الانشقاق
Al-Inshiqaq
The Sundering
إِذَا ٱلسَّمَآءُ ٱنشَقَّتْ
idhā l-samāu inshaqqat
Idan sama ta kẽce,
وَأَذِنَتْ لِرَبِّهَا وَحُقَّتْ
wa-adhinat lirabbihā waḥuqqat
Ta saurari Ubangijinta, kuma aka wajabta mata yin saurãron,
وَإِذَا ٱلْأَرْضُ مُدَّتْ
wa-idhā l-arḍu muddat
Kuma idan ƙasã aka mĩƙe ta,
وَأَلْقَتْ مَا فِيهَا وَتَخَلَّتْ
wa-alqat mā fīhā watakhallat
Kuma ta jẽfar da abin da yake a cikinta, tã wõfinta daga kõme.
وَأَذِنَتْ لِرَبِّهَا وَحُقَّتْ
wa-adhinat lirabbihā waḥuqqat
Kuma ta saurãri Ubangijinta, aka wajabta mata yin saurãren,
يَـٰٓأَيُّهَا ٱلْإِنسَـٰنُ إِنَّكَ كَادِحٌ إِلَىٰ رَبِّكَ كَدْحًۭا فَمُلَـٰقِيهِ
yāayyuhā l-insānu innaka kādiḥun ilā rabbika kadḥan famulāqīhi
Ya kai mutum! Lalle ne kai mai aikin wahal da kai ne zuwa ga Ubangijinka, wahala mai tsanani, To, kai mai haɗuwa da Shi ne.
فَأَمَّا مَنْ أُوتِىَ كِتَـٰبَهُۥ بِيَمِينِهِۦ
fa-ammā man ūtiya kitābahu biyamīnihi
To, amma wanda aka bai wa littãfinsa da damansa.
فَسَوْفَ يُحَاسَبُ حِسَابًۭا يَسِيرًۭا
fasawfa yuḥāsabu ḥisāban yasīran
To, za a yi masa hisãbi, hisãbi mai sauƙi.
وَيَنقَلِبُ إِلَىٰٓ أَهْلِهِۦ مَسْرُورًۭا
wayanqalibu ilā ahlihi masrūran
Kuma ya jũya zuwa ga iyãlinsa (a cikin Aljanna), yanã mai raha.
وَأَمَّا مَنْ أُوتِىَ كِتَـٰبَهُۥ وَرَآءَ ظَهْرِهِۦ
wa-ammā man ūtiya kitābahu warāa ẓahrihi
Kuma amma wanda aka bai wa littãfinsa, daga wajen bãyansa.
فَسَوْفَ يَدْعُوا۟ ثُبُورًۭا
fasawfa yadʿū thubūran
To, zã shi dinga kiran halaka!
وَيَصْلَىٰ سَعِيرًا
wayaṣlā saʿīran
Kuma ya shiga sa'ĩr.
إِنَّهُۥ كَانَ فِىٓ أَهْلِهِۦ مَسْرُورًا
innahu kāna fī ahlihi masrūran
Lale ne shi, yã kasance (a dũniya) cikin iyãlinsa yanã mai raha.
إِنَّهُۥ ظَنَّ أَن لَّن يَحُورَ
innahu ẓanna an lan yaḥūra
Lalle ne yã yi zaton bã zai kõmo ba.
بَلَىٰٓ إِنَّ رَبَّهُۥ كَانَ بِهِۦ بَصِيرًۭا
balā inna rabbahu kāna bihi baṣīran
Na'am! Lalle ne, Ubangijinsa Ya kasance Mai gani gare shi.
فَلَآ أُقْسِمُ بِٱلشَّفَقِ
falā uq'simu bil-shafaqi
To, ba sai Nã rantse da shafaƙi ba.
وَٱلَّيْلِ وَمَا وَسَقَ
wa-al-layli wamā wasaqa
Da dare, da abin da ya ƙunsa.
وَٱلْقَمَرِ إِذَا ٱتَّسَقَ
wal-qamari idhā ittasaqa
Da watã idan (haskensa) ya cika.
لَتَرْكَبُنَّ طَبَقًا عَن طَبَقٍۢ
latarkabunna ṭabaqan ʿan ṭabaqin
Lalle ne kunã hawan wani hãli daga wani hãli.
فَمَا لَهُمْ لَا يُؤْمِنُونَ
famā lahum lā yu'minūna
To, mẽ ya sãme su, ba su yin ĩmãni?
وَإِذَا قُرِئَ عَلَيْهِمُ ٱلْقُرْءَانُ لَا يَسْجُدُونَ ۩
wa-idhā quri-a ʿalayhimu l-qur'ānu lā yasjudūna
Kuma idan an karanta Alkur'ãni a kansu, bã su yin tawãli'u?
بَلِ ٱلَّذِينَ كَفَرُوا۟ يُكَذِّبُونَ
bali alladhīna kafarū yukadhibūna
Ba haka ba! waɗanda suka kãfirta, sai ƙaryatãwa suke yi.
وَٱللَّهُ أَعْلَمُ بِمَا يُوعُونَ
wal-lahu aʿlamu bimā yūʿūna
Alhãli Allah Shĩ ne Mafi sani ga abin a suke tãrãwa.
فَبَشِّرْهُم بِعَذَابٍ أَلِيمٍ
fabashir'hum biʿadhābin alīmin
Saboda haka, ka yi musu bushãra da azãba mai raɗaɗi.
إِلَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ وَعَمِلُوا۟ ٱلصَّـٰلِحَـٰتِ لَهُمْ أَجْرٌ غَيْرُ مَمْنُونٍۭ
illā alladhīna āmanū waʿamilū l-ṣāliḥāti lahum ajrun ghayru mamnūnin
Fãce waɗanda suka yi ĩmãni, suka aikata ayyukan ƙwarai, sunã da wani sakamako wanda bã ya yankẽwa.