمِنُونَ بِهِۦ حَتَّىٰ يَرَوُا۟ ٱلْعَذَابَ ٱلْأَلِيمَ

lā yu'minūna bihi ḥattā yarawū l-ʿadhāba l-alīma

Bã zã su yi ĩmãni da shĩ ba sai sun ga azãbar nan mai raɗadi.

202

فَيَأْتِيَهُم بَغْتَةًۭ وَهُمْ لَا يَشْعُرُونَ

fayatiyahum baghtatan wahum lā yashʿurūna

Sai ta taho musu kwatsam, alhãli kuwa sũ, ba su sansance ba.

203

فَيَقُولُوا۟ هَلْ نَحْنُ مُنظَرُونَ

fayaqūlū hal naḥnu munẓarūna

Sai su ce: "Shin, mu waɗanda ake yi wa jinkiri ne?"

204

أَفَبِعَذَابِنَا يَسْتَعْجِلُونَ

afabiʿadhābinā yastaʿjilūna

Ashe, to, da azãbar Mu suke nẽman gaggãwa?

205

أَفَرَءَيْتَ إِن مَّتَّعْنَـٰهُمْ سِنِينَ

afara-ayta in mattaʿnāhum sinīna

Ashe, to, kã gani, idan Muka jĩshe su daɗi a shẽkaru,

206

ثُمَّ جَآءَهُم مَّا كَانُوا۟ يُوعَدُونَ

thumma jāahum mā kānū yūʿadūna

Sa'an nan abin da suka kasance anã yi musu wa'adi (da shi) ya jẽ musu,

207

مَآ أَغْنَىٰ عَنْهُم مَّا كَانُوا۟ يُمَتَّعُونَ

mā aghnā ʿanhum mā kānū yumattaʿūna

Abin da suka kasance anã jĩshe su dãɗin bã zai tunkuɗe azãba ba daga gare1 su.

208

وَمَآ أَهْلَكْنَا مِن قَرْيَةٍ إِلَّا لَهَا مُنذِرُونَ

wamā ahlaknā min qaryatin illā lahā mundhirūna

Kuma bã Mu halakar da wata alƙarya ba fãce tanã da mãsu gargaɗi.

209

ذِكْرَىٰ وَمَا كُنَّا ظَـٰلِمِينَ

dhik'rā wamā kunnā ẓālimīna

Dõmin tunãtarwa, kuma ba Mu kasance Mãsu zãlunci ba.

210

وَمَا تَنَزَّلَتْ بِهِ ٱلشَّيَـٰطِينُ

wamā tanazzalat bihi l-shayāṭīnu

Kuma (Alƙur'ãni) Shaiɗãnu ba su ɗõra sauka da shĩba.

211

وَمَا يَنۢبَغِى لَهُمْ وَمَا يَسْتَطِيعُونَ

wamā yanbaghī lahum wamā yastaṭīʿūna

Kuma bã ya kamãta a gare su (su Shaiɗãnu su sauka da shi), kuma ba su iyãwa.

212

إِنَّهُمْ عَنِ ٱلسَّمْعِ لَمَعْزُولُونَ

innahum ʿani l-samʿi lamaʿzūlūna

Lalle ne sũ, daga saurãre, haƙĩƙa, waɗanda aka nĩsantar ne.

213

فَلَا تَدْعُ مَعَ ٱللَّهِ إِلَـٰهًا ءَاخَرَ فَتَكُونَ مِنَ ٱلْمُعَذَّبِينَ

falā tadʿu maʿa l-lahi ilāhan ākhara fatakūna mina l-muʿadhabīna

Sabõda haka, kada ka kira wani abin bautãwa na dabam tãre da Allah, sai ka kasance daga waɗanda ake yi wa azãba.

214

وَأَنذِرْ عَشِيرَتَكَ ٱلْأَقْرَبِينَ

wa-andhir ʿashīrataka l-aqrabīna

Kuma ka yi gargaɗi ga danginka mafiya kusanci.

215

وَٱخْفِضْ جَنَاحَكَ لِمَنِ ٱتَّبَعَكَ مِنَ ٱلْمُؤْمِنِينَ

wa-ikh'fiḍ janāḥaka limani ittabaʿaka mina l-mu'minīna

Kuma ka sassauta fikãfikanka1 ga wanda ya bĩ ka daga mũminai.

216

فَإِنْ عَصَوْكَ فَقُلْ إِنِّى بَرِىٓءٌۭ مِّمَّا تَعْمَلُونَ

fa-in ʿaṣawka faqul innī barīon mimmā taʿmalūna

Sa'an nan idan suka sãɓã maka to ka ce: "Lalle nĩ, barrantacce ne daga abin da kuko aikatãwa."

217

وَتَوَكَّلْ عَلَى ٱلْعَزِيزِ ٱلرَّحِيمِ

watawakkal ʿalā l-ʿazīzi l-raḥīmi

Kuma ka dõgara ga Mabuwãyi, Mai jin ƙai.

218

ٱلَّذِى يَرَىٰكَ حِينَ تَقُومُ

alladhī yarāka ḥīna taqūmu

Wanda Yake ganin ka a lõkacin da kake tãshi tsaye.

219

وَتَقَلُّبَكَ فِى ٱلسَّـٰجِدِينَ

wataqallubaka fī l-sājidīna

Da jujjuyãwarka a cikin mãsu yin sujada.

220

إِنَّهُۥ هُوَ ٱلسَّمِيعُ ٱلْعَلِيمُ

innahu huwa l-samīʿu l-ʿalīmu

Lalle Shi, Shi1 ne Mai ji, Masani.

221

هَلْ أُنَبِّئُكُمْ عَلَىٰ مَن تَنَزَّلُ ٱلشَّيَـٰطِينُ

hal unabbi-ukum ʿalā man tanazzalu l-shayāṭīnu

Shin, (kunã so) in gaya1 muku a kan wanda Shaiɗãnnu kan sauka?

222

تَنَزَّلُ عَلَىٰ كُلِّ أَفَّاكٍ أَثِيمٍۢ

tanazzalu ʿalā kulli affākin athīmin

Sukan sauka a kan dukkan maƙaryaci, mai zunubi.

223

يُلْقُونَ ٱلسَّمْعَ وَأَكْثَرُهُمْ كَـٰذِبُونَ

yul'qūna l-samʿa wa-aktharuhum kādhibūna

Sunã jẽfa (abin da suka) ji, alhãli kuwa mafi yawansu maƙaryata ne.

224

وَٱلشُّعَرَآءُ يَتَّبِعُهُمُ ٱلْغَاوُۥنَ

wal-shuʿarāu yattabiʿuhumu l-ghāwūna

Kuma mawãƙa1 halakakku ne ke bin su.

225

أَلَمْ تَرَ أَنَّهُمْ فِى كُلِّ وَادٍۢ يَهِيمُونَ

alam tara annahum fī kulli wādin yahīmūna

Shin, ba ku cẽwa, lalle ne sũ, cikin kõwane rango sunã yin ɗimuwa (su ƙẽtare haddi) ba?

226

وَأَنَّهُمْ يَقُولُونَ مَا لَا يَفْعَلُونَ

wa-annahum yaqūlūna mā lā yafʿalūna

Kuma lalle ne, sũ, sunã faɗin abin da bã su aikatãwa?

227

إِلَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ وَعَمِلُوا۟ ٱلصَّـٰلِحَـٰتِ وَذَكَرُوا۟ ٱللَّهَ كَثِيرًۭا وَٱنتَصَرُوا۟ مِنۢ بَعْدِ مَا ظُلِمُوا۟ ۗ وَسَيَعْلَمُ ٱلَّذِينَ ظَلَمُوٓا۟ أَىَّ مُنقَلَبٍۢ يَنقَلِبُونَ

illā alladhīna āmanū waʿamilū l-ṣāliḥāti wadhakarū l-laha kathīran wa-intaṣarū min baʿdi mā ẓulimū wasayaʿlamu alladhīna ẓalamū ayya munqalabin yanqalibūna

Fãce waɗanda suka yi ĩmãni suka aikata ayyukan ƙwarai, kuma suka ambaci Allah da yawa, kuma suka rãma zãlunci, daga bãyan an zãlunce su. Kuma waɗanda suka yi zãlunci, zã su sani a wace majũya suke jũyãwa.

Game da Wannan Sura