37

الصافات

As-Saffat

Those Who Set The Ranks

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ Da sunan Allah Mai rahama Mai jin kai
Ayoyi 182
Juzu'i 23
Shafi 446-452
Nau'i Makkiya
Tsarin Saukarwa 56
0:00 / 0:00
Aya: 1 / 182
1

وَٱلصَّـٰٓفَّـٰتِ صَفًّۭا

wal-ṣāfāti ṣaffan

Inã rantsuwa da mãsu yin sahu-sahu (a cikin salla kõ yãƙi).

2

فَٱلزَّٰجِرَٰتِ زَجْرًۭا

fal-zājirāti zajran

Sa'an nan mãsu yin tsãwa1 dõmin gargaɗi.

3

فَٱلتَّـٰلِيَـٰتِ ذِكْرًا

fal-tāliyāti dhik'ran

Sa'an nan da mãsu karãtun abin tunãtarwa.

4

إِنَّ إِلَـٰهَكُمْ لَوَٰحِدٌۭ

inna ilāhakum lawāḥidun

Lalle Abin bautawarku haƙĩƙa ¦aya ne.

5

رَّبُّ ٱلسَّمَـٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ وَمَا بَيْنَهُمَا وَرَبُّ ٱلْمَشَـٰرِقِ

rabbu l-samāwāti wal-arḍi wamā baynahumā warabbu l-mashāriqi

Ubangijin sammai da ƙasã da abin da ke tsakãninsu, kuma Ubangijin wurãren fitar rãnã.

6

إِنَّا زَيَّنَّا ٱلسَّمَآءَ ٱلدُّنْيَا بِزِينَةٍ ٱلْكَوَاكِبِ

innā zayyannā l-samāa l-dun'yā bizīnatin l-kawākibi

Lalle Mũ, Mun ƙãwatãr da sama ta kusa da wata ƙawa, watau taurãri.

7

وَحِفْظًۭا مِّن كُلِّ شَيْطَـٰنٍۢ مَّارِدٍۢ

waḥif'ẓan min kulli shayṭānin māridin

Kuma sunã tsari daga dukan Shaiɗan mai tsaurin kai.

8

لَّا يَسَّمَّعُونَ إِلَى ٱلْمَلَإِ ٱلْأَعْلَىٰ وَيُقْذَفُونَ مِن كُلِّ جَانِبٍۢ

lā yassammaʿūna ilā l-mala-i l-aʿlā wayuq'dhafūna min kulli jānibin

Bã zã su iya saurãre zuwa ga jama'a mafi ɗaukaka (Malã'iku) ba, kuma anã jĩfar su daga kõwane gẽfe.

9

دُحُورًۭا ۖ وَلَهُمْ عَذَابٌۭ وَاصِبٌ

duḥūran walahum ʿadhābun wāṣibun

Dõmin tunkuɗẽwa kuma sunã da wata azãba tabbatacciya.

10

إِلَّا مَنْ خَطِفَ ٱلْخَطْفَةَ فَأَتْبَعَهُۥ شِهَابٌۭ ثَاقِبٌۭ

illā man khaṭifa l-khaṭfata fa-atbaʿahu shihābun thāqibun

Fãce wanda ya fizgi wata kalma, sai yũla mai haske ta bĩ shi.

11

فَٱسْتَفْتِهِمْ أَهُمْ أَشَدُّ خَلْقًا أَم مَّنْ خَلَقْنَآ ۚ إِنَّا خَلَقْنَـٰهُم مِّن طِينٍۢ لَّازِبٍۭ

fa-is'taftihim ahum ashaddu khalqan am man khalaqnā innā khalaqnāhum min ṭīnin lāzibin

Ka tambaye su: "Shin sũ ne mafi wuya ga halittawa, kõ, kuwa waɗanda Muka halitta?" Lalle Mũ, Mun halitta su daga lãkã mai ɗauri.

12

بَلْ عَجِبْتَ وَيَسْخَرُونَ

bal ʿajib'ta wayaskharūna

Ã'a, kã yi mãmãki, alhãli kuwa sunã ta yin izgili.

13

وَإِذَا ذُكِّرُوا۟ لَا يَذْكُرُونَ

wa-idhā dhukkirū lā yadhkurūna

Kuma idan aka tunãtar da su, bã su tunãwa.

14

وَإِذَا رَأَوْا۟ ءَايَةًۭ يَسْتَسْخِرُونَ

wa-idhā ra-aw āyatan yastaskhirūna

Idan suka ga wata ãyã, sai su dinga yin izgili.

15

وَقَالُوٓا۟ إِنْ هَـٰذَآ إِلَّا سِحْرٌۭ مُّبِينٌ

waqālū in hādhā illā siḥ'run mubīnun

Kuma su ce, "Wannnan bã kõme ba, fãce sihiri, ne bayyananne."

16

أَءِذَا مِتْنَا وَكُنَّا تُرَابًۭا وَعِظَـٰمًا أَءِنَّا لَمَبْعُوثُونَ

a-idhā mit'nā wakunnā turāban waʿiẓāman a-innā lamabʿūthūna

"Shin, idan mun mutu, kuma muka kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle mũ tabbas waɗandaake tãyarwa ne?

17

أَوَءَابَآؤُنَا ٱلْأَوَّلُونَ

awaābāunā l-awalūna

"Ashe kõ da ubanninmu na farko?"

18

قُلْ نَعَمْ وَأَنتُمْ دَٰخِرُونَ

qul naʿam wa-antum dākhirūna

Ka ce: "Na'am alhãli kuwa kunã ƙasƙantattu."

19

فَإِنَّمَا هِىَ زَجْرَةٌۭ وَٰحِدَةٌۭ فَإِذَا هُمْ يَنظُرُونَ

fa-innamā hiya zajratun wāḥidatun fa-idhā hum yanẓurūna

Tsãwa guda kawai ce, sai gã su, sunã dũbi.

20

وَقَالُوا۟ يَـٰوَيْلَنَا هَـٰذَا يَوْمُ ٱلدِّينِ

waqālū yāwaylanā hādhā yawmu l-dīni

Kuma su ce: "Yã bonenmu! Wannan ita ce rãnar sakamako."

21

هَـٰذَا يَوْمُ ٱلْفَصْلِ ٱلَّذِى كُنتُم بِهِۦ تُكَذِّبُونَ

hādhā yawmu l-faṣli alladhī kuntum bihi tukadhibūna

Wannan ita ce rãnar rarrabẽwa wadda kuka kasance kuna ƙaryatãwa.

22

۞ ٱحْشُرُوا۟ ٱلَّذِينَ ظَلَمُوا۟ وَأَزْوَٰجَهُمْ وَمَا كَانُوا۟ يَعْبُدُونَ

uḥ'shurū alladhīna ẓalamū wa-azwājahum wamā kānū yaʿbudūna

Ku tãra waɗanda suka yi zãlunci, da abõkan haɗinsu, da abin da suka kasance sunã bautãwa.

23

مِن دُونِ ٱللَّهِ فَٱهْدُوهُمْ إِلَىٰ صِرَٰطِ ٱلْجَحِيمِ

min dūni l-lahi fa-ih'dūhum ilā ṣirāṭi l-jaḥīmi

Wanin Allah, sabõda haka ku shiryar da su zuwa ga hanyar Jahĩm.

24

وَقِفُوهُمْ ۖ إِنَّهُم مَّسْـُٔولُونَ

waqifūhum innahum masūlūna

Kuma ku tsayar da su, lalle su, waɗanda ake yi wa tambaya ne.

25

مَا لَكُمْ لَا تَنَاصَرُونَ

mā lakum lā tanāṣarūna

Me ya sãme ku, bã ku taimakon jũna?

26

بَلْ هُمُ ٱلْيَوْمَ مُسْتَسْلِمُونَ

bal humu l-yawma mus'taslimūna

Ã'a, sũ a yau, mãsu sallamãwa ne.

27

وَأَقْبَلَ بَعْضُهُمْ عَلَىٰ بَعْضٍۢ يَتَسَآءَلُونَ

wa-aqbala baʿḍuhum ʿalā baʿḍin yatasāalūna

Kuma sãshensu ya fuskanta ga sãshe, sunã tambayar jũna.

28

قَالُوٓا۟ إِنَّكُمْ كُنتُمْ تَأْتُونَنَا عَنِ ٱلْيَمِينِ

qālū innakum kuntum tatūnanā ʿani l-yamīni

Suka ce: "Lalle kũ, kun kasance kunã jẽ mana daga wajen dãma (inda muka amince)."

29

قَالُوا۟ بَل لَّمْ تَكُونُوا۟ مُؤْمِنِينَ

qālū bal lam takūnū mu'minīna

Suka ce: "Ã'a, ba ku kasance mũminai ba.

30

وَمَا كَانَ لَنَا عَلَيْكُم مِّن سُلْطَـٰنٍۭ ۖ بَلْ كُنتُمْ قَوْمًۭا طَـٰغِينَ

wamā kāna lanā ʿalaykum min sul'ṭānin bal kuntum qawman ṭāghīna

"Kuma wani dalĩli bai kasance ba gare mu a kanku. Ã'a, kun kasance mutãne ne mãsu kẽtare iyãka."

31

فَحَقَّ عَلَيْنَا قَوْلُ رَبِّنَآ ۖ إِنَّا لَذَآئِقُونَ

faḥaqqa ʿalaynā qawlu rabbinā innā ladhāiqūna

"Sabõda haka maganar Ubangijinmu ta wajaba a kanmu. Lalle mũ, mãsu ɗanɗanãwa ne."

32

فَأَغْوَيْنَـٰكُمْ إِنَّا كُنَّا غَـٰوِينَ

fa-aghwaynākum innā kunnā ghāwīna

"Sabõda haka muka ɓatar da ku. Lalle mũ, mun kasance ɓatattu."

33

فَإِنَّهُمْ يَوْمَئِذٍۢ فِى ٱلْعَذَابِ مُشْتَرِكُونَ

fa-innahum yawma-idhin fī l-ʿadhābi mush'tarikūna

To lalle sũ a rãnar nan, mãsu tãrayya ne a cikin azãbar.

34

إِنَّا كَذَٰلِكَ نَفْعَلُ بِٱلْمُجْرِمِينَ

innā kadhālika nafʿalu bil-muj'rimīna

Lalle Mũ, kamar haka Muke aikatãwa game, da mãsu laifi.

35

إِنَّهُمْ كَانُوٓا۟ إِذَا قِيلَ لَهُمْ لَآ إِلَـٰهَ إِلَّا ٱللَّهُ يَسْتَكْبِرُونَ

innahum kānū idhā qīla lahum lā ilāha illā l-lahu yastakbirūna

Lalle sũ, sun kasance idan an ce musu: "Bãbu abin bautãwa, fãce Allah," sai su dõra girman kai.

36

وَيَقُولُونَ أَئِنَّا لَتَارِكُوٓا۟ ءَالِهَتِنَا لِشَاعِرٍۢ مَّجْنُونٍۭ

wayaqūlūna a-innā latārikū ālihatinā lishāʿirin majnūnin

Kuma sunã cẽwa, "Shin, mũ lalle mãsu barin gumãkanmu ne, sabõda maganar wani mawãƙi mahaukaci?

37

بَلْ جَآءَ بِٱلْحَقِّ وَصَدَّقَ ٱلْمُرْسَلِينَ

bal jāa bil-ḥaqi waṣaddaqa l-mur'salīna

Ã'a, yã zo da gaskiya kuma ya gaskata Manzanni.

38

إِنَّكُمْ لَذَآئِقُوا۟ ٱلْعَذَابِ ٱلْأَلِيمِ

innakum ladhāiqū l-ʿadhābi l-alīmi

Lalle kũ, haƙĩƙa mãsu ɗanɗana azãba mai raɗaɗi ne.

39

وَمَا تُجْزَوْنَ إِلَّا مَا كُنتُمْ تَعْمَلُونَ

wamā tuj'zawna illā mā kuntum taʿmalūna

Kuma bã zã a sãka muku ba fãce da abin da kuka kasance kunã aikatãwa.

40

إِلَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلْمُخْلَصِينَ

illā ʿibāda l-lahi l-mukh'laṣīna

Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.

41

أُو۟لَـٰٓئِكَ لَهُمْ رِزْقٌۭ مَّعْلُومٌۭ

ulāika lahum riz'qun maʿlūmun

Waɗannan sunã da abinci sananne.

42

فَوَٰكِهُ ۖ وَهُم مُّكْرَمُونَ

fawākihu wahum muk'ramūna

Ya'yan itãcen marmari, kuma sunã waɗanda ake girmamãwa.

43

فِى جَنَّـٰتِ ٱلنَّعِيمِ

fī jannāti l-naʿīmi

A cikin gidãjen Aljannar ni'ima.

44

عَلَىٰ سُرُرٍۢ مُّتَقَـٰبِلِينَ

ʿalā sururin mutaqābilīna

A kan karagu, sunã mãsu fuskantar jũna.

45

يُطَافُ عَلَيْهِم بِكَأْسٍۢ مِّن مَّعِينٍۭ

yuṭāfu ʿalayhim bikasin min maʿīnin

Anã kẽwayãwa a kansu da hinjãlan giya, ta daga waɗansu marẽmari.

46

بَيْضَآءَ لَذَّةٍۢ لِّلشَّـٰرِبِينَ

bayḍāa ladhatin lilshāribīna

Farã mai dãɗi ga mashãyan.

47

لَا فِيهَا غَوْلٌۭ وَلَا هُمْ عَنْهَا يُنزَفُونَ

lā fīhā ghawlun walā hum ʿanhā yunzafūna

A cikinta bãbu jirĩ kuma ba su zama mãsu mãye daga gare ta ba,

48

وَعِندَهُمْ قَـٰصِرَٰتُ ٱلطَّرْفِ عِينٌۭ

waʿindahum qāṣirātu l-ṭarfi ʿīnun

Kuma a wurinsu, akwai mãtan aure mãsu taƙaita kallonsu, mãsu manyan idãnu.

49

كَأَنَّهُنَّ بَيْضٌۭ مَّكْنُونٌۭ

ka-annahunna bayḍun maknūnun

Kamar dai su ƙwai ne ɓõyayye.

50

فَأَقْبَلَ بَعْضُهُمْ عَلَىٰ بَعْضٍۢ يَتَسَآءَلُونَ

fa-aqbala baʿḍuhum ʿalā baʿḍin yatasāalūna

Sai sãshensu ya fuskanta a kan sãshe, sunã tambayar jũna.

51

قَالَ قَآئِلٌۭ مِّنْهُمْ إِنِّى كَانَ لِى قَرِينٌۭ

qāla qāilun min'hum innī kāna lī qarīnun

Wani mai magana daga cikinsu ya ce: "Lalle ni wani abõki ya kasance a gare ni (a dũniya)."

52

يَقُولُ أَءِنَّكَ لَمِنَ ٱلْمُصَدِّقِينَ

yaqūlu a-innaka lamina l-muṣadiqīna

Yanã cewa, "Shin, kai lalle, kanã daga mãsu gaskatãwa ne?"

53

أَءِذَا مِتْنَا وَكُنَّا تُرَابًۭا وَعِظَـٰمًا أَءِنَّا لَمَدِينُونَ

a-idhā mit'nā wakunnā turāban waʿiẓāman a-innā lamadīnūna

"Ashe, idan muka mutu, kuma muka, kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle, mũ tabbas waɗanda ake sãka wa ne?"

54

قَالَ هَلْ أَنتُم مُّطَّلِعُونَ

qāla hal antum muṭṭaliʿūna

(Mai maganar) ya ce: "Shin, kõ ku, mãsu tsinkãya ne (mu gan shi)?"

55

فَٱطَّلَعَ فَرَءَاهُ فِى سَوَآءِ ٱلْجَحِيمِ

fa-iṭṭalaʿa faraāhu fī sawāi l-jaḥīmi

Sai ya tsinkãya, sai ya gan shi a cikin tsakar Jahim.

56

قَالَ تَٱللَّهِ إِن كِدتَّ لَتُرْدِينِ

qāla tal-lahi in kidtta latur'dīni

Ya ce (masa), "Wallahi, lalle, kã yi kusa, haƙĩƙã, ka halakãni."

57

وَلَوْلَا نِعْمَةُ رَبِّى لَكُنتُ مِنَ ٱلْمُحْضَرِينَ

walawlā niʿ'matu rabbī lakuntu mina l-muḥ'ḍarīna

"Kuma bã dõmin ni'imar Ubangijĩna ba, lalle, dã na kasance daga waɗanda ake halartarwa (tãre da kai a cikin wutã)."

58

أَفَمَا نَحْنُ بِمَيِّتِينَ

afamā naḥnu bimayyitīna

"Shin fa, ba mu zama mãsu mutuwa ba."

59

إِلَّا مَوْتَتَنَا ٱلْأُولَىٰ وَمَا نَحْنُ بِمُعَذَّبِينَ

illā mawtatanā l-ūlā wamā naḥnu bimuʿadhabīna

"Sai mutuwarmu ta farko, kuma ba mu zama waɗanda ake azabtarwa ba?"

60

إِنَّ هَـٰذَا لَهُوَ ٱلْفَوْزُ ٱلْعَظِيمُ

inna hādhā lahuwa l-fawzu l-ʿaẓīmu

Lalle, wannan shĩ ne babban rabo mai girma.

61

لِمِثْلِ هَـٰذَا فَلْيَعْمَلِ ٱلْعَـٰمِلُونَ

limith'li hādhā falyaʿmali l-ʿāmilūna

Sabõda irin wannan, sai mãsu aiki su yi ta aikatãwa.

62

أَذَٰلِكَ خَيْرٌۭ نُّزُلًا أَمْ شَجَرَةُ ٱلزَّقُّومِ

adhālika khayrun nuzulan am shajaratu l-zaqūmi

Shin wancan shĩ ne mafi zama alhẽri ga liyafa kõ itãciyar zaƙƙũm?

63

إِنَّا جَعَلْنَـٰهَا فِتْنَةًۭ لِّلظَّـٰلِمِينَ

innā jaʿalnāhā fit'natan lilẓẓālimīna

Lalle, Mũ, Mun sanya ta fitina ga. azzãlumai.

64

إِنَّهَا شَجَرَةٌۭ تَخْرُجُ فِىٓ أَصْلِ ٱلْجَحِيمِ

innahā shajaratun takhruju fī aṣli l-jaḥīmi

Lalle ita wata itãciya ce wadda take fita daga asalin Jahĩm.

65

طَلْعُهَا كَأَنَّهُۥ رُءُوسُ ٱلشَّيَـٰطِينِ

ṭalʿuhā ka-annahu ruūsu l-shayāṭīni

Gundarta, kamar dai shi kãnun Shaiɗan ne.

66

فَإِنَّهُمْ لَـَٔاكِلُونَ مِنْهَا فَمَالِـُٔونَ مِنْهَا ٱلْبُطُونَ

fa-innahum laākilūna min'hā famāliūna min'hā l-buṭūna

To, lalle sũ haƙĩƙa mãsu ci ne daga gare ta. Sa'an nan mãsu cika cikuna ne daga gare ta.

67

ثُمَّ إِنَّ لَهُمْ عَلَيْهَا لَشَوْبًۭا مِّنْ حَمِيمٍۢ

thumma inna lahum ʿalayhā lashawban min ḥamīmin

Sa'an nan lalle sunã da wani garwaye a kanta, daga ruwan zãfi.

68

ثُمَّ إِنَّ مَرْجِعَهُمْ لَإِلَى ٱلْجَحِيمِ

thumma inna marjiʿahum la-ilā l-jaḥīmi

Sa'an nan lalle makomarsu, haƙĩƙa, zuwa ga Jãhĩm take.

69

إِنَّهُمْ أَلْفَوْا۟ ءَابَآءَهُمْ ضَآلِّينَ

innahum alfaw ābāahum ḍāllīna

Lalle sũ, sun iske ubanninsu batattu.

70

فَهُمْ عَلَىٰٓ ءَاثَـٰرِهِمْ يُهْرَعُونَ

fahum ʿalā āthārihim yuh'raʿūna

Sabõda haka sũ, a kan gurãbunsu, suke gaggãwa.

71

وَلَقَدْ ضَلَّ قَبْلَهُمْ أَكْثَرُ ٱلْأَوَّلِينَ

walaqad ḍalla qablahum aktharu l-awalīna

Kuma tabbas haƙĩƙa mafi yawan mutãnen farko sun ɓace a gabãninsu.

72

وَلَقَدْ أَرْسَلْنَا فِيهِم مُّنذِرِينَ

walaqad arsalnā fīhim mundhirīna

Kuma tabbas haƙĩƙa, Mun aika mãsu gargaɗi a cikinsu.

73

فَٱنظُرْ كَيْفَ كَانَ عَـٰقِبَةُ ٱلْمُنذَرِينَ

fa-unẓur kayfa kāna ʿāqibatu l-mundharīna

Sai ka dũba yadda ãƙibar waɗanda aka yi wa gargaɗi ta kasance.

74

إِلَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلْمُخْلَصِينَ

illā ʿibāda l-lahi l-mukh'laṣīna

Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.

75

وَلَقَدْ نَادَىٰنَا نُوحٌۭ فَلَنِعْمَ ٱلْمُجِيبُونَ

walaqad nādānā nūḥun falaniʿ'ma l-mujībūna

Kuma lalle, haƙĩƙa' Nũhu ya kira Mu. To, madalla da mãsu karɓãwa, Mu.

76

وَنَجَّيْنَـٰهُ وَأَهْلَهُۥ مِنَ ٱلْكَرْبِ ٱلْعَظِيمِ

wanajjaynāhu wa-ahlahu mina l-karbi l-ʿaẓīmi

Kuma Mun tsĩrar da shi da mutãnensa daga bakin ciki babba.

77

وَجَعَلْنَا ذُرِّيَّتَهُۥ هُمُ ٱلْبَاقِينَ

wajaʿalnā dhurriyyatahu humu l-bāqīna

Muka sanya zurriyarsa sunã mãsu wanzuwa.

78

وَتَرَكْنَا عَلَيْهِ فِى ٱلْـَٔاخِرِينَ

wataraknā ʿalayhi fī l-ākhirīna

Kuma Muka bar masa (yabo) a cikin jama'ar ƙarshe.

79

سَلَـٰمٌ عَلَىٰ نُوحٍۢ فِى ٱلْعَـٰلَمِينَ

salāmun ʿalā nūḥin fī l-ʿālamīna

Aminci ya tabbata ga Nũhu, a cikin halittu.

80

إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِى ٱلْمُحْسِنِينَ

innā kadhālika najzī l-muḥ'sinīna

Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.

81

إِنَّهُۥ مِنْ عِبَادِنَا ٱلْمُؤْمِنِينَ

innahu min ʿibādinā l-mu'minīna

Lalle shi, yanã daga bãyin Mu mũminai.

82

ثُمَّ أَغْرَقْنَا ٱلْـَٔاخَرِينَ

thumma aghraqnā l-ākharīna

Sã'an nan Muka nutsar da waɗansunsu.

83

۞ وَإِنَّ مِن شِيعَتِهِۦ لَإِبْرَٰهِيمَ

wa-inna min shīʿatihi la-ib'rāhīma

Kuma lalle daga ƙungiyarsa, haƙĩƙa, Ibrahĩm yake.

84

إِذْ جَآءَ رَبَّهُۥ بِقَلْبٍۢ سَلِيمٍ

idh jāa rabbahu biqalbin salīmin

A lõkacin da ya je wa ubangijinsa da zũciya kuɓutacciya.

85

إِذْ قَالَ لِأَبِيهِ وَقَوْمِهِۦ مَاذَا تَعْبُدُونَ

idh qāla li-abīhi waqawmihi mādhā taʿbudūna

A lõkacin da ya ce wa ubansa da mutãnensa, "Mẽne ne kuke bautãwa?"

86

أَئِفْكًا ءَالِهَةًۭ دُونَ ٱللَّهِ تُرِيدُونَ

a-if'kan ālihatan dūna l-lahi turīdūna

"Shin, ƙiren ƙarya (wãtau) gumãka, wanin Allah, kuke bautãwa?"

87

فَمَا ظَنُّكُم بِرَبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ

famā ẓannukum birabbi l-ʿālamīna

"To, mẽne ne zatonku game da Ubangijin halittu?"

88

فَنَظَرَ نَظْرَةًۭ فِى ٱلنُّجُومِ

fanaẓara naẓratan fī l-nujūmi

Sai ya yi dũbi, dũba ta sõsai, a cikin taurãri.

89

فَقَالَ إِنِّى سَقِيمٌۭ

faqāla innī saqīmun

Sã'an nan ya ce: "Nĩ mai rashin lãfiya ne."

90

فَتَوَلَّوْا۟ عَنْهُ مُدْبِرِينَ

fatawallaw ʿanhu mud'birīna

Sai suka jũya ga barinsa, sunã mãsu jũyãwa da bãya.

91

فَرَاغَ إِلَىٰٓ ءَالِهَتِهِمْ فَقَالَ أَلَا تَأْكُلُونَ

farāgha ilā ālihatihim faqāla alā takulūna

Sai ya karkata zuwa ga gumãkansu, sa'an nan ya ce: "Ashe bã zã ku ci ba?

92

مَا لَكُمْ لَا تَنطِقُونَ

mā lakum lā tanṭiqūna

"Me ya sãme ku, bã ku magana?"

93

فَرَاغَ عَلَيْهِمْ ضَرْبًۢا بِٱلْيَمِينِ

farāgha ʿalayhim ḍarban bil-yamīni

Sai ya zuba dũka a kansu da hannun dãma.

94

فَأَقْبَلُوٓا۟ إِلَيْهِ يَزِفُّونَ

fa-aqbalū ilayhi yaziffūna

Sai suka fuskanto zuwa gare shi, sunã gaggãwa.

95

قَالَ أَتَعْبُدُونَ مَا تَنْحِتُونَ

qāla ataʿbudūna mā tanḥitūna

Ya ce, "Kunã bauta wa abin da kuke sassaƙawa,

96

وَٱللَّهُ خَلَقَكُمْ وَمَا تَعْمَلُونَ

wal-lahu khalaqakum wamā taʿmalūna

"Alhãli, Allah ne Ya halitta ku game da abin da kuke aikatãwa?"

97

قَالُوا۟ ٱبْنُوا۟ لَهُۥ بُنْيَـٰنًۭا فَأَلْقُوهُ فِى ٱلْجَحِيمِ

qālū ib'nū lahu bun'yānan fa-alqūhu fī l-jaḥīmi

Suka ce: "Ku gina wani gini sabõda shi, sa'an nan ku jẽfa shi a cikin Jahĩm."

98

فَأَرَادُوا۟ بِهِۦ كَيْدًۭا فَجَعَلْنَـٰهُمُ ٱلْأَسْفَلِينَ

fa-arādū bihi kaydan fajaʿalnāhumu l-asfalīna

Sabõda haka suka yi nufin makĩda game da shi. Sai Muka sanya su, sũ ne mafi ƙasƙanci.

99

وَقَالَ إِنِّى ذَاهِبٌ إِلَىٰ رَبِّى سَيَهْدِينِ

waqāla innī dhāhibun ilā rabbī sayahdīni

Kuma (Ibrahĩm] ya ce: "Lalle, nĩ mai tafiya ne zuwa ga Ubangijĩna, zai shiryar da ni."

100

رَبِّ هَبْ لِى مِنَ ٱلصَّـٰلِحِينَ

rabbi hab lī mina l-ṣāliḥīna

"Ya Ubangijĩna! Ka bã ni (abõkin zama) daga sãlihan mutãne."

101

فَبَشَّرْنَـٰهُ بِغُلَـٰمٍ حَلِيمٍۢ

fabasharnāhu bighulāmin ḥalīmin

Sai Muka yi masa bushãra da wani yãro 1mai haƙuri.

102

فَلَمَّا بَلَغَ مَعَهُ ٱلسَّعْىَ قَالَ يَـٰبُنَىَّ إِنِّىٓ أَرَىٰ فِى ٱلْمَنَامِ أَنِّىٓ أَذْبَحُكَ فَٱنظُرْ مَاذَا تَرَىٰ ۚ قَالَ يَـٰٓأَبَتِ ٱفْعَلْ مَا تُؤْمَرُ ۖ سَتَجِدُنِىٓ إِن شَآءَ ٱللَّهُ مِنَ ٱلصَّـٰبِرِينَ

falammā balagha maʿahu l-saʿya qāla yābunayya innī arā fī l-manāmi annī adhbaḥuka fa-unẓur mādhā tarā qāla yāabati if'ʿal mā tu'maru satajidunī in shāa l-lahu mina l-ṣābirīna

To, a lõkacin da ya isa aiki tãre da shi, ya ce: "Ya ƙaramin ɗãna! Lalle ne inã gani, a ciki barci, lalle inã yanka ka. To, ka dũba mẽ ka gani?" (Yãron) ya ce: "Ya, Bãbãna! Ka aikata abin da aka umurce ka, zã ka sãme ni, in Allah Ya so, daga mãsu haƙuri."

103

فَلَمَّآ أَسْلَمَا وَتَلَّهُۥ لِلْجَبِينِ

falammā aslamā watallahu lil'jabīni

Yayin da suka mika wuya sai muka fansheshi da Rago

104

وَنَـٰدَيْنَـٰهُ أَن يَـٰٓإِبْرَٰهِيمُ

wanādaynāhu an yāib'rāhīmu

Kuma Muka kira shi cẽwa "Ya Ibrahĩm!"

105

قَدْ صَدَّقْتَ ٱلرُّءْيَآ ۚ إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِى ٱلْمُحْسِنِينَ

qad ṣaddaqta l-ru'yā innā kadhālika najzī l-muḥ'sinīna

"Haƙĩƙa kã gaskata mafarkin." Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.

106

إِنَّ هَـٰذَا لَهُوَ ٱلْبَلَـٰٓؤُا۟ ٱلْمُبِينُ

inna hādhā lahuwa l-balāu l-mubīnu

Lalle wannan ita ce jarrabãwa bayyananna.

107

وَفَدَيْنَـٰهُ بِذِبْحٍ عَظِيمٍۢ

wafadaynāhu bidhib'ḥin ʿaẓīmin

Kuma Muka yi fansar yãron da wani abin yanka, mai girma.

108

وَتَرَكْنَا عَلَيْهِ فِى ٱلْـَٔاخِرِينَ

wataraknā ʿalayhi fī l-ākhirīna

Kuma Muka bar (yabo) a kansa a cikin mutãnen ƙarshe.

109

سَلَـٰمٌ عَلَىٰٓ إِبْرَٰهِيمَ

salāmun ʿalā ib'rāhīma

Aminci ya tabbata ga Ibrãhĩm.

110

كَذَٰلِكَ نَجْزِى ٱلْمُحْسِنِينَ

kadhālika najzī l-muḥ'sinīna

Kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.

111

إِنَّهُۥ مِنْ عِبَادِنَا ٱلْمُؤْمِنِينَ

innahu min ʿibādinā l-mu'minīna

Lalle shĩ, yanã daga bãyinMu mũminai.

112

وَبَشَّرْنَـٰهُ بِإِسْحَـٰقَ نَبِيًّۭا مِّنَ ٱلصَّـٰلِحِينَ

wabasharnāhu bi-is'ḥāqa nabiyyan mina l-ṣāliḥīna

Kuma Muka yi masa bushãra1 Da Is'hãƙa ya zama Annabi daga sãlihan mutãne.

113

وَبَـٰرَكْنَا عَلَيْهِ وَعَلَىٰٓ إِسْحَـٰقَ ۚ وَمِن ذُرِّيَّتِهِمَا مُحْسِنٌۭ وَظَالِمٌۭ لِّنَفْسِهِۦ مُبِينٌۭ

wabāraknā ʿalayhi waʿalā is'ḥāqa wamin dhurriyyatihimā muḥ'sinun waẓālimun linafsihi mubīnun

Kuma Muka yi albarka a gare shi, kuma ga Is'hãka. Kuma daga cikin zurriyarsu akwai mai kyautatãwa da kuma maizãlunci dõmin kansa, mai bayyanãwa (ga zãluncin).

114

وَلَقَدْ مَنَنَّا عَلَىٰ مُوسَىٰ وَهَـٰرُونَ

walaqad manannā ʿalā mūsā wahārūna

Kuma lalle, Mun yi ni'ima ga Mũsã da Hãrũna.

115

وَنَجَّيْنَـٰهُمَا وَقَوْمَهُمَا مِنَ ٱلْكَرْبِ ٱلْعَظِيمِ

wanajjaynāhumā waqawmahumā mina l-karbi l-ʿaẓīmi

Kuma Muka tsĩrar da su da mutãnensu daga bakin ciki mai girma.

116

وَنَصَرْنَـٰهُمْ فَكَانُوا۟ هُمُ ٱلْغَـٰلِبِينَ

wanaṣarnāhum fakānū humu l-ghālibīna

Kuma Muka taimake su, sabõda haka suka kasance mãsu rinjãya.

117

وَءَاتَيْنَـٰهُمَا ٱلْكِتَـٰبَ ٱلْمُسْتَبِينَ

waātaynāhumā l-kitāba l-mus'tabīna

Kuma Muka ba su Littãfi mai iyãkar bayãni.

118

وَهَدَيْنَـٰهُمَا ٱلصِّرَٰطَ ٱلْمُسْتَقِيمَ

wahadaynāhumā l-ṣirāṭa l-mus'taqīma

Kuma Muka shiryar da su ga hanya mĩƙaƙƙiya.

119

وَتَرَكْنَا عَلَيْهِمَا فِى ٱلْـَٔاخِرِينَ

wataraknā ʿalayhimā fī l-ākhirīna

Kuma Muka bar (yabo) a gare su a cikin mutãnen karshe.

120

سَلَـٰمٌ عَلَىٰ مُوسَىٰ وَهَـٰرُونَ

salāmun ʿalā mūsā wahārūna

Aminci ya tabbata ga Mũsã da Hãruna.

121

إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِى ٱلْمُحْسِنِينَ

innā kadhālika najzī l-muḥ'sinīna

Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.

122

إِنَّهُمَا مِنْ عِبَادِنَا ٱلْمُؤْمِنِينَ

innahumā min ʿibādinā l-mu'minīna

Lalle, sunã daga bãyin Mu mũminai.

123

وَإِنَّ إِلْيَاسَ لَمِنَ ٱلْمُرْسَلِينَ

wa-inna il'yāsa lamina l-mur'salīna

Kuma lalle Ilyãs, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.

124

إِذْ قَالَ لِقَوْمِهِۦٓ أَلَا تَتَّقُونَ

idh qāla liqawmihi alā tattaqūna

A lõkacin da yake ce wa mutãnensa, "Ashe, bã zã ku yi taƙawa ba?"

125

أَتَدْعُونَ بَعْلًۭا وَتَذَرُونَ أَحْسَنَ ٱلْخَـٰلِقِينَ

atadʿūna baʿlan watadharūna aḥsana l-khāliqīna

"Shin, kunã bauta wa Ba'al ne, kuma kunã barin Mafi kyautatãwar mãsu halitta?"

126

ٱللَّهَ رَبَّكُمْ وَرَبَّ ءَابَآئِكُمُ ٱلْأَوَّلِينَ

al-laha rabbakum warabba ābāikumu l-awalīna

"Allah Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku farko?"

127

فَكَذَّبُوهُ فَإِنَّهُمْ لَمُحْضَرُونَ

fakadhabūhu fa-innahum lamuḥ'ḍarūna

Sai suka ƙaryata shi. Sabõda haka sũ lalle waɗanda zã a halartãwa ne (a wutã).

128

إِلَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلْمُخْلَصِينَ

illā ʿibāda l-lahi l-mukh'laṣīna

Sai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.

129

وَتَرَكْنَا عَلَيْهِ فِى ٱلْـَٔاخِرِينَ

wataraknā ʿalayhi fī l-ākhirīna

Kuma Muka bar (yabo) a gare shi, a cikin mutãnen ƙarshe.

130

سَلَـٰمٌ عَلَىٰٓ إِلْ يَاسِينَ

salāmun ʿalā il yāsīna

Aminci ya tabbata ga Ilyãs.

131

إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِى ٱلْمُحْسِنِينَ

innā kadhālika najzī l-muḥ'sinīna

Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.

132

إِنَّهُۥ مِنْ عِبَادِنَا ٱلْمُؤْمِنِينَ

innahu min ʿibādinā l-mu'minīna

Lalle shĩ, yanã daga bãyin Mu mũminai.

133

وَإِنَّ لُوطًۭا لَّمِنَ ٱلْمُرْسَلِينَ

wa-inna lūṭan lamina l-mur'salīna

Kuma lalle Lũdu, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.

134

إِذْ نَجَّيْنَـٰهُ وَأَهْلَهُۥٓ أَجْمَعِينَ

idh najjaynāhu wa-ahlahu ajmaʿīna

A lõkacin da Muka tsĩrar da shi, da mutãnensa gabã ɗaya.

135

إِلَّا عَجُوزًۭا فِى ٱلْغَـٰبِرِينَ

illā ʿajūzan fī l-ghābirīna

Sai wata tsõhuwa tanã a cikin mãsu wanzuwa (a cikin azãba).

136

ثُمَّ دَمَّرْنَا ٱلْـَٔاخَرِينَ

thumma dammarnā l-ākharīna

Sã'an nan Muka darkãke waɗansu mutãnen.

137

وَإِنَّكُمْ لَتَمُرُّونَ عَلَيْهِم مُّصْبِحِينَ

wa-innakum latamurrūna ʿalayhim muṣ'biḥīna

Kuma lalle kũ, haƙĩƙa, kunã shũɗewa a kansu, kunã mãsu asubanci.

138

وَبِٱلَّيْلِ ۗ أَفَلَا تَعْقِلُونَ

wabi-al-layli afalā taʿqilūna

Kuma da dare. Shin fa, bã zã ku hankalta ba?

139

وَإِنَّ يُونُسَ لَمِنَ ٱلْمُرْسَلِينَ

wa-inna yūnusa lamina l-mur'salīna

Kuma lalle Yũnusa, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.

140

إِذْ أَبَقَ إِلَى ٱلْفُلْكِ ٱلْمَشْحُونِ

idh abaqa ilā l-ful'ki l-mashḥūni

A lõkacin da ya gudu zuwa ga jirgin ruwa wanda aka yi wa lõdi.

141

فَسَاهَمَ فَكَانَ مِنَ ٱلْمُدْحَضِينَ

fasāhama fakāna mina l-mud'ḥaḍīna

Sã'an nan ya yi ƙuri'a, sai ya kasance a cikin waɗanda aka rinjaya.

142

فَٱلْتَقَمَهُ ٱلْحُوتُ وَهُوَ مُلِيمٌۭ

fal-taqamahu l-ḥūtu wahuwa mulīmun

Sai kĩfi ya yi lõma da shi, alhãli kuwa yanã wanda ake zargi.

143

فَلَوْلَآ أَنَّهُۥ كَانَ مِنَ ٱلْمُسَبِّحِينَ

falawlā annahu kāna mina l-musabiḥīna

To, ba dõmin lalle shi ya kasance daga mãsu tasbĩhi ba,

144

لَلَبِثَ فِى بَطْنِهِۦٓ إِلَىٰ يَوْمِ يُبْعَثُونَ

lalabitha fī baṭnihi ilā yawmi yub'ʿathūna

Lalle dã ya zauna a cikin cikinsa har ya zuwa rãnar da zã a tãyar da su.

145

۞ فَنَبَذْنَـٰهُ بِٱلْعَرَآءِ وَهُوَ سَقِيمٌۭ

fanabadhnāhu bil-ʿarāi wahuwa saqīmun

Sai Muka jẽfa shi ga wani fĩli alhãli kuwa yanã mai raunin rashin lãfiya.

146

وَأَنۢبَتْنَا عَلَيْهِ شَجَرَةًۭ مِّن يَقْطِينٍۢ

wa-anbatnā ʿalayhi shajaratan min yaqṭīnin

Kuma Muka tsirar da wata itãciya ta kankana a kusa da shi.

147

وَأَرْسَلْنَـٰهُ إِلَىٰ مِا۟ئَةِ أَلْفٍ أَوْ يَزِيدُونَ

wa-arsalnāhu ilā mi-ati alfin aw yazīdūna

Kuma Muka aika shi zuwa ga waɗansu mutãne dubuɗari, kõ sunã ƙaruwa (a kan haka).

148

فَـَٔامَنُوا۟ فَمَتَّعْنَـٰهُمْ إِلَىٰ حِينٍۢ

faāmanū famattaʿnāhum ilā ḥīnin

Sai suka yi ĩmãni sabõda haka Muka jiyar da su dãdi har wani lõkaci.

149

فَٱسْتَفْتِهِمْ أَلِرَبِّكَ ٱلْبَنَاتُ وَلَهُمُ ٱلْبَنُونَ

fa-is'taftihim alirabbika l-banātu walahumu l-banūna

Sabõda haka, ka tambaye su, "Shin, Ubangijinka ne da 'ya'ya mãtã, kuma su da ɗiya maza?"

150

أَمْ خَلَقْنَا ٱلْمَلَـٰٓئِكَةَ إِنَـٰثًۭا وَهُمْ شَـٰهِدُونَ

am khalaqnā l-malāikata ināthan wahum shāhidūna

Kõ kuma Mun halitta malã'iku mãtã ne, alhãli kuwa sũ sunãhalarce?

151

أَلَآ إِنَّهُم مِّنْ إِفْكِهِمْ لَيَقُولُونَ

alā innahum min if'kihim layaqūlūna

To! Lalle sũ, daga ƙiren ƙaryarsu sunã cẽwa.

152

وَلَدَ ٱللَّهُ وَإِنَّهُمْ لَكَـٰذِبُونَ

walada l-lahu wa-innahum lakādhibūna

"Allah Yã haihu," alhãli kuwa lalle sũ, haƙĩƙa maƙaryata ne.

153

أَصْطَفَى ٱلْبَنَاتِ عَلَى ٱلْبَنِينَ

aṣṭafā l-banāti ʿalā l-banīna

Shin, Yã zãɓi 'yã'ya mãtã ne a kan ɗiya maza?

154

مَا لَكُمْ كَيْفَ تَحْكُمُونَ

mā lakum kayfa taḥkumūna

Mẽ ya same ku? Yãya kuke hukuntãwa (wannan hukunci)?

155

أَفَلَا تَذَكَّرُونَ

afalā tadhakkarūna

Shin, bã ku tunãni?

156

أَمْ لَكُمْ سُلْطَـٰنٌۭ مُّبِينٌۭ

am lakum sul'ṭānun mubīnun

Ko kuma kunã da wani dalĩli bayyananne ne?

157

فَأْتُوا۟ بِكِتَـٰبِكُمْ إِن كُنتُمْ صَـٰدِقِينَ

fatū bikitābikum in kuntum ṣādiqīna

To, ku zo da littãfinku idan kun kasance mãsu gaskiya.

158

وَجَعَلُوا۟ بَيْنَهُۥ وَبَيْنَ ٱلْجِنَّةِ نَسَبًۭا ۚ وَلَقَدْ عَلِمَتِ ٱلْجِنَّةُ إِنَّهُمْ لَمُحْضَرُونَ

wajaʿalū baynahu wabayna l-jinati nasaban walaqad ʿalimati l-jinatu innahum lamuḥ'ḍarūna

Kuma suka sanya nasaba a tsakãnin Sa da tsakãnin aljannu. Alhãli kuwa Lalle aljannu sun sani, "Lalle sũ, haƙĩƙa waɗanda ake halartarwa ne (a cikin wutã.)"

159

سُبْحَـٰنَ ٱللَّهِ عَمَّا يَصِفُونَ

sub'ḥāna l-lahi ʿammā yaṣifūna

Tsarki ya tabbata ga Allah daga abin da suke siffantãwa.

160

إِلَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلْمُخْلَصِينَ

illā ʿibāda l-lahi l-mukh'laṣīna

Sai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.

161

فَإِنَّكُمْ وَمَا تَعْبُدُونَ

fa-innakum wamā taʿbudūna

To, lalle, ku da abin da kuke bautãwa,

162

مَآ أَنتُمْ عَلَيْهِ بِفَـٰتِنِينَ

mā antum ʿalayhi bifātinīna

Ba ku zama mãsu buwãya ba a gare Shi.

163

إِلَّا مَنْ هُوَ صَالِ ٱلْجَحِيمِ

illā man huwa ṣāli l-jaḥīmi

Sai wanda yake mai shiga babbar wutã Jahĩm.

164

وَمَا مِنَّآ إِلَّا لَهُۥ مَقَامٌۭ مَّعْلُومٌۭ

wamā minnā illā lahu maqāmun maʿlūmun

"Kuma bãbu kõwa daga cikinmu,1 fãce yanã da matsayi sananne."

165

وَإِنَّا لَنَحْنُ ٱلصَّآفُّونَ

wa-innā lanaḥnu l-ṣāfūna

"Kuma lalle mu, haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin sahu-sahu (dõmin ibãda)."

166

وَإِنَّا لَنَحْنُ ٱلْمُسَبِّحُونَ

wa-innā lanaḥnu l-musabiḥūna

"Kuma lalle mũ haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin tasbĩhi."

167

وَإِن كَانُوا۟ لَيَقُولُونَ

wa-in kānū layaqūlūna

Kuma lalle sũ, sun kasance sunã cẽwa,

168

لَوْ أَنَّ عِندَنَا ذِكْرًۭا مِّنَ ٱلْأَوَّلِينَ

law anna ʿindanā dhik'ran mina l-awalīna

"Dã lalle munã da wani littãfi irin na mutãnen farko."

169

لَكُنَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلْمُخْلَصِينَ

lakunnā ʿibāda l-lahi l-mukh'laṣīna

"Lalle dã mun kasance bãyin Allah waɗanda aka tsarkake."

170

فَكَفَرُوا۟ بِهِۦ ۖ فَسَوْفَ يَعْلَمُونَ

fakafarū bihi fasawfa yaʿlamūna

Sai suka kãfirta da shi. Sabõda haka zã su sani.

171

وَلَقَدْ سَبَقَتْ كَلِمَتُنَا لِعِبَادِنَا ٱلْمُرْسَلِينَ

walaqad sabaqat kalimatunā liʿibādinā l-mur'salīna

Kuma lalle, haƙĩƙa kalmar Mu ta gabãta ga bãyinMu, Manzanni.

172

إِنَّهُمْ لَهُمُ ٱلْمَنصُورُونَ

innahum lahumu l-manṣūrūna

Lalle sũ, haƙĩƙa, sũ ne waɗanda ake taimako.

173

وَإِنَّ جُندَنَا لَهُمُ ٱلْغَـٰلِبُونَ

wa-inna jundanā lahumu l-ghālibūna

Kuma lalle rundunarMu, haƙĩƙa, sũ ne marinjaya.

174

فَتَوَلَّ عَنْهُمْ حَتَّىٰ حِينٍۢ

fatawalla ʿanhum ḥattā ḥīnin

Sabõda haka juya daga barinsu, har a wani lõkaci.

175

وَأَبْصِرْهُمْ فَسَوْفَ يُبْصِرُونَ

wa-abṣir'hum fasawfa yub'ṣirūna

Ka nũna musu (gaskiya), da haka zã su dinga gani.1

176

أَفَبِعَذَابِنَا يَسْتَعْجِلُونَ

afabiʿadhābinā yastaʿjilūna

Shin fa, da azabarMu suke nẽman gaggãwa?

177

فَإِذَا نَزَلَ بِسَاحَتِهِمْ فَسَآءَ صَبَاحُ ٱلْمُنذَرِينَ

fa-idhā nazala bisāḥatihim fasāa ṣabāḥu l-mundharīna

To, idan ta sauka ga farfãjiyarsu, to, sãfiyar wadanda ake yi wa gargaɗi ta mũnana.

178

وَتَوَلَّ عَنْهُمْ حَتَّىٰ حِينٍۢ

watawalla ʿanhum ḥattā ḥīnin

Kuma ka jũya daga barinsu har a wani lõkaci.

179

وَأَبْصِرْ فَسَوْفَ يُبْصِرُونَ

wa-abṣir fasawfa yub'ṣirūna

Ka nũna (musu gaskiya), da haka zã su dinga nũnãwa.

180

سُبْحَـٰنَ رَبِّكَ رَبِّ ٱلْعِزَّةِ عَمَّا يَصِفُونَ

sub'ḥāna rabbika rabbi l-ʿizati ʿammā yaṣifūna

Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka, Ubangijin rinjãye, daga barin abin da suke siffantãwa.

181

وَسَلَـٰمٌ عَلَى ٱلْمُرْسَلِينَ

wasalāmun ʿalā l-mur'salīna

Kuma aminci ya tabbata ga Manzanni.

182

وَٱلْحَمْدُ لِلَّهِ رَبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ

wal-ḥamdu lillahi rabbi l-ʿālamīna

Kuma gõdiya ta tabbata ga Allah Ubangijin halittu.

Game da Wannan Sura