15

الحجر

Al-Hijr

The Rocky Tract

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ Da sunan Allah Mai rahama Mai jin kai
Ayoyi 99
Juzu'i 14
Shafi 262-267
Nau'i Makkiya
Tsarin Saukarwa 54
0:00 / 0:00
Aya: 1 / 99
1

الٓر ۚ تِلْكَ ءَايَـٰتُ ٱلْكِتَـٰبِ وَقُرْءَانٍۢ مُّبِينٍۢ

alif-lam-ra til'ka āyātu l-kitābi waqur'ānin mubīnin

A. L̃.R. Waɗan can ãyoyin littãfi ne da abin karantãwa mai bayyanãwa.

2

رُّبَمَا يَوَدُّ ٱلَّذِينَ كَفَرُوا۟ لَوْ كَانُوا۟ مُسْلِمِينَ

rubamā yawaddu alladhīna kafarū law kānū mus'limīna

Da yawa waɗanda suka kãfirta suke gũrin dã dai sun kasance Musulmi.1

3

ذَرْهُمْ يَأْكُلُوا۟ وَيَتَمَتَّعُوا۟ وَيُلْهِهِمُ ٱلْأَمَلُ ۖ فَسَوْفَ يَعْلَمُونَ

dharhum yakulū wayatamattaʿū wayul'hihimu l-amalu fasawfa yaʿlamūna

Ka bar su su ci kuma su ji dãdi, kuma gũri ya shagaltar da su, sa'an nan da sannu zã su sani.

4

وَمَآ أَهْلَكْنَا مِن قَرْيَةٍ إِلَّا وَلَهَا كِتَابٌۭ مَّعْلُومٌۭ

wamā ahlaknā min qaryatin illā walahā kitābun maʿlūmun

Kuma ba Mu halakar da wata alƙarya ba fãce tanã da littafi sananne.

5

مَّا تَسْبِقُ مِنْ أُمَّةٍ أَجَلَهَا وَمَا يَسْتَـْٔخِرُونَ

mā tasbiqu min ummatin ajalahā wamā yastakhirūna

Wata al'umma bã ta gabãtar ajalinta, kuma bã zã su jinkirta ba.

6

وَقَالُوا۟ يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِى نُزِّلَ عَلَيْهِ ٱلذِّكْرُ إِنَّكَ لَمَجْنُونٌۭ

waqālū yāayyuhā alladhī nuzzila ʿalayhi l-dhik'ru innaka lamajnūnun

Suka ce: "Yã kai wanda aka saukar da Ambato (Alƙur'ãni) a kansa! Lalle ne kai, haƙĩƙa, mahaukaci ne."

7

لَّوْ مَا تَأْتِينَا بِٱلْمَلَـٰٓئِكَةِ إِن كُنتَ مِنَ ٱلصَّـٰدِقِينَ

law mā tatīnā bil-malāikati in kunta mina l-ṣādiqīna

"Dõmin me bã zã ka zo mana da malã'ĩku ba idan ka kasance daga mãsu gaskiya?"

8

مَا نُنَزِّلُ ٱلْمَلَـٰٓئِكَةَ إِلَّا بِٱلْحَقِّ وَمَا كَانُوٓا۟ إِذًۭا مُّنظَرِينَ

mā nunazzilu l-malāikata illā bil-ḥaqi wamā kānū idhan munẓarīna

Bã Mu sassaukar da malã'iku fãce da gaskiya,1 bã zã su kasance, a wannan lõkacin, waɗanda ake yi wa jinkĩri ba.

9

إِنَّا نَحْنُ نَزَّلْنَا ٱلذِّكْرَ وَإِنَّا لَهُۥ لَحَـٰفِظُونَ

innā naḥnu nazzalnā l-dhik'ra wa-innā lahu laḥāfiẓūna

Lalle Mũ ne, Muka saukar da Ambato (Alƙur'ãni), kuma lale Mũ, haƙĩƙa, Mãsu kiyayẽwane gare shi.

10

وَلَقَدْ أَرْسَلْنَا مِن قَبْلِكَ فِى شِيَعِ ٱلْأَوَّلِينَ

walaqad arsalnā min qablika fī shiyaʿi l-awalīna

Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun aika Manzanni a cikin ƙungiyõyin farko, gabãnin ka.

11

وَمَا يَأْتِيهِم مِّن رَّسُولٍ إِلَّا كَانُوا۟ بِهِۦ يَسْتَهْزِءُونَ

wamā yatīhim min rasūlin illā kānū bihi yastahziūna

Kuma wani Manzo bã ya zuwa gare su fãce sun kasance sunã mãsu, izgili a gare shi.

12

كَذَٰلِكَ نَسْلُكُهُۥ فِى قُلُوبِ ٱلْمُجْرِمِينَ

kadhālika naslukuhu fī qulūbi l-muj'rimīna

Kamar wancan ne Muke shigar da shi1 a cikin zukãtan mãsu laifi.

13

لَا يُؤْمِنُونَ بِهِۦ ۖ وَقَدْ خَلَتْ سُنَّةُ ٱلْأَوَّلِينَ

lā yu'minūna bihi waqad khalat sunnatu l-awalīna

Bã su yin ĩmãni da shi,( kuma haƙĩƙa, hanyar mutãnen farko ta shige. 1

14

وَلَوْ فَتَحْنَا عَلَيْهِم بَابًۭا مِّنَ ٱلسَّمَآءِ فَظَلُّوا۟ فِيهِ يَعْرُجُونَ

walaw fataḥnā ʿalayhim bāban mina l-samāi faẓallū fīhi yaʿrujūna

Kuma dã Mun bũɗe wata ƙõfa daga sama a kansu har suka wuni a ciki sunã tãkãwa.

15

لَقَالُوٓا۟ إِنَّمَا سُكِّرَتْ أَبْصَـٰرُنَا بَلْ نَحْنُ قَوْمٌۭ مَّسْحُورُونَ

laqālū innamā sukkirat abṣārunā bal naḥnu qawmun masḥūrūna

Lalle ne dã sun ce: "Abin sani kawai, an rufe idãnuwanmu ne. Ã'a, mũ mutãne ne waɗanda aka sihirce."

16

وَلَقَدْ جَعَلْنَا فِى ٱلسَّمَآءِ بُرُوجًۭا وَزَيَّنَّـٰهَا لِلنَّـٰظِرِينَ

walaqad jaʿalnā fī l-samāi burūjan wazayyannāhā lilnnāẓirīna

Kuma lalle ne, haƙĩƙa Mun sanya waɗansu masaukai a, cikin sama, kuma Muka ƙawãta ta ga masu kallo.

17

وَحَفِظْنَـٰهَا مِن كُلِّ شَيْطَـٰنٍۢ رَّجِيمٍ

waḥafiẓ'nāhā min kulli shayṭānin rajīmin

Kuma Muka kiyãye ta daga dukan Shaiɗani wanda ake jĩfa.

18

إِلَّا مَنِ ٱسْتَرَقَ ٱلسَّمْعَ فَأَتْبَعَهُۥ شِهَابٌۭ مُّبِينٌۭ

illā mani is'taraqa l-samʿa fa-atbaʿahu shihābun mubīnun

Fãce wanda ya sãci saurãre sai wutar yũlã bayyananniya ta bĩ shi.

19

وَٱلْأَرْضَ مَدَدْنَـٰهَا وَأَلْقَيْنَا فِيهَا رَوَٰسِىَ وَأَنۢبَتْنَا فِيهَا مِن كُلِّ شَىْءٍۢ مَّوْزُونٍۢ

wal-arḍa madadnāhā wa-alqaynā fīhā rawāsiya wa-anbatnā fīhā min kulli shayin mawzūnin

Kuma ƙasa Mun mĩkẽ ta kuma Mun jẽfa duwãtsu tabbatattu a cikinta kuma Mun tsirar a cikinta, daga dukan abu wanda ake aunãwa da sikẽli.

20

وَجَعَلْنَا لَكُمْ فِيهَا مَعَـٰيِشَ وَمَن لَّسْتُمْ لَهُۥ بِرَٰزِقِينَ

wajaʿalnā lakum fīhā maʿāyisha waman lastum lahu birāziqīna

Kuma Muka sanyã muku, a cikinta, abũbuwan rãyuwã1 da wanda ba ku zamã mãsu ciyarwa gare shi ba.

21

وَإِن مِّن شَىْءٍ إِلَّا عِندَنَا خَزَآئِنُهُۥ وَمَا نُنَزِّلُهُۥٓ إِلَّا بِقَدَرٍۢ مَّعْلُومٍۢ

wa-in min shayin illā ʿindanā khazāinuhu wamā nunazziluhu illā biqadarin maʿlūmin

Kuma bãbu wani abu fãce a wurinMu, akwai taskõkĩnsa kuma ba Mu saukar da shi ba fãce kan gwargwado sananne.

22

وَأَرْسَلْنَا ٱلرِّيَـٰحَ لَوَٰقِحَ فَأَنزَلْنَا مِنَ ٱلسَّمَآءِ مَآءًۭ فَأَسْقَيْنَـٰكُمُوهُ وَمَآ أَنتُمْ لَهُۥ بِخَـٰزِنِينَ

wa-arsalnā l-riyāḥa lawāqiḥa fa-anzalnā mina l-samāi māan fa-asqaynākumūhu wamā antum lahu bikhāzinīna

Kuma Muka aika iskõki mãsu barbarar jũna sa'an nan Muka saukar da ruwa daga sama, sa'an nan Muka shãyar da ku shi, kuma ba ku zama mãsu taskacẽwa a gare shi ba.

23

وَإِنَّا لَنَحْنُ نُحْىِۦ وَنُمِيتُ وَنَحْنُ ٱلْوَٰرِثُونَ

wa-innā lanaḥnu nuḥ'yī wanumītu wanaḥnu l-wārithūna

Kuma lalle ne Mu Muke rãyarwa, kuma Muke kashẽwa kuma Mũ ne magada.

24

وَلَقَدْ عَلِمْنَا ٱلْمُسْتَقْدِمِينَ مِنكُمْ وَلَقَدْ عَلِمْنَا ٱلْمُسْتَـْٔخِرِينَ

walaqad ʿalim'nā l-mus'taqdimīna minkum walaqad ʿalim'nā l-mus'takhirīna

Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun san mãsu gabãta daga cikinku, kuma Mun san mãsu jinkiri.

25

وَإِنَّ رَبَّكَ هُوَ يَحْشُرُهُمْ ۚ إِنَّهُۥ حَكِيمٌ عَلِيمٌۭ

wa-inna rabbaka huwa yaḥshuruhum innahu ḥakīmun ʿalīmun

Kuma lalle ne Ubangijinka Shĩ ne Yake tãra su, lalle Shĩ ne Mai hikima, Masani.

26

وَلَقَدْ خَلَقْنَا ٱلْإِنسَـٰنَ مِن صَلْصَـٰلٍۢ مِّنْ حَمَإٍۢ مَّسْنُونٍۢ

walaqad khalaqnā l-insāna min ṣalṣālin min ḥama-in masnūnin

Kuma lalle ne Mun halicci mutum daga ƙeƙasasshiyar lãka, daga baƙin yumɓu wanda ya canja.

27

وَٱلْجَآنَّ خَلَقْنَـٰهُ مِن قَبْلُ مِن نَّارِ ٱلسَّمُومِ

wal-jāna khalaqnāhu min qablu min nāri l-samūmi

Kuma Aljani Mun haliccẽ shi daga gabãni, daga wutar1 iskar zafi.

28

وَإِذْ قَالَ رَبُّكَ لِلْمَلَـٰٓئِكَةِ إِنِّى خَـٰلِقٌۢ بَشَرًۭا مِّن صَلْصَـٰلٍۢ مِّنْ حَمَإٍۢ مَّسْنُونٍۢ

wa-idh qāla rabbuka lil'malāikati innī khāliqun basharan min ṣalṣālin min ḥama-in masnūnin

Kuma a lõkacin da Ubangijinka ya ce wa malã'iku: "Lalle Nĩ mai halittar wani jiki ne daga ƙẽƙasasshen yumɓu wanda ya canja."

29

فَإِذَا سَوَّيْتُهُۥ وَنَفَخْتُ فِيهِ مِن رُّوحِى فَقَعُوا۟ لَهُۥ سَـٰجِدِينَ

fa-idhā sawwaytuhu wanafakhtu fīhi min rūḥī faqaʿū lahu sājidīna

"To idan Na daidaitã shi kuma Na hũra daga RũhĩNa1 a cikinsa, to, ku fãɗi a gare shi, kunã mãsu yin sujada."

30

فَسَجَدَ ٱلْمَلَـٰٓئِكَةُ كُلُّهُمْ أَجْمَعُونَ

fasajada l-malāikatu kulluhum ajmaʿūna

Sai malã'iku suka yi sujada dukkansu gaba ɗaya.

31

إِلَّآ إِبْلِيسَ أَبَىٰٓ أَن يَكُونَ مَعَ ٱلسَّـٰجِدِينَ

illā ib'līsa abā an yakūna maʿa l-sājidīna

Fãce Iblĩs, ya ƙi kasancẽwa daga mãsu yin sujadar.

32

قَالَ يَـٰٓإِبْلِيسُ مَا لَكَ أَلَّا تَكُونَ مَعَ ٱلسَّـٰجِدِينَ

qāla yāib'līsu mā laka allā takūna maʿa l-sājidīna

Ya ce: "Yã Iblĩs mẽne ne a gare ka, ba ka kasance tãre da mãsu yin sujuda ba?"

33

قَالَ لَمْ أَكُن لِّأَسْجُدَ لِبَشَرٍ خَلَقْتَهُۥ مِن صَلْصَـٰلٍۢ مِّنْ حَمَإٍۢ مَّسْنُونٍۢ

qāla lam akun li-asjuda libasharin khalaqtahu min ṣalṣālin min ḥama-in masnūnin

Ya ce: "Ban kasance inã yin sujada ba ga mutum wanda Ka halicce shi daga bũsasshen yumɓun lãka wadda ta canja."

34

قَالَ فَٱخْرُجْ مِنْهَا فَإِنَّكَ رَجِيمٌۭ

qāla fa-ukh'ruj min'hā fa-innaka rajīmun

Ya ce: "To, ka fita daga gare ta, dõmin lalle kai abin jĩfa ne."

35

وَإِنَّ عَلَيْكَ ٱللَّعْنَةَ إِلَىٰ يَوْمِ ٱلدِّينِ

wa-inna ʿalayka l-laʿnata ilā yawmi l-dīni

"Kuma lalle ne akwai la'ana a kanka har ya zuwa rãnar sakamako."

36

قَالَ رَبِّ فَأَنظِرْنِىٓ إِلَىٰ يَوْمِ يُبْعَثُونَ

qāla rabbi fa-anẓir'nī ilā yawmi yub'ʿathūna

Ya ce: "Yã Ubangjĩna! Sai Ka yi mini jinkiri zuwa rãnar da ake tãshin su."

37

قَالَ فَإِنَّكَ مِنَ ٱلْمُنظَرِينَ

qāla fa-innaka mina l-munẓarīna

Ya ce: "To, lalle ne kanã daga waɗanda ake yi wa jinkiri."

38

إِلَىٰ يَوْمِ ٱلْوَقْتِ ٱلْمَعْلُومِ

ilā yawmi l-waqti l-maʿlūmi

"Zuwa ga Yinin Lõkacin nan sanan ne."

39

قَالَ رَبِّ بِمَآ أَغْوَيْتَنِى لَأُزَيِّنَنَّ لَهُمْ فِى ٱلْأَرْضِ وَلَأُغْوِيَنَّهُمْ أَجْمَعِينَ

qāla rabbi bimā aghwaytanī la-uzayyinanna lahum fī l-arḍi wala-ugh'wiyannahum ajmaʿīna

Ya ce: "Yã Ubangijina! Inã rantsuwa da abin da Ka ɓatar da ni da shi, haƙĩƙa inã ƙawãta musu (rãyuwa) a cikin ƙasã kuma haƙĩƙa inã ɓatar da su gabã ɗaya."

40

إِلَّا عِبَادَكَ مِنْهُمُ ٱلْمُخْلَصِينَ

illā ʿibādaka min'humu l-mukh'laṣīna

"Fãce bãyinKa daga gare su, waɗanda Ka tsarkake."

41

قَالَ هَـٰذَا صِرَٰطٌ عَلَىَّ مُسْتَقِيمٌ

qāla hādhā ṣirāṭun ʿalayya mus'taqīmun

Ya ce: "Wannan tafarki ne a gare Ni, madaidaici."

42

إِنَّ عِبَادِى لَيْسَ لَكَ عَلَيْهِمْ سُلْطَـٰنٌ إِلَّا مَنِ ٱتَّبَعَكَ مِنَ ٱلْغَاوِينَ

inna ʿibādī laysa laka ʿalayhim sul'ṭānun illā mani ittabaʿaka mina l-ghāwīna

"Lalle ne bãyĩNa, bã ka da ĩkõ a kansu, fãce wanda ya bĩ ka daga ɓatattu."

43

وَإِنَّ جَهَنَّمَ لَمَوْعِدُهُمْ أَجْمَعِينَ

wa-inna jahannama lamawʿiduhum ajmaʿīna

Kuma lalle Jahannama ce haƙĩƙa, ma'akawartarsu gabã ɗaya.

44

لَهَا سَبْعَةُ أَبْوَٰبٍۢ لِّكُلِّ بَابٍۢ مِّنْهُمْ جُزْءٌۭ مَّقْسُومٌ

lahā sabʿatu abwābin likulli bābin min'hum juz'on maqsūmun

Tanã da ƙõfõfi bakwai,1 ga kõwace ƙõfa akwai wani juz'i daga gare su rababbe.

45

إِنَّ ٱلْمُتَّقِينَ فِى جَنَّـٰتٍۢ وَعُيُونٍ

inna l-mutaqīna fī jannātin waʿuyūnin

Lalle mãsu taƙawa sunã a cikin gidãjen Aljanna mai idandunan ruwa.

46

ٱدْخُلُوهَا بِسَلَـٰمٍ ءَامِنِينَ

ud'khulūhā bisalāmin āminīna

"Ku shigẽ ta da aminci, kunã amintattu."

47

وَنَزَعْنَا مَا فِى صُدُورِهِم مِّنْ غِلٍّ إِخْوَٰنًا عَلَىٰ سُرُرٍۢ مُّتَقَـٰبِلِينَ

wanazaʿnā mā fī ṣudūrihim min ghillin ikh'wānan ʿalā sururin mutaqābilīna

Kuma Muka ɗẽbe abinda ke a cikin zukãtansu na daga ƙullin zũci, suka zama 'yan'uwa a kan gadãje, sunã mãsu fuskantar junã.

48

لَا يَمَسُّهُمْ فِيهَا نَصَبٌۭ وَمَا هُم مِّنْهَا بِمُخْرَجِينَ

lā yamassuhum fīhā naṣabun wamā hum min'hā bimukh'rajīna

Wata wahala bã zã ta shãfe su bã a cikinta kuma ba su zama mãsu fita daga, cikin ta ba.

49

۞ نَبِّئْ عِبَادِىٓ أَنِّىٓ أَنَا ٱلْغَفُورُ ٱلرَّحِيمُ

nabbi ʿibādī annī anā l-ghafūru l-raḥīmu

Ka bai wa bãyiNa lãbari cẽwa lalle ne Ni, Mai gãfarane, Mai jin ƙai.

50

وَأَنَّ عَذَابِى هُوَ ٱلْعَذَابُ ٱلْأَلِيمُ

wa-anna ʿadhābī huwa l-ʿadhābu l-alīmu

Kuma azãbãTa ita ce Azãba mai raɗaɗi.

51

وَنَبِّئْهُمْ عَن ضَيْفِ إِبْرَٰهِيمَ

wanabbi'hum ʿan ḍayfi ib'rāhīma

Kuma ka bã su lãbãrin bãƙin Ibrãhĩm.

52

إِذْ دَخَلُوا۟ عَلَيْهِ فَقَالُوا۟ سَلَـٰمًۭا قَالَ إِنَّا مِنكُمْ وَجِلُونَ

idh dakhalū ʿalayhi faqālū salāman qāla innā minkum wajilūna

A lõkacin da suka shiga gunsa, sai suka ce: "Sallama." Ya ce: "Lalle mũ, daga gare ku, mãsu firgita ne."

53

قَالُوا۟ لَا تَوْجَلْ إِنَّا نُبَشِّرُكَ بِغُلَـٰمٍ عَلِيمٍۢ

qālū lā tawjal innā nubashiruka bighulāmin ʿalīmin

Suka ce: "Kada ka firgita. Lalle ne mũ, munã yi makabushãra game da wani yãro masani."

54

قَالَ أَبَشَّرْتُمُونِى عَلَىٰٓ أَن مَّسَّنِىَ ٱلْكِبَرُ فَبِمَ تُبَشِّرُونَ

qāla abashartumūnī ʿalā an massaniya l-kibaru fabima tubashirūna

Ya ce: "Shin kun bã ni bushãra1 ne a kan tsũfa yã shãfe ni? To, da me kuke bã ni bushara?"

55

قَالُوا۟ بَشَّرْنَـٰكَ بِٱلْحَقِّ فَلَا تَكُن مِّنَ ٱلْقَـٰنِطِينَ

qālū basharnāka bil-ḥaqi falā takun mina l-qāniṭīna

Suka ce: "Munã yi maka bushãra da gaskiya ne, sabõda haka, kada da kasance daga mãsu yanke tsammãni."

56

قَالَ وَمَن يَقْنَطُ مِن رَّحْمَةِ رَبِّهِۦٓ إِلَّا ٱلضَّآلُّونَ

qāla waman yaqnaṭu min raḥmati rabbihi illā l-ḍālūna

Ya ce: "Kuma wãne ne yake yanke tsammãni daga rahamar Ubangijin sa, fãce ɓatattu?"

57

قَالَ فَمَا خَطْبُكُمْ أَيُّهَا ٱلْمُرْسَلُونَ

qāla famā khaṭbukum ayyuhā l-mur'salūna

Ya ce: "To, mẽne ne babban al'amarinku? Yã kũ manzanni!"

58

قَالُوٓا۟ إِنَّآ أُرْسِلْنَآ إِلَىٰ قَوْمٍۢ مُّجْرِمِينَ

qālū innā ur'sil'nā ilā qawmin muj'rimīna

Suka ce: "Lalle ne mũ, an aika mu zuwa ga wasu mutãne mãsu laifi."

59

إِلَّآ ءَالَ لُوطٍ إِنَّا لَمُنَجُّوهُمْ أَجْمَعِينَ

illā āla lūṭin innā lamunajjūhum ajmaʿīna

"Fãce mutãnen Lũɗu, lalle ne mũ, haƙĩƙa, mãsu tsĩrar dasu ne gabã ɗaya."

60

إِلَّا ٱمْرَأَتَهُۥ قَدَّرْنَآ ۙ إِنَّهَا لَمِنَ ٱلْغَـٰبِرِينَ

illā im'ra-atahu qaddarnā innahā lamina l-ghābirīna

"Fãce mãtarsa mun ƙaddara cẽwa lalle ne ita, haƙĩƙa, tanã daga mãsu halaka."

61

فَلَمَّا جَآءَ ءَالَ لُوطٍ ٱلْمُرْسَلُونَ

falammā jāa āla lūṭin l-mur'salūna

To, a lõkacin da mazannin suka jẽ wa mutãnen Lũɗu,

62

قَالَ إِنَّكُمْ قَوْمٌۭ مُّنكَرُونَ

qāla innakum qawmun munkarūna

Ya ce: "Lalle ne ku mutãne ne waɗanda ba a sani ba."

63

قَالُوا۟ بَلْ جِئْنَـٰكَ بِمَا كَانُوا۟ فِيهِ يَمْتَرُونَ

qālū bal ji'nāka bimā kānū fīhi yamtarūna

Suka ce: "Ã'a, mun zo maka sabõda abin da suka kasance sunã shakka a cikinsa."

64

وَأَتَيْنَـٰكَ بِٱلْحَقِّ وَإِنَّا لَصَـٰدِقُونَ

wa-ataynāka bil-ḥaqi wa-innā laṣādiqūna

"Kuma mun zo maka da gaskiya. Kuma lalle ne mũ, haƙĩƙa, mãsu gaskiya ne."

65

فَأَسْرِ بِأَهْلِكَ بِقِطْعٍۢ مِّنَ ٱلَّيْلِ وَٱتَّبِعْ أَدْبَـٰرَهُمْ وَلَا يَلْتَفِتْ مِنكُمْ أَحَدٌۭ وَٱمْضُوا۟ حَيْثُ تُؤْمَرُونَ

fa-asri bi-ahlika biqiṭ'ʿin mina al-layli wa-ittabiʿ adbārahum walā yaltafit minkum aḥadun wa-im'ḍū ḥaythu tu'marūna

"Sai ka yi tafiya da iyãlinka, a wani yanki na dare, kuma ka bi bãyansu, kuma kada wani daga cikinku ya yi waiwaye, kuma ku bi ta inda aka aumurce ku."

66

وَقَضَيْنَآ إِلَيْهِ ذَٰلِكَ ٱلْأَمْرَ أَنَّ دَابِرَ هَـٰٓؤُلَآءِ مَقْطُوعٌۭ مُّصْبِحِينَ

waqaḍaynā ilayhi dhālika l-amra anna dābira hāulāi maqṭūʿun muṣ'biḥīna

Kuma Muka hukunta wancan al'amarin zuwa gare shi cẽwa lalle ne ƙarshen waɗancan abin yankẽwa ne a lõkacin da suke mãsu shiga Asuba.

67

وَجَآءَ أَهْلُ ٱلْمَدِينَةِ يَسْتَبْشِرُونَ

wajāa ahlu l-madīnati yastabshirūna

Kuma mutãnen alƙaryar suka je sunã mãsu bushãra.

68

قَالَ إِنَّ هَـٰٓؤُلَآءِ ضَيْفِى فَلَا تَفْضَحُونِ

qāla inna hāulāi ḍayfī falā tafḍaḥūni

Ya ce: "Lalle ne waɗannan bãƙĩna ne, sabõda haka kada ku kunyata ni."

69

وَٱتَّقُوا۟ ٱللَّهَ وَلَا تُخْزُونِ

wa-ittaqū l-laha walā tukh'zūni

"Kuma ku bi Allah da taƙawa, kuma kada ku sanya ni a baƙin ciki."

70

قَالُوٓا۟ أَوَلَمْ نَنْهَكَ عَنِ ٱلْعَـٰلَمِينَ

qālū awalam nanhaka ʿani l-ʿālamīna

Suka ce: "Ashe ba mu hana ka daga tãlikai ba?"

71

قَالَ هَـٰٓؤُلَآءِ بَنَاتِىٓ إِن كُنتُمْ فَـٰعِلِينَ

qāla hāulāi banātī in kuntum fāʿilīna

Ya ce: "Ga waɗannan, 'ya'yãna1 idan kun kasance mãsu aikatãwa ne."

72

لَعَمْرُكَ إِنَّهُمْ لَفِى سَكْرَتِهِمْ يَعْمَهُونَ

laʿamruka innahum lafī sakratihim yaʿmahūna

Rantsuwa da1 rãyuwarka! Lalle ne sũ a cikin mãyensu sunã ta ɗĩmuwa.

73

فَأَخَذَتْهُمُ ٱلصَّيْحَةُ مُشْرِقِينَ

fa-akhadhathumu l-ṣayḥatu mush'riqīna

Sa'an nan tsãwa ta kãma su, sunã mãsu shiga lõkacin hũdõwar rãnã.

74

فَجَعَلْنَا عَـٰلِيَهَا سَافِلَهَا وَأَمْطَرْنَا عَلَيْهِمْ حِجَارَةًۭ مِّن سِجِّيلٍ

fajaʿalnā ʿāliyahā sāfilahā wa-amṭarnā ʿalayhim ḥijāratan min sijjīlin

Sa'an nan Muka sanya samanta ya kõma ƙasanta, kuma Muka yi ruwan duwãtsu na lãkar wuta a kansu.

75

إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَـَٔايَـٰتٍۢ لِّلْمُتَوَسِّمِينَ

inna fī dhālika laāyātin lil'mutawassimīna

Lalle ne a cikin wancan akwai ãyõyi ga mãsu tsõkaci da hankali.

76

وَإِنَّهَا لَبِسَبِيلٍۢ مُّقِيمٍ

wa-innahā labisabīlin muqīmin

Kuma lalle ne ita, haƙĩƙa sunã a gẽfen wata hanyã tabbatacciya.1

77

إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَـَٔايَةًۭ لِّلْمُؤْمِنِينَ

inna fī dhālika laāyatan lil'mu'minīna

Lalle ne a cikin wancan akwai ãyã ga mãsu ĩmãni.

78

وَإِن كَانَ أَصْحَـٰبُ ٱلْأَيْكَةِ لَظَـٰلِمِينَ

wa-in kāna aṣḥābu l-aykati laẓālimīna

Kuma lalle ne ma'abũta Al'aika1 sun kasance, haƙĩƙa, mãsu zãlunci!

79

فَٱنتَقَمْنَا مِنْهُمْ وَإِنَّهُمَا لَبِإِمَامٍۢ مُّبِينٍۢ

fa-intaqamnā min'hum wa-innahumā labi-imāmin mubīnin

Sai Muka yi azãbar rãmuwã a gare su, kuma lalle sũ biyun, haƙĩƙa, sunã a gẽfen wani tafarki mabayyani.

80

وَلَقَدْ كَذَّبَ أَصْحَـٰبُ ٱلْحِجْرِ ٱلْمُرْسَلِينَ

walaqad kadhaba aṣḥābu l-ḥij'ri l-mur'salīna

Kuma lalle ne haƙĩƙa ma'abũta Hijiri1 sun ƙaryata Manzanni.

81

وَءَاتَيْنَـٰهُمْ ءَايَـٰتِنَا فَكَانُوا۟ عَنْهَا مُعْرِضِينَ

waātaynāhum āyātinā fakānū ʿanhā muʿ'riḍīna

Kuma Kuka kai musu ãyõyinMu, sai suka kasance mãsu bijirẽwa daga gare su.

82

وَكَانُوا۟ يَنْحِتُونَ مِنَ ٱلْجِبَالِ بُيُوتًا ءَامِنِينَ

wakānū yanḥitūna mina l-jibāli buyūtan āminīna

Kuma sun kasance sunã sassaƙa gidãje daga duwãtsu, alhãli sunã amintattu.

83

فَأَخَذَتْهُمُ ٱلصَّيْحَةُ مُصْبِحِينَ

fa-akhadhathumu l-ṣayḥatu muṣ'biḥīna

Sai tsãwa ta kãma su sunã mãsu shiga Asuba.

84

فَمَآ أَغْنَىٰ عَنْهُم مَّا كَانُوا۟ يَكْسِبُونَ

famā aghnā ʿanhum mā kānū yaksibūna

Sa'an nan abin da suka kasance sunã tsirfantãwa bai wadãtar ga barinsu ba.

85

وَمَا خَلَقْنَا ٱلسَّمَـٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضَ وَمَا بَيْنَهُمَآ إِلَّا بِٱلْحَقِّ ۗ وَإِنَّ ٱلسَّاعَةَ لَـَٔاتِيَةٌۭ ۖ فَٱصْفَحِ ٱلصَّفْحَ ٱلْجَمِيلَ

wamā khalaqnā l-samāwāti wal-arḍa wamā baynahumā illā bil-ḥaqi wa-inna l-sāʿata laātiyatun fa-iṣ'faḥi l-ṣafḥa l-jamīla

Kuma ba Mu halicci sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu ba fãce da gaskiya. Kuma lalle ne Sã'a (Rãnar Alƙiyãma) haƙĩƙa mai zuwa ce. Sabõdahaka ka yi rangwame, rangwame mai kyau.

86

إِنَّ رَبَّكَ هُوَ ٱلْخَلَّـٰقُ ٱلْعَلِيمُ

inna rabbaka huwa l-khalāqu l-ʿalīmu

Lalle ne Ubangijinka, shi ne Mai yawan halitta, Masani.

87

وَلَقَدْ ءَاتَيْنَـٰكَ سَبْعًۭا مِّنَ ٱلْمَثَانِى وَٱلْقُرْءَانَ ٱلْعَظِيمَ

walaqad ātaynāka sabʿan mina l-mathānī wal-qur'āna l-ʿaẓīma

Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun bã ka bakwai waɗan da ake maimaita karatunsu1 da Alƙur'ãni mai girma.

88

لَا تَمُدَّنَّ عَيْنَيْكَ إِلَىٰ مَا مَتَّعْنَا بِهِۦٓ أَزْوَٰجًۭا مِّنْهُمْ وَلَا تَحْزَنْ عَلَيْهِمْ وَٱخْفِضْ جَنَاحَكَ لِلْمُؤْمِنِينَ

lā tamuddanna ʿaynayka ilā mā mattaʿnā bihi azwājan min'hum walā taḥzan ʿalayhim wa-ikh'fiḍ janāḥaka lil'mu'minīna

Kada lalle kaƙĩƙa idãnunka biyu zuwa ga abin da Muka jiyar da su dãɗi game da shi, nau'i-nau'i a gare su, kuma kada ka yi baƙin ciki a kansu, kuma sassauta fikãfikanka ga mãsu ĩmãni.

89

وَقُلْ إِنِّىٓ أَنَا ٱلنَّذِيرُ ٱلْمُبِينُ

waqul innī anā l-nadhīru l-mubīnu

Kuma ka ce: "Lalle nĩ nĩ ne mai gargaɗi bayyanan ne."

90

كَمَآ أَنزَلْنَا عَلَى ٱلْمُقْتَسِمِينَ

kamā anzalnā ʿalā l-muq'tasimīna

Kamar yadda Muka saukar a kan mãsu yin rantsuwa,1

91

ٱلَّذِينَ جَعَلُوا۟ ٱلْقُرْءَانَ عِضِينَ

alladhīna jaʿalū l-qur'āna ʿiḍīna

Waɗanda suka sanya Alƙur'ãni tãtsuniyõyi.

92

فَوَرَبِّكَ لَنَسْـَٔلَنَّهُمْ أَجْمَعِينَ

fawarabbika lanasalannahum ajmaʿīna

To, rantsuwa da Ubangijinka!1 Haƙĩƙa, Munã tambayarsugabã ɗaya.

93

عَمَّا كَانُوا۟ يَعْمَلُونَ

ʿammā kānū yaʿmalūna

Daga abin da suka kasance sunã aikatãwa.

94

فَٱصْدَعْ بِمَا تُؤْمَرُ وَأَعْرِضْ عَنِ ٱلْمُشْرِكِينَ

fa-iṣ'daʿ bimā tu'maru wa-aʿriḍ ʿani l-mush'rikīna

Sai ka tsage gaskiya game da abin da ake umurnin ka kuma ka kau da kai daga masu shirki.

95

إِنَّا كَفَيْنَـٰكَ ٱلْمُسْتَهْزِءِينَ

innā kafaynāka l-mus'tahziīna

Lalle ne Mũ Mun isar maka daga mãsu1 izgili.

96

ٱلَّذِينَ يَجْعَلُونَ مَعَ ٱللَّهِ إِلَـٰهًا ءَاخَرَ ۚ فَسَوْفَ يَعْلَمُونَ

alladhīna yajʿalūna maʿa l-lahi ilāhan ākhara fasawfa yaʿlamūna

Waɗanda suke sanyãwar wani abin bautãwa na dabam tare da Allah, sa'an nan da sannu zã su sani.

97

وَلَقَدْ نَعْلَمُ أَنَّكَ يَضِيقُ صَدْرُكَ بِمَا يَقُولُونَ

walaqad naʿlamu annaka yaḍīqu ṣadruka bimā yaqūlūna

Kuma lalle ne haƙĩƙa Munã sanin cẽwa lalle kai, ƙirjinka yanã yin ƙunci game da abin da suke faɗã (na izgili).

98

فَسَبِّحْ بِحَمْدِ رَبِّكَ وَكُن مِّنَ ٱلسَّـٰجِدِينَ

fasabbiḥ biḥamdi rabbika wakun mina l-sājidīna

Sabõda haka ka yi tasbĩhi game da gõde wa Ubangijinka, kuma ka kasance daga mãsu sujada.

99

وَٱعْبُدْ رَبَّكَ حَتَّىٰ يَأْتِيَكَ ٱلْيَقِينُ

wa-uʿ'bud rabbaka ḥattā yatiyaka l-yaqīnu

Kuma ka bauta wa Ubangijinka, har mutuwa ta zo maka.

Game da Wannan Sura