84

الانشقاق

Al-Inshiqaq

The Sundering

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ Da sunan Allah Mai rahama Mai jin kai
Ayoyi 25
Juzu'i 30
Shafi 589
Nau'i Makkiya
Tsarin Saukarwa 83
0:00 / 0:00
Aya: 1 / 25
1

إِذَا ٱلسَّمَآءُ ٱنشَقَّتْ

idhā l-samāu inshaqqat

Idan sama ta kẽce,

2

وَأَذِنَتْ لِرَبِّهَا وَحُقَّتْ

wa-adhinat lirabbihā waḥuqqat

Ta saurari Ubangijinta, kuma aka wajabta mata yin saurãron,

3

وَإِذَا ٱلْأَرْضُ مُدَّتْ

wa-idhā l-arḍu muddat

Kuma idan ƙasã aka mĩƙe ta,

4

وَأَلْقَتْ مَا فِيهَا وَتَخَلَّتْ

wa-alqat mā fīhā watakhallat

Kuma ta jẽfar da abin da yake a cikinta, tã wõfinta daga kõme.

5

وَأَذِنَتْ لِرَبِّهَا وَحُقَّتْ

wa-adhinat lirabbihā waḥuqqat

Kuma ta saurãri Ubangijinta, aka wajabta mata yin saurãren,

6

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلْإِنسَـٰنُ إِنَّكَ كَادِحٌ إِلَىٰ رَبِّكَ كَدْحًۭا فَمُلَـٰقِيهِ

yāayyuhā l-insānu innaka kādiḥun ilā rabbika kadḥan famulāqīhi

Ya kai mutum! Lalle ne kai mai aikin wahal da kai ne zuwa ga Ubangijinka, wahala mai tsanani, To, kai mai haɗuwa da Shi ne.

7

فَأَمَّا مَنْ أُوتِىَ كِتَـٰبَهُۥ بِيَمِينِهِۦ

fa-ammā man ūtiya kitābahu biyamīnihi

To, amma wanda aka bai wa littãfinsa da damansa.

8

فَسَوْفَ يُحَاسَبُ حِسَابًۭا يَسِيرًۭا

fasawfa yuḥāsabu ḥisāban yasīran

To, za a yi masa hisãbi, hisãbi mai sauƙi.

9

وَيَنقَلِبُ إِلَىٰٓ أَهْلِهِۦ مَسْرُورًۭا

wayanqalibu ilā ahlihi masrūran

Kuma ya jũya zuwa ga iyãlinsa (a cikin Aljanna), yanã mai raha.

10

وَأَمَّا مَنْ أُوتِىَ كِتَـٰبَهُۥ وَرَآءَ ظَهْرِهِۦ

wa-ammā man ūtiya kitābahu warāa ẓahrihi

Kuma amma wanda aka bai wa littãfinsa, daga wajen bãyansa.

11

فَسَوْفَ يَدْعُوا۟ ثُبُورًۭا

fasawfa yadʿū thubūran

To, zã shi dinga kiran halaka!

12

وَيَصْلَىٰ سَعِيرًا

wayaṣlā saʿīran

Kuma ya shiga sa'ĩr.

13

إِنَّهُۥ كَانَ فِىٓ أَهْلِهِۦ مَسْرُورًا

innahu kāna fī ahlihi masrūran

Lale ne shi, yã kasance (a dũniya) cikin iyãlinsa yanã mai raha.

14

إِنَّهُۥ ظَنَّ أَن لَّن يَحُورَ

innahu ẓanna an lan yaḥūra

Lalle ne yã yi zaton bã zai kõmo ba.

15

بَلَىٰٓ إِنَّ رَبَّهُۥ كَانَ بِهِۦ بَصِيرًۭا

balā inna rabbahu kāna bihi baṣīran

Na'am! Lalle ne, Ubangijinsa Ya kasance Mai gani gare shi.

16

فَلَآ أُقْسِمُ بِٱلشَّفَقِ

falā uq'simu bil-shafaqi

To, ba sai Nã rantse da shafaƙi ba.

17

وَٱلَّيْلِ وَمَا وَسَقَ

wa-al-layli wamā wasaqa

Da dare, da abin da ya ƙunsa.

18

وَٱلْقَمَرِ إِذَا ٱتَّسَقَ

wal-qamari idhā ittasaqa

Da watã idan (haskensa) ya cika.

19

لَتَرْكَبُنَّ طَبَقًا عَن طَبَقٍۢ

latarkabunna ṭabaqan ʿan ṭabaqin

Lalle ne kunã hawan wani hãli daga wani hãli.

20

فَمَا لَهُمْ لَا يُؤْمِنُونَ

famā lahum lā yu'minūna

To, mẽ ya sãme su, ba su yin ĩmãni?

21

وَإِذَا قُرِئَ عَلَيْهِمُ ٱلْقُرْءَانُ لَا يَسْجُدُونَ ۩

wa-idhā quri-a ʿalayhimu l-qur'ānu lā yasjudūna

Kuma idan an karanta Alkur'ãni a kansu, bã su yin tawãli'u?

Sujada
22

بَلِ ٱلَّذِينَ كَفَرُوا۟ يُكَذِّبُونَ

bali alladhīna kafarū yukadhibūna

Ba haka ba! waɗanda suka kãfirta, sai ƙaryatãwa suke yi.

23

وَٱللَّهُ أَعْلَمُ بِمَا يُوعُونَ

wal-lahu aʿlamu bimā yūʿūna

Alhãli Allah Shĩ ne Mafi sani ga abin a suke tãrãwa.

24

فَبَشِّرْهُم بِعَذَابٍ أَلِيمٍ

fabashir'hum biʿadhābin alīmin

Saboda haka, ka yi musu bushãra da azãba mai raɗaɗi.

25

إِلَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ وَعَمِلُوا۟ ٱلصَّـٰلِحَـٰتِ لَهُمْ أَجْرٌ غَيْرُ مَمْنُونٍۭ

illā alladhīna āmanū waʿamilū l-ṣāliḥāti lahum ajrun ghayru mamnūnin

Fãce waɗanda suka yi ĩmãni, suka aikata ayyukan ƙwarai, sunã da wani sakamako wanda bã ya yankẽwa.

Game da Wannan Sura