55

الرحمن

Ar-Rahman

The Beneficent

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ Da sunan Allah Mai rahama Mai jin kai
Ayoyi 78
Juzu'i 27
Shafi 531-534
Nau'i Madaniya
Tsarin Saukarwa 97
0:00 / 0:00
Aya: 1 / 78
1

ٱلرَّحْمَـٰنُ

al-raḥmānu

(Allah) Mai rahama.

2

عَلَّمَ ٱلْقُرْءَانَ

ʿallama l-qur'āna

Yã sanar da Alƙur'ani.

3

خَلَقَ ٱلْإِنسَـٰنَ

khalaqa l-insāna

Yã halitta mutum.

4

عَلَّمَهُ ٱلْبَيَانَ

ʿallamahu l-bayāna

Yã sanar da shi bayãni (magana).

5

ٱلشَّمْسُ وَٱلْقَمَرُ بِحُسْبَانٍۢ

al-shamsu wal-qamaru biḥus'bānin

Rãnã da watã a kan lissãfi suke.

6

وَٱلنَّجْمُ وَٱلشَّجَرُ يَسْجُدَانِ

wal-najmu wal-shajaru yasjudāni

Kuma tsirrai mãsu yãɗo da itãce sunã tawãlu'i.

7

وَٱلسَّمَآءَ رَفَعَهَا وَوَضَعَ ٱلْمِيزَانَ

wal-samāa rafaʿahā wawaḍaʿa l-mīzāna

Kuma samã Ya ɗaukaka ta, Kuma Yã aza sikẽli.

8

أَلَّا تَطْغَوْا۟ فِى ٱلْمِيزَانِ

allā taṭghaw fī l-mīzāni

Dõmin kada ku karkatar da sikẽlin.

9

وَأَقِيمُوا۟ ٱلْوَزْنَ بِٱلْقِسْطِ وَلَا تُخْسِرُوا۟ ٱلْمِيزَانَ

wa-aqīmū l-wazna bil-qis'ṭi walā tukh'sirū l-mīzāna

Kuma ku daidaita awo da ãdalci, kuma kada ku rage sikẽlin.

10

وَٱلْأَرْضَ وَضَعَهَا لِلْأَنَامِ

wal-arḍa waḍaʿahā lil'anāmi

Kuma ƙasã Yã aza ta dõmin tãlikai.

11

فِيهَا فَـٰكِهَةٌۭ وَٱلنَّخْلُ ذَاتُ ٱلْأَكْمَامِ

fīhā fākihatun wal-nakhlu dhātu l-akmāmi

A cikinta akwai 'ya'yan itãcen marmari da dabĩno mai kwasfa.

12

وَٱلْحَبُّ ذُو ٱلْعَصْفِ وَٱلرَّيْحَانُ

wal-ḥabu dhū l-ʿaṣfi wal-rayḥānu

Da ƙwãya mai sõshiya da ƙamshi.

13

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

fabi-ayyi ālāi rabbikumā tukadhibāni

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangjinku 1kuke ƙaryatãwa?

14

خَلَقَ ٱلْإِنسَـٰنَ مِن صَلْصَـٰلٍۢ كَٱلْفَخَّارِ

khalaqa l-insāna min ṣalṣālin kal-fakhāri

Yã halitta mutum daga ƙẽkasasshen yumɓu kumar kasko.

15

وَخَلَقَ ٱلْجَآنَّ مِن مَّارِجٍۢ مِّن نَّارٍۢ

wakhalaqa l-jāna min mārijin min nārin

Kuma ya halitta aljani daga bira daga wutã.

16

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

fabi-ayyi ālāi rabbikumā tukadhibāni

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

17

رَبُّ ٱلْمَشْرِقَيْنِ وَرَبُّ ٱلْمَغْرِبَيْنِ

rabbu l-mashriqayni warabbu l-maghribayni

Ubangjin mafita biyu na rãnã, kuma Ubangijin mafãɗã biyu na rãnã.

18

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

fabi-ayyi ālāi rabbikumā tukadhibāni

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

19

مَرَجَ ٱلْبَحْرَيْنِ يَلْتَقِيَانِ

maraja l-baḥrayni yaltaqiyāni

Yã garwaya tẽku biyu (ruwan dãɗi da na zartsi) sunã haɗuwa.

20

بَيْنَهُمَا بَرْزَخٌۭ لَّا يَبْغِيَانِ

baynahumā barzakhun lā yabghiyāni

A tsakãninsu akwai shãmaki, bã za su ƙetare haddi ba.

21

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

fabi-ayyi ālāi rabbikumā tukadhibāni

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

22

يَخْرُجُ مِنْهُمَا ٱللُّؤْلُؤُ وَٱلْمَرْجَانُ

yakhruju min'humā l-lu'lu-u wal-marjānu

Lu'ulu'u da murjãni na fita daga gare su.

23

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

fabi-ayyi ālāi rabbikumā tukadhibāni

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

24

وَلَهُ ٱلْجَوَارِ ٱلْمُنشَـَٔاتُ فِى ٱلْبَحْرِ كَٱلْأَعْلَـٰمِ

walahu l-jawāri l-munshaātu fī l-baḥri kal-aʿlāmi

Kuma Yanã da manyan jirãge, waɗanda ake ƙãgãwa a cikin tẽku kamar manyan duwãtsu.

25

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

fabi-ayyi ālāi rabbikumā tukadhibāni

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

26

كُلُّ مَنْ عَلَيْهَا فَانٍۢ

kullu man ʿalayhā fānin

Dukkan wanda ke kanta1 mai ƙãrẽwa ne.

27

وَيَبْقَىٰ وَجْهُ رَبِّكَ ذُو ٱلْجَلَـٰلِ وَٱلْإِكْرَامِ

wayabqā wajhu rabbika dhū l-jalāli wal-ik'rāmi

Kuma Fuskarar Ubangijinka, Mai girman Jalala da karimci, ita ce take wanzuwa.

28

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

fabi-ayyi ālāi rabbikumā tukadhibāni

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

29

يَسْـَٔلُهُۥ مَن فِى ٱلسَّمَـٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ ۚ كُلَّ يَوْمٍ هُوَ فِى شَأْنٍۢ

yasaluhu man fī l-samāwāti wal-arḍi kulla yawmin huwa fī shanin

wanda ke a cikin sammai da ƙasã yanã rõƙon Sa (Allah), a kullum Allah na a cikin wani sha'ani.

30

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

fabi-ayyi ālāi rabbikumā tukadhibāni

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

31

سَنَفْرُغُ لَكُمْ أَيُّهَ ٱلثَّقَلَانِ

sanafrughu lakum ayyuha l-thaqalāni

Zã mu ɗauki lõkaci sabõda ku, yã kũ 1mãsu nauyin halitta biyu!

32

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

fabi-ayyi ālāi rabbikumā tukadhibāni

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

33

يَـٰمَعْشَرَ ٱلْجِنِّ وَٱلْإِنسِ إِنِ ٱسْتَطَعْتُمْ أَن تَنفُذُوا۟ مِنْ أَقْطَارِ ٱلسَّمَـٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ فَٱنفُذُوا۟ ۚ لَا تَنفُذُونَ إِلَّا بِسُلْطَـٰنٍۢ

yāmaʿshara l-jini wal-insi ini is'taṭaʿtum an tanfudhū min aqṭāri l-samāwāti wal-arḍi fa-unfudhū lā tanfudhūna illā bisul'ṭānin

Ya jama'ar aljannu da mutãne! Idan kunã iya zarcẽwa daga sãsannin sammai da ƙasã to ku zarce. Bã za ku iya zarcẽwaba fãce da wani dalĩli.

34

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

fabi-ayyi ālāi rabbikumā tukadhibāni

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

35

يُرْسَلُ عَلَيْكُمَا شُوَاظٌۭ مِّن نَّارٍۢ وَنُحَاسٌۭ فَلَا تَنتَصِرَانِ

yur'salu ʿalaykumā shuwāẓun min nārin wanuḥāsun falā tantaṣirāni

Anã sako wani harshe daga wata wutã a kanku, da narkakkiyar tagulla. To, bã zã ku nẽmi taimako ba?

36

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

fabi-ayyi ālāi rabbikumā tukadhibāni

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

37

فَإِذَا ٱنشَقَّتِ ٱلسَّمَآءُ فَكَانَتْ وَرْدَةًۭ كَٱلدِّهَانِ

fa-idhā inshaqqati l-samāu fakānat wardatan kal-dihāni

Sa'an nan idan sama ta tsãge kuma ta zama jã kamar jar fãta.

38

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

fabi-ayyi ālāi rabbikumā tukadhibāni

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

39

فَيَوْمَئِذٍۢ لَّا يُسْـَٔلُ عَن ذَنۢبِهِۦٓ إِنسٌۭ وَلَا جَآنٌّۭ

fayawma-idhin lā yus'alu ʿan dhanbihi insun walā jānnun

To, a ran nan bã zã a tambayi wani mutum laifinsa ba, kuma haka aljani.

40

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

fabi-ayyi ālāi rabbikumā tukadhibāni

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

41

يُعْرَفُ ٱلْمُجْرِمُونَ بِسِيمَـٰهُمْ فَيُؤْخَذُ بِٱلنَّوَٰصِى وَٱلْأَقْدَامِ

yuʿ'rafu l-muj'rimūna bisīmāhum fayu'khadhu bil-nawāṣī wal-aqdāmi

zã a iya sanin mãsu laifi da alãmarsu, sabõda haka sai a kãma kwarkaɗarsu da sãwãyensu.

42

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

fabi-ayyi ālāi rabbikumā tukadhibāni

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

43

هَـٰذِهِۦ جَهَنَّمُ ٱلَّتِى يُكَذِّبُ بِهَا ٱلْمُجْرِمُونَ

hādhihi jahannamu allatī yukadhibu bihā l-muj'rimūna

Wannan Jahannama ce wadda mãsu laifi ke ƙaryatãwa game da ita.

44

يَطُوفُونَ بَيْنَهَا وَبَيْنَ حَمِيمٍ ءَانٍۢ

yaṭūfūna baynahā wabayna ḥamīmin ānin

Sunã kẽwaya a tsakaninta da ruwan ɗimi mai tsananin tafasa.

45

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

fabi-ayyi ālāi rabbikumā tukadhibāni

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

46

وَلِمَنْ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِۦ جَنَّتَانِ

waliman khāfa maqāma rabbihi jannatāni

Kuma wanda ya ji tsõron tsayãwa a gaba ga Ubangijinsa yanã da Aljanna biyu.

47

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

fabi-ayyi ālāi rabbikumā tukadhibāni

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

48

ذَوَاتَآ أَفْنَانٍۢ

dhawātā afnānin

Mãsu rassan itãce.

49

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

fabi-ayyi ālāi rabbikumā tukadhibāni

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

50

فِيهِمَا عَيْنَانِ تَجْرِيَانِ

fīhimā ʿaynāni tajriyāni

A cikinsu akwai marẽmari biyu sunã gudãna.

51

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

fabi-ayyi ālāi rabbikumā tukadhibāni

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

52

فِيهِمَا مِن كُلِّ فَـٰكِهَةٍۢ زَوْجَانِ

fīhimā min kulli fākihatin zawjāni

A cikinsu akwai nau'i biyu daga kõwane 'ya'yan itãcen marmari.

53

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

fabi-ayyi ālāi rabbikumā tukadhibāni

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

54

مُتَّكِـِٔينَ عَلَىٰ فُرُشٍۭ بَطَآئِنُهَا مِنْ إِسْتَبْرَقٍۢ ۚ وَجَنَى ٱلْجَنَّتَيْنِ دَانٍۢ

muttakiīna ʿalā furushin baṭāinuhā min is'tabraqin wajanā l-janatayni dānin

Sunã gincire a kan waɗansu shimfiɗu cikinsu tufãfin alharĩni mai kauri ne kuma nũnannun 'yã'yan itãcen Aljannar biyu kusakusa suke.

55

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

fabi-ayyi ālāi rabbikumā tukadhibāni

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

56

فِيهِنَّ قَـٰصِرَٰتُ ٱلطَّرْفِ لَمْ يَطْمِثْهُنَّ إِنسٌۭ قَبْلَهُمْ وَلَا جَآنٌّۭ

fīhinna qāṣirātu l-ṭarfi lam yaṭmith'hunna insun qablahum walā jānnun

A cikinsu akwai mãtã mãsu taƙaita ganinsu, wani mutum, gabanin mazajensu bai ɗebe budurcinsu ba kuma haka wani aljani.

57

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

fabi-ayyi ālāi rabbikumā tukadhibāni

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

58

كَأَنَّهُنَّ ٱلْيَاقُوتُ وَٱلْمَرْجَانُ

ka-annahunna l-yāqūtu wal-marjānu

Kamar dai su yaƙũtu ne da murjãni.

59

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

fabi-ayyi ālāi rabbikumā tukadhibāni

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

60

هَلْ جَزَآءُ ٱلْإِحْسَـٰنِ إِلَّا ٱلْإِحْسَـٰنُ

hal jazāu l-iḥ'sāni illā l-iḥ'sānu

Shin, kyautatãwa nã da wani sakamako? (Ã'aha) fãce kyautatãwa.

61

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

fabi-ayyi ālāi rabbikumā tukadhibāni

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

62

وَمِن دُونِهِمَا جَنَّتَانِ

wamin dūnihimā jannatāni

Kuma baicinsu akwai waɗansu gidãjen Aljanna biyu.

63

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

fabi-ayyi ālāi rabbikumā tukadhibāni

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

64

مُدْهَآمَّتَانِ

mud'hāmmatāni

Mãsu duhun inuwa.

65

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

fabi-ayyi ālāi rabbikumā tukadhibāni

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

66

فِيهِمَا عَيْنَانِ نَضَّاخَتَانِ

fīhimā ʿaynāni naḍḍākhatāni

A cikinsu akwai marẽmari biyu masu kwarãrar ruwa.

67

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

fabi-ayyi ālāi rabbikumā tukadhibāni

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

68

فِيهِمَا فَـٰكِهَةٌۭ وَنَخْلٌۭ وَرُمَّانٌۭ

fīhimā fākihatun wanakhlun warummānun

A cikinsu akwai 'ya'yan itãcen marmari da dabĩno darummãni.

69

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

fabi-ayyi ālāi rabbikumā tukadhibāni

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

70

فِيهِنَّ خَيْرَٰتٌ حِسَانٌۭ

fīhinna khayrātun ḥisānun

A cikinsu, akwai wasu mãtã mãsu kyawun hãlãye, mãsu kyaun halitta.

71

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

fabi-ayyi ālāi rabbikumā tukadhibāni

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

72

حُورٌۭ مَّقْصُورَٰتٌۭ فِى ٱلْخِيَامِ

ḥūrun maqṣūrātun fī l-khiyāmi

Mãsu farin idãnu da baƙinsu waɗanda aka tsare a cikin haimõmi.

73

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

fabi-ayyi ālāi rabbikumā tukadhibāni

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

74

لَمْ يَطْمِثْهُنَّ إِنسٌۭ قَبْلَهُمْ وَلَا جَآنٌّۭ

lam yaṭmith'hunna insun qablahum walā jānnun

Wani mutum, gabanin mazajensu bai ɗẽbe budurcinsu ba, kuma haka wani aljani.

75

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

fabi-ayyi ālāi rabbikumā tukadhibāni

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

76

مُتَّكِـِٔينَ عَلَىٰ رَفْرَفٍ خُضْرٍۢ وَعَبْقَرِىٍّ حِسَانٍۢ

muttakiīna ʿalā rafrafin khuḍ'rin waʿabqariyyin ḥisānin

Sunã gincire a kan wasu matãsai mãsu kõren launi da katĩfun Abkara kyãwãwa.

77

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

fabi-ayyi ālāi rabbikumā tukadhibāni

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

78

تَبَـٰرَكَ ٱسْمُ رَبِّكَ ذِى ٱلْجَلَـٰلِ وَٱلْإِكْرَامِ

tabāraka us'mu rabbika dhī l-jalāli wal-ik'rāmi

Sũnan Ubangjinka, Mai girman Jalãla da Karimci, ya tsarkaka.

Game da Wannan Sura