الدخان
Ad-Dukhan
The Smoke
حمٓ
hha-meem
Ḥ. M̃.
وَٱلْكِتَـٰبِ ٱلْمُبِينِ
wal-kitābi l-mubīni
Inã rantsuwa da Littãfi Mabayyani.
إِنَّآ أَنزَلْنَـٰهُ فِى لَيْلَةٍۢ مُّبَـٰرَكَةٍ ۚ إِنَّا كُنَّا مُنذِرِينَ
innā anzalnāhu fī laylatin mubārakatin innā kunnā mundhirīna
Lalle ne, Mũ, Muka saukar da shi a cikin wani dare mai albarka. Lalle Mũ' Mun kasance Mãsu yin gargaɗi.
فِيهَا يُفْرَقُ كُلُّ أَمْرٍ حَكِيمٍ
fīhā yuf'raqu kullu amrin ḥakīmin
A cikinsa (shi daren) ake rarrabe kõwane umurui bayyananne.
أَمْرًۭا مِّنْ عِندِنَآ ۚ إِنَّا كُنَّا مُرْسِلِينَ
amran min ʿindinā innā kunnā mur'silīna
Umurni na daga wurin Mu. Lalle Mũ ne Muka kasance Mãsu aikãwã.
رَحْمَةًۭ مِّن رَّبِّكَ ۚ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلسَّمِيعُ ٱلْعَلِيمُ
raḥmatan min rabbika innahu huwa l-samīʿu l-ʿalīmu
Sabõda rahama daga Ubangijinka. Lalle Shĩ, Shi ne Mai ji, Mãsani.
رَبِّ ٱلسَّمَـٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ وَمَا بَيْنَهُمَآ ۖ إِن كُنتُم مُّوقِنِينَ
rabbi l-samāwāti wal-arḍi wamā baynahumā in kuntum mūqinīna
(Shĩ ne) Ubangijin sammai da ƙasa da abin da ke a tsakãninsu, idan kun kasance mãsu yaƙĩni (za ku gãne haka).
لَآ إِلَـٰهَ إِلَّا هُوَ يُحْىِۦ وَيُمِيتُ ۖ رَبُّكُمْ وَرَبُّ ءَابَآئِكُمُ ٱلْأَوَّلِينَ
lā ilāha illā huwa yuḥ'yī wayumītu rabbukum warabbu ābāikumu l-awalīna
Babu abin bautãwa fãce Shi. Yana rãyarwa Kuma Yana kashẽwa. (Shi ne) Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku na farko.
بَلْ هُمْ فِى شَكٍّۢ يَلْعَبُونَ
bal hum fī shakkin yalʿabūna
A'a sũ, sunã wãsã a cikin shakka.
فَٱرْتَقِبْ يَوْمَ تَأْتِى ٱلسَّمَآءُ بِدُخَانٍۢ مُّبِينٍۢ
fa-ir'taqib yawma tatī l-samāu bidukhānin mubīnin
Sabõda haka, ka dakata rãnar da sama zã tã zo da hayãƙi bayyananne.
يَغْشَى ٱلنَّاسَ ۖ هَـٰذَا عَذَابٌ أَلِيمٌۭ
yaghshā l-nāsa hādhā ʿadhābun alīmun
Yanã rufe mutãne. Wannan wata azãba ce mai raɗaɗi.
رَّبَّنَا ٱكْشِفْ عَنَّا ٱلْعَذَابَ إِنَّا مُؤْمِنُونَ
rabbanā ik'shif ʿannā l-ʿadhāba innā mu'minūna
Ya Ubangijinmu! Ka kuranye mana azãba. Lalle Mũ, mãsu ĩmãni ne.
أَنَّىٰ لَهُمُ ٱلذِّكْرَىٰ وَقَدْ جَآءَهُمْ رَسُولٌۭ مُّبِينٌۭ
annā lahumu l-dhik'rā waqad jāahum rasūlun mubīnun
Inã tunãwa take a gare su, alhãli kuwa, haƙĩƙa, Manzo mai bayyanãwa Ya je musu (da gargaɗin saukar azãbar, ba su karɓa ba)?
ثُمَّ تَوَلَّوْا۟ عَنْهُ وَقَالُوا۟ مُعَلَّمٌۭ مَّجْنُونٌ
thumma tawallaw ʿanhu waqālū muʿallamun majnūnun
Sa'an nan suka jũya baya daga gare shi, Kuma suka ce: "Wanda ake gayãwa1 ne, mahaukaci."
إِنَّا كَاشِفُوا۟ ٱلْعَذَابِ قَلِيلًا ۚ إِنَّكُمْ عَآئِدُونَ
innā kāshifū l-ʿadhābi qalīlan innakum ʿāidūna
Lalle Mũ, Mãsu kuranyẽwar azãba ne, a ɗan lõkaci kaɗan, lalle kũ, mãsu kõmãwa ne (ga laifin).
يَوْمَ نَبْطِشُ ٱلْبَطْشَةَ ٱلْكُبْرَىٰٓ إِنَّا مُنتَقِمُونَ
yawma nabṭishu l-baṭshata l-kub'rā innā muntaqimūna
Rãnar da Muke damƙa, damƙa mafi girma, lalle ne Mũ mãsu azãbar rãmuwa ne.
۞ وَلَقَدْ فَتَنَّا قَبْلَهُمْ قَوْمَ فِرْعَوْنَ وَجَآءَهُمْ رَسُولٌۭ كَرِيمٌ
walaqad fatannā qablahum qawma fir'ʿawna wajāahum rasūlun karīmun
Kuma lalle ne haƙĩƙa a gabaninsu, Mun fitini mutãnen Fir'auna, kuma wani Manzo karĩmi ya jẽ musu.
أَنْ أَدُّوٓا۟ إِلَىَّ عِبَادَ ٱللَّهِ ۖ إِنِّى لَكُمْ رَسُولٌ أَمِينٌۭ
an addū ilayya ʿibāda l-lahi innī lakum rasūlun amīnun
(Mazon ya ce): "Ku kãwo mini (ĩmãninku) ya bayin Allah! Lalle ni, Manzo ne amintacce zuwa gare ku."
وَأَن لَّا تَعْلُوا۟ عَلَى ٱللَّهِ ۖ إِنِّىٓ ءَاتِيكُم بِسُلْطَـٰنٍۢ مُّبِينٍۢ
wa-an lā taʿlū ʿalā l-lahi innī ātīkum bisul'ṭānin mubīnin
"Kuma kada ku nẽmi ɗaukaka a kan Allah. Lalle nĩ mai zo muku ne da dalĩli bayyananne."
وَإِنِّى عُذْتُ بِرَبِّى وَرَبِّكُمْ أَن تَرْجُمُونِ
wa-innī ʿudh'tu birabbī warabbikum an tarjumūni
"Kuma lalle nĩ na nẽmi tsari da Ubangijĩna, kuma Ubangijinku, dõmin kada ku jẽfe ni."
وَإِن لَّمْ تُؤْمِنُوا۟ لِى فَٱعْتَزِلُونِ
wa-in lam tu'minū lī fa-iʿ'tazilūni
"Kuma idan ba ku yi ĩmãni sabõda nĩ ba, to, ku nĩsance ni."
فَدَعَا رَبَّهُۥٓ أَنَّ هَـٰٓؤُلَآءِ قَوْمٌۭ مُّجْرِمُونَ
fadaʿā rabbahu anna hāulāi qawmun muj'rimūna
Sai ya kirayi Ubangjinsa cẽwa waɗannan mutãnene mãsu laifi.
فَأَسْرِ بِعِبَادِى لَيْلًا إِنَّكُم مُّتَّبَعُونَ
fa-asri biʿibādī laylan innakum muttabaʿūna
(Allah Ya ce): "To, ka yi tafiyar dare da bayiNa, da dare. Lalle kũ, waɗanda ake bĩ ne (dõmin a kãma ku.)"
وَٱتْرُكِ ٱلْبَحْرَ رَهْوًا ۖ إِنَّهُمْ جُندٌۭ مُّغْرَقُونَ
wa-ut'ruki l-baḥra rahwan innahum jundun mugh'raqūna
"Kuma ka bar tẽku rarrabe. Lalle sũ, runduna ce abar nutsarwa."
كَمْ تَرَكُوا۟ مِن جَنَّـٰتٍۢ وَعُيُونٍۢ
kam tarakū min jannātin waʿuyūnin
Da yawa suka bar gõnaki da marẽmari.
وَزُرُوعٍۢ وَمَقَامٍۢ كَرِيمٍۢ
wazurūʿin wamaqāmin karīmin
Da shuke-shuke da matsayi mai kyau.
وَنَعْمَةٍۢ كَانُوا۟ فِيهَا فَـٰكِهِينَ
wanaʿmatin kānū fīhā fākihīna
Da wata ni'ima da suka kasance a cikinta sunã mãsu hutu.
كَذَٰلِكَ ۖ وَأَوْرَثْنَـٰهَا قَوْمًا ءَاخَرِينَ
kadhālika wa-awrathnāhā qawman ākharīna
Kamar haka! Kuma Muka gãdar da ita ga waɗansu mutãne na dabam.
فَمَا بَكَتْ عَلَيْهِمُ ٱلسَّمَآءُ وَٱلْأَرْضُ وَمَا كَانُوا۟ مُنظَرِينَ
famā bakat ʿalayhimu l-samāu wal-arḍu wamā kānū munẓarīna
Sa'an nan samã da ƙasã ba su yi kũka 1a kansu ba, Kuma ba su kasance waɗanda ake yi wa jinkiri ba.
وَلَقَدْ نَجَّيْنَا بَنِىٓ إِسْرَٰٓءِيلَ مِنَ ٱلْعَذَابِ ٱلْمُهِينِ
walaqad najjaynā banī is'rāīla mina l-ʿadhābi l-muhīni
Kuma lalle ne, haƙĩƙa Mun tsĩrar da Banĩ Isrã'ĩla daga, azãba mai wulãkantãwa.
مِن فِرْعَوْنَ ۚ إِنَّهُۥ كَانَ عَالِيًۭا مِّنَ ٱلْمُسْرِفِينَ
min fir'ʿawna innahu kāna ʿāliyan mina l-mus'rifīna
Daga Fir'auna. Lalle shi, ya kasance maɗaukaki daga cikin mãsu ɓarna.
وَلَقَدِ ٱخْتَرْنَـٰهُمْ عَلَىٰ عِلْمٍ عَلَى ٱلْعَـٰلَمِينَ
walaqadi ikh'tarnāhum ʿalā ʿil'min ʿalā l-ʿālamīna
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun zãɓe su sabõda wani ilmi (na Taurata) a kan mutãne.
وَءَاتَيْنَـٰهُم مِّنَ ٱلْـَٔايَـٰتِ مَا فِيهِ بَلَـٰٓؤٌۭا۟ مُّبِينٌ
waātaynāhum mina l-āyāti mā fīhi balāon mubīnun
Kuma Muka bã su, daga ãyõyin mu'ujizõji, abin da yake a cikinsa, akwai ni'ima bayyananna1
إِنَّ هَـٰٓؤُلَآءِ لَيَقُولُونَ
inna hāulāi layaqūlūna
Lalle waɗannan mutãne1, haƙĩka, sunã cẽwa,
إِنْ هِىَ إِلَّا مَوْتَتُنَا ٱلْأُولَىٰ وَمَا نَحْنُ بِمُنشَرِينَ
in hiya illā mawtatunā l-ūlā wamā naḥnu bimunsharīna
"Babu wani abu sai mutuwarmu ta farko, kuma ba mu zama waɗanda ake tãyarwa ba."
فَأْتُوا۟ بِـَٔابَآئِنَآ إِن كُنتُمْ صَـٰدِقِينَ
fatū biābāinā in kuntum ṣādiqīna
"Sai ku zo da ubanninmu, idan kun kasance mãsu gaskiya."
أَهُمْ خَيْرٌ أَمْ قَوْمُ تُبَّعٍۢ وَٱلَّذِينَ مِن قَبْلِهِمْ ۚ أَهْلَكْنَـٰهُمْ ۖ إِنَّهُمْ كَانُوا۟ مُجْرِمِينَ
ahum khayrun am qawmu tubbaʿin wa-alladhīna min qablihim ahlaknāhum innahum kānū muj'rimīna
shin, sũ ne mafĩfĩta kõ kuwa mutãnen Tubba'u, kuma da waɗanda ke a gabãninsu? Mun halaka su, lalle sũ, sun kasance mãsu laifi.
وَمَا خَلَقْنَا ٱلسَّمَـٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضَ وَمَا بَيْنَهُمَا لَـٰعِبِينَ
wamā khalaqnā l-samāwāti wal-arḍa wamā baynahumā lāʿibīna
Kuma ba Mu halitta slmmai da ƙasa da abin da ke a tsakãninsu ba, alhãli kuwa Munã mãsu wãsã.
مَا خَلَقْنَـٰهُمَآ إِلَّا بِٱلْحَقِّ وَلَـٰكِنَّ أَكْثَرَهُمْ لَا يَعْلَمُونَ
mā khalaqnāhumā illā bil-ḥaqi walākinna aktharahum lā yaʿlamūna
Ba Mu halitta su ba fãce da manufa ta gaskiya, kuma amma mafi yawansu, ba su sani ba.
إِنَّ يَوْمَ ٱلْفَصْلِ مِيقَـٰتُهُمْ أَجْمَعِينَ
inna yawma l-faṣli mīqātuhum ajmaʿīna
Lalle rãnar rarrabẽwa, ita ce lõkacin wa'adinsu gabã ɗaya.
يَوْمَ لَا يُغْنِى مَوْلًى عَن مَّوْلًۭى شَيْـًۭٔا وَلَا هُمْ يُنصَرُونَ
yawma lā yugh'nī mawlan ʿan mawlan shayan walā hum yunṣarūna
Rãnar da wani zumu bã ya amfãnin wani zumu da kõme kuma ba su zama anã taimakon su ba.
إِلَّا مَن رَّحِمَ ٱللَّهُ ۚ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلْعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ
illā man raḥima l-lahu innahu huwa l-ʿazīzu l-raḥīmu
fãce wanda Allah Ya yi wa rahama. Lalle Shi (Allah), shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
إِنَّ شَجَرَتَ ٱلزَّقُّومِ
inna shajarata l-zaqūmi
Lalle itãciyar zaƙƙũm (ɗanyen wutã),
طَعَامُ ٱلْأَثِيمِ
ṭaʿāmu l-athīmi
Ita ce abincin mai laifi.
كَٱلْمُهْلِ يَغْلِى فِى ٱلْبُطُونِ
kal-muh'li yaghlī fī l-buṭūni
Kamar narkakken kwalta yanã tafasa a cikin cikunna.
كَغَلْىِ ٱلْحَمِيمِ
kaghalyi l-ḥamīmi
Kamar tafasar ruwan zãfi.
خُذُوهُ فَٱعْتِلُوهُ إِلَىٰ سَوَآءِ ٱلْجَحِيمِ
khudhūhu fa-iʿ'tilūhu ilā sawāi l-jaḥīmi
(A cẽ wa malã'ikun wutã), "Ku kãmã shi, sa'an nan ku fizge shi zuwa ga tsakiyar Jahĩm."
ثُمَّ صُبُّوا۟ فَوْقَ رَأْسِهِۦ مِنْ عَذَابِ ٱلْحَمِيمِ
thumma ṣubbū fawqa rasihi min ʿadhābi l-ḥamīmi
"Sa'an nan ku zuba, a kansa, daga azãbar ruwan zãfi."
ذُقْ إِنَّكَ أَنتَ ٱلْعَزِيزُ ٱلْكَرِيمُ
dhuq innaka anta l-ʿazīzu l-karīmu
(A ce masã), "Ka ɗanɗana! Lalle kai, kai ne mabuwãyi mai girma!"
إِنَّ هَـٰذَا مَا كُنتُم بِهِۦ تَمْتَرُونَ
inna hādhā mā kuntum bihi tamtarūna
"Lalle wannan, shi ne abin da kuka kasance kunã shakka game da shi."
إِنَّ ٱلْمُتَّقِينَ فِى مَقَامٍ أَمِينٍۢ
inna l-mutaqīna fī maqāmin amīnin
Lalle mãsu taƙawa sunã cikin matsayi amintacce.
فِى جَنَّـٰتٍۢ وَعُيُونٍۢ
fī jannātin waʿuyūnin
A cikin gidãjen Aljanna da marẽmari.
يَلْبَسُونَ مِن سُندُسٍۢ وَإِسْتَبْرَقٍۢ مُّتَقَـٰبِلِينَ
yalbasūna min sundusin wa-is'tabraqin mutaqābilīna
Sunã tufanta daga tufãfin alharĩni raƙĩƙi, da mai kauri, sunã mãsu zaman fuskantar jũna.
كَذَٰلِكَ وَزَوَّجْنَـٰهُم بِحُورٍ عِينٍۢ
kadhālika wazawwajnāhum biḥūrin ʿīnin
Kamar haka, kuma Mun aurar da su da mãtã mãsu kyawun idãnu, mãsu girmansu.
يَدْعُونَ فِيهَا بِكُلِّ فَـٰكِهَةٍ ءَامِنِينَ
yadʿūna fīhā bikulli fākihatin āminīna
Sunã kira, a cikinsu (gidẽjen) ga dukan 'ya'yan itãcen marmari, sunã amintattu (daga dukan abin tsõro).
لَا يَذُوقُونَ فِيهَا ٱلْمَوْتَ إِلَّا ٱلْمَوْتَةَ ٱلْأُولَىٰ ۖ وَوَقَىٰهُمْ عَذَابَ ٱلْجَحِيمِ
lā yadhūqūna fīhā l-mawta illā l-mawtata l-ūlā wawaqāhum ʿadhāba l-jaḥīmi
Bã su ɗanɗanar mutuwa, a cikinsu, fãce mutuwar farko, kuma (Allah), Ya tsare musu azãbar Jahĩm.
فَضْلًۭا مِّن رَّبِّكَ ۚ ذَٰلِكَ هُوَ ٱلْفَوْزُ ٱلْعَظِيمُ
faḍlan min rabbika dhālika huwa l-fawzu l-ʿaẓīmu
Sabõda falala daga Ubangijinka. Wancan shi ne babban rabo, mai girma.
فَإِنَّمَا يَسَّرْنَـٰهُ بِلِسَانِكَ لَعَلَّهُمْ يَتَذَكَّرُونَ
fa-innamā yassarnāhu bilisānika laʿallahum yatadhakkarūna
Dõmin haka kawai Muka sauƙaƙar da shi (Alƙur'ãni) da harshenka, tsammãninsu, su riƙa tunãwa.
فَٱرْتَقِبْ إِنَّهُم مُّرْتَقِبُونَ
fa-ir'taqib innahum mur'taqibūna
Sai ka yi jira. Lalle sũ, mãsu jira ne.1